Header Ads
Showing 1 words to 3000 words out of 11711 words

Chapter 1 - KANGIN BAUTA Littafin Yaki Complete by Mansur Usman Sufi .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

Kangin Bauta 1
Littafin yaki
Rubuta labari
Mansur Usman Sufi
Wthapp number
08137237071










Kyawawan samari ne majiya karfin damtse su uku, mai matukar kwarjini da ban tsoro. Na farkonsu yana rataye da waɗansu zaratan takubba guda biyu a gadon bayanshi kuma ya kasance mai matuƙar kaurin jiki fiye da 'yan uwanshi.
Saurayi na biyu yana dauke da wani irin KWARI DA BAKA mai daukar hankali,jikinsa a murde yake ya tara kwanji,


kallo daya zakayi masa kafahimci cewa ya fi sauran yan uwansa kirar sadaukantaka.


Na ukun kuwa yana ɗauke da dauke da dogon nashi mai baki biyu,


bakin yakasance daga farkon sa yayi fadi daga karshe yayi tsini ya fitar da baki biyu.


Babu abin da zai burge ka ga samarin sama da yadda suka yi shigar yaƙi iri daya sak,


kuma suna zaune abisa jajayen dawakai ingarmu.


Samarin uku suna tafiya ne acikin wani daji ma,abincin dogayen bishiyoyi,koramu,


tare da kwazazzabai.gaba daya yanayin dajin ya banbanta da sauran dazuzzukan da idanuwa suka saba gani.


Domin hatta kwari da tsuntsayen dake cikin sa abin tsoro ne.awasu lokutan sai kaga tsuntsaye na dauke da fuskokin bil,adama,hatta bishiyoyin dajin suna canza launi zuwa launi,


Tabbas dajin yana da matukar kwarjini ga duk jarumin daya tsinci kansa acikin sa dolane ya razana


Haka dai zaratan samarin uku suka cigaba da tafiya adajin Babu alamun razani atattare da fuskokinsu Lokacin da suka shafe tsawon sa,a daya da dakika talatin suna tafiya acikin dajin,a dai dai wannan lokaci ne suka fara hango wani katafaren gida kwaya daya jal adajin,


Al,amarin da yayi matukar basu mamaki kenan suka ce acikin zukatan su.taya za,ace wannan kasurgumin daji ace an gina wannan kerarrran gida a cikinsa.


Amsar tambayoyin da suka kasa bawa kansu kenan, suka cigaba da tafiya,


Da isar su bakin gidan suka tarar da gidan ya kasance tankameme Tamkar gari guda.gaba daya ginin anyi shine da waɗansu manyan duwatsun wuta wadanda ido bai taba gani ba,


Katangun gidan sun kasance masu tsawon gaske.akwai ƙatuwar kofa guda daya jal mai tsawo da kauri inda za,a sanya karti majiya karfi mutum hamsin bazasu iya ture ta.


Nanfa samarin suka yi cirko-cirko suna nazarin kofar tsawon dakika arba,in dayansu bai ce uffan ba.


Daga can sai daya daga cikin su wanda ake kira da suna Hilwas yayi gyaran murya yace "yaku 'yan uwana yanzu mene ne abinyi?


Gashi yanzu mun iso gidan boka kimraz,naji ajiki na cewa dukkan baiwar da muke da ita bazata yi mana wani amfani ba face muyi Amfani da fasahar da muke da ita."


Koda jin wannan batu sai sharwas yayi caraf ya tari numfashin Hilwasa


yace"Ni shawarar dazan bamu muyi tunanin hanyar da zamu bude Wannan kofa,


kunsan masu iya magana na cewa abari ya huce shi ke kawo rabon wani, kuma da zafi-zafi a kan daki karfe."


Duk wannan tattaunawa da akeyi kahzib yayi shiru bai ce kala ba. Fuskar sa cike da damuwa,


Kahzib yayi gyaran murya yace"yaku abokaina nifa ba wannan abu ne damuwata ba.


shin kun mantane cewa rayuwar iyayenmu tana hannun sarki shardasu.


A cikin ku wane yake da tabbacin sarki shardasu zai cika alkawarin daya daukar mana idan muka mallako masa abubuwan da yake buƙata na bamu fansar rayukan iyayemu.


meyasa baza muyi tunani me yasa baza muyi tunani akan nemo musu maganin dazai warkar da lalurar dake samun su ba?


Sa,adda kahzib ya zo daidai nan azancen sa sai jikin Hilwasa da sharwas yayi sanyi.


Kuma hankalinsu ya dugunzuma ainun suka zurfafa izuwa kogin tunani,


Su dai wadannan samari sun fito ne daga Wani birni da akewa lakabi da BAITUL-NA'IM.


dalilin daya baro dasu daga gida shine kamar haka:-


*


Birnin baitul-na,im yakasance kasaitaccen birni daya shahara a fannin noma, kasuwanci.


wanda ya haɗar da attajirai da manoma.kuma suna da ZARATAN MAYAKA masu juriya a filin daga. Sarkin da yake rike da Sarautar wannan birnin ana kiransa da shardasu ibn furais,


Sarki shardasu yakasance Gwarzon mayaki mai tarwatsa maza afilin fama.


mutum ne mai son abin duniya .dadin dadawa kuma yakasance AZZALUMI nagaban kwatance.


Domin duk shekara a birnin sa ana noma abinda bokaye da masu hasashe suka tabbatar da cewa zai iya ciyar da kasashen dake nahiyar na tsawon shekaru biyu amma saboda zaluncin sa sai dai ya siyar da abincin ga manyan kasashen da ke wata nahiyar daban Duk yawan abin da mutum ya noma zai kasashi gida Biyar ya dauki daya kaso hudun na sarki shardasu ne.


hatta dabbobi bai kyale ba duk shekara a kwai kason sa aciki, Sai da ya Zamo duk faɗin nahiyar babu attajiri kamarsa.


Mahaifan Waɗannan samari uku sun kasance bayi ne ga sarki shardasu asali sarki shardasu ne ya cinye kasar su da yaki ya ribato su a matsayin fursunonin yaki.


A tarihin samartakar su ba,a samu jarumai kamar su ba a can ƙasar su Mahaifan su sun samu lalurar dake jikin sune saboda bautar da suke yi a karkashin sarki shardasu.


Mahaifin Hilwasa ana kiransa da suna Rukaisu , Rukaisu ya samu lalurar makantane saboda aikin ƙera dukkan nau,ikan kayan yaki,kofuna,da sauransu abubuwan da ake sana'anta su da zinariya da jauhari. Tunda Rukaisu yake Wannan aiki nasa ba,a taba samu ya ƙera wani abu ba yadda sarki ya buƙata ba amma


saboda wata rana an samu akasi ya kera wadansu kofuna ba yadda aka umarta ba ya sanya aka soke masa idanu da wasu kibiyoyi na wuta idanunsa suka makance kuma aka aikashi izuwa kurkuku.


Mahaifin sharwas kuwa ana kiransa da suna Rauzil ya kamu da ciwon kuturtane a hannayen sa da ƙafafuwan sa saboda aikin dafa sarki shardasu ruwan wanka wata rana rauzil ya kammala dafawa sarki ruwan zafi a bahon wanka bayan ya kammala zuba turaruka da sabulai masu kanshi,


sai ya umarci wadansu kuyangi da sukai ruwan izuwa kewaye.


Jim kadan sai ga sarki shardasu ya fito daga kewayen fuskarsa a murtuke tamkar an aiko masa da sakon mutuwa.


kawai sai ya damki gashin kan Rauzil yana janshi akasa har izuwa inda wani ƙaton kasko yake a turakar sa.


Kaskon yana dauke da wani tafashasshan ruwan zafi mai kauri baƙi baƙi.


kawai sai sarki shardasu ya kama hannayen Rauzil ya tsomasu acikin kaskon.


Tun Rauzil yana kwarara ihu har takai bana iyawa sai dai hawaye kawai yake zuba a idanunsa.lokacin daya fito da ƙafafuwan take naman jikinsu ya zagwanye Babu tausayi afuskar sarki shardasu ya damki hannayen Rauzil ya motsa akaskon,


Hakika komai rashin imanin mutum idan yaga yadda Rauzil yake kwarara ihu yana zubar da hawaye dolane ya tausaya masa sai da naman jikin hannayen ya zagwanye sannan ya yi jifa dashi gefe guda


Rauzil na fitar da numfashi sama-sama tamkar zai sheka barzahu daga nan aka kaishi izuwa kurkuku yazamo gurgu baya iya tafiya sai dai rarrafe


Mahaifin kahzib kuwa ana kiransa da suna Hashim Shi kuma ya samu lalurar kurumtane


saboda wani laifi da ya yi wa Sarki shardasu ya dunga dura masa garwashin wuta a baki yana hadiyewa


Matayen su hasham kuwa sai suka kasance cikin matukar bakin ciki tare da kewaye mazajen su dare da rana Bayan shudewar wannan al,amari ne da kwanaki arba'in sai sarki shardasu na zaune a fadar sa.


Fadar ta kasance makekiya mai tsawo da fadi.an kawatata da dukkan kayan kyale kyalen alatun jin dadin duniya.


Duk inda mutum ya kalla bayi ne da kuyangi suna ta hidima,


kowacce kusurwa a fadar dakarun ne atsaitsaye cikin matsananciyar shigar yaƙi mai matukar kwarjini da ban tsoro hannayen su rike da miyagun makamai Domin tabbatar da cikekken tsaro.


Sarki shardasu Sarki shardasu na zaune a bisa kan ƙasaitacciyar karagar mulki da akayi da farin lu,u lu,u da jauhari.


Ajikinsa yana sanye da yar karamar rigar Koriya mai gajeran hannu a hannun sa na hagu yana rike da wata ƙasaitacciyar sanda irin ta hamshakan sarakai sanye a kansa akwai kambun sarauta na zinare.


A ƙafarsa yana sanye da takalmi baki da aka yi masa ado da nau,ikan gashin dawisu.


A wannan lokacin ana tafiyar da harkokin mulki cikin kwanciyar hankali kwatsam sai aka hango Wani badakare ya shigo fadar yayin da rage tsakaninsa da karagar mulki bai huce taku goma ba sai kawai ya zube kasa ya kwashi gaisuwa.


sannan daga bisani ya dago da kansa yayi gyaran murya yace"ya shugabana labari ya riskeni cewa matayen su hasham sun sauka lafiya,


kuma dukkanninsu sun haifi yaya maza, Koda jin wannan batu daga bakin bawa Durshuf sai fuskar sarki shardasu ta faɗa ɗa da murmushi tamkar wanda aka bawa SARAUTAR DUNIYA


kuma ya mike tsaye tsam daga kan karagar sa daga bisani ya murtuke fuska tamkar an aiko masa da sakon mutuwa ya dubi Bawa Durshuf yace"ina so kayi mini jagora izuwa inda matayen suke"


Sarki na gama faɗin hakan sai bawa Durshuf ya shige gaba sarki shardasu yabi bayansa take dakarun Sa suka mara masa baya.


Suna fita wajen fadar aka kawo keken doki sarki Yakamata ya hau aka cigaba da tafiya.


Tafiyar dakika talatin da hudu, su badakare Durshuf kadai su kayi suka iso wani bangare da bayi suke a cikin Gidan sarautar,


















Shi dai wannan bangare akalla yana dauke da dakuna fiye da talatin kuma musamman an Gina nasa ne domin bayi mata masu dauke da juna biyu. Da isowar su durshuf


Sai wani badakare ya rugo izuwa inda suke tsaye ya sauke matattakalar keken dokin take Sarki shardasu ya taka matattakalar keken dokin Ya sauko kasa Sannan badakaren ya zube kasa Ya kwashi gaisuwa cikin ladabi yace"ya mai duniya ai Sai ku shigo izuwa ciki


















Sarki shardasu Ya karewa matayen kallo da nazarin jariran dake hannayen su na wani dan lokaci Sannan daga bisani ya mayar da dubansa ga shugaban dake kula da Gidan wani garjejen kato yace dashi cikin kakkausar murya






"yakai Larbus kayi Sani cewa ban zo wannan gida ba Sai don na baka wani umarni. Abin da nake bukata shi ne ka kula da lafiyar wadannan mataye da jariran su.






Tabbas nan gaba zasu zamo masu amfani agareni". Koda gama wannan jawabin Sai Sarki shardasu Ya juya ya nufi kofar fita daga gidan dakarun sa na take masa baya.






yana fita ya hau bisa keken dokin Sa, Ya nufi hanyar da zata mayar dashi izuwa fada.






Tun daga wannan rana matayen su Hasham suka kasance cikin kulawa ta musamman.






Amma dai-dai da rana daya basu taba daina begen masoyan su ba,






Gaskiyar masu iya magana da su kace sannu-sannu bata hana zuwa Sai dai adade ba,a je ba Sai gashi jariran su Hasham sun shekara goma,






tun a wannan lokaci Sarki shardasu Ya umarni sarkin yaki Hatyal ya dauke su ya kaisu izuwa gidan horan yaki Nan fa yazamo cewa su sharwas sun kware ainun a fagen salon yaki iri daban-daban.






A bangaren mahaifan su Hilwas kuwa tun da aka tafi da Yaya yen su Sai izuwa gidan horar da mayaka Sai Ya zama na sun kasance cikin KANGIN BAUTA Ya zama na duk wata kulawa da ake basu lokacin da suka haihu an dai na yi musu ,






domin a wasu lokutan dakyar suke samun abinda zasu ci.














****






Kasaitacciyar turaka ce da aka kawata ta da nau'ikan kayan kawa da alatun jin dadin rayuwar duniya.
Babban abinda ya kara fito da kyawun turakar shi ne wadansu fararen kushin na alfarma da aka kewaye turakar dasu kowacce kusurwa a turakar an kawata ta da wasu kawatattun fitulu na azurfa.
idan mai kallo ya yi duba daga bangaren yamma a turakar bisa kayatattun kujerun zai yi arba da wani sadauki zaune shirye cikin gagarumar shigar yaki Mai matukar kwarjini da ban tsoro Duba daya zaka yi masa ka kawar da fuskar ka saboda tsananin munin sa,
A bisa wata karaga ta alfarma wani mutum ma,abocin kyawun fuska da kwarjini,
yana sanye da tufafin sarauta na alfarma sun yi matukar yi masa kyau kai da gani kasan yana jin dadin duniya.
Shiru ne ya wanzu a tsakanin su Sai Daga bisani ne Sarki shardasu Ya katse shirun da ya wanzu ta hanyar budar baki yayi gyaran murya
yace "yakai dirkar birnin baitul-na,im kayi Sani Sani cewa ban kirawo ka nan ba Sai domin na tunasar dakai cewa lokacin gudanar da GASAR JARUMTA ya gabato nan da kwana talatin kacal!
Lallai ina so a fara shirye shiryen wannan gasa. Kasani cewa awannnan karon akwai manayan sarakunan nahiyoyi hudu da zasu halarci wannan Gasa Sannan salon gasar zai canza izuwa rukuni uku .wato fadan takobi,
Sai kuma na KWARI DA BAKA da kuma ta KARFIN DANTSE.
Koda Sarki shardasu Ya zo nan azancensa Sai Ya zira hannun sa aljihunsa na Riga ya dauko wata doguwar takarda ya mikawa sarkin yaki,
Cikin biyayya ya sa hannayen sa ya karba Sannan ya warware ta yafara karanta abinda ke kunshe a cikinta.
Koda kammala karantawar Sai yaji zuciyar sa yayi bakikkirin bakomai ne ya sanya shi cikin wannan hali ba Sai domin a cikin sunayen jaruman gasar da aka bashi yaga sunan yarima kinzaru Wanda tsakanin su akwai rashin jituwa,
Saboda sarkin yaki yana matukar kaunar kanwarsa gimbiya lashmira Tsakanin lashmira da yarima kinzaru akwai rashin jituwa saboda kowannen su na kwadayin ya gaji karagar mulki,
Sa,adda Sarki yaki Ya zo dai dai nan a tunanin sa Sai ya cika da matukar bakin ciki yana cikin wannan hali ne Sai ya lura akwai sauran rubutu a ayan takardar. Cikin matukar farin ciki ya juya takardar ai kuwa Sai yayi arba da sunan gimbiya lashmira,Bawa Hilwas, sharwas da bawa kahzib,
saboda farin ciki bai San sa,adda murmushi ya subuce masa ba,
yayin da ya hada idanu da Sarki shardasu sai ya sunkui da kansa kasa cikin alamun rashin gaskiya Sarki shardasu Ya dubi sarkin yaki da duban dake nuna fahimtar wani abu game da murmushi nasa Sannan yayi gyaran murya yace


" ya dirkar birnina kayi Sani cewa inaso ka gaggauta sanar da dukkan Wanda sunan sa ke kunshe a cikin wannan takardar jaruman Gasa kuma a tabbatar da cikekken tsaro daga yanzu har izuwa bayan gasa domin wannan gasa ce ta musamman.
Koda gama fadin hakan sai Sarki shardasu Ya mike tsaye tsam! daga kan kujerar sa ya taka da kafafunsa ya nufi wata har siririyar kofa a turakar.


Yana tafiya cikin kasaita da BAKAR IZZA! yana isa bakin kofar wadansu ZARATAN MAYAKA na sihiri suka bayyana su kimanin arba,in shirye cikin gagrumar shigar yaki suka Mara masa ba ya har ya kule izuwa cikin Gidan sarautar.
Hakika Sarki shardasu Ya zurfafa acikin ilimin tsafi da kamo kafar shi sai mutum yayi da gaske.


Nan take Sarki yaki Ya mike tsaye ya fice daga turakar zuciyar sa cike da tunane - tunane iri - iri.














Mu hadu a kangin bauta 3






Don cigaban wannan kayataccen labari






Daga mai debe muku kewa akoda yaushe






MANSUR USMAN (SUFI)






Wthapp number 08137237071























KANGIN BAUTA 6






Marubuci






MANSUR USMAN SUFI














Sarki Barsus na kwance bisa gado a cikin masaukinsa sanye da riga falmaran da dogon wando marar nauyi irin na hamshakan attajirai, kawai sai ya ji wani kwankwasa masa kofar shigowa turakar nan take ya mike tsaye tsam daga kan gadon ya je ya bude kofar. Wani saurayi


kyakykyawa sanye cikin sulken yaki ya yi ido biyu da shi,


Barsus ya yi guntun murmushi a gare shi.


Saurayin ya zube kasa ya kwashi gaisuwa sannan ya budi baki cikin ladabi ya yi gyaran murya ya ce,


"Ya shugabana tuni kyaumu sun iso tare da shugaban barayin wannan nahiya, kuma tuni ma sun fara yin kyau da ayy kyau, domin isa in da turakar sarki Shardasu da gimbiya Lashmira take.


Koda jin wannan batun daga bakin saurayin sai sarki Barsus ya bushe da dariyar mugunta, a lokaci guda kuma ya turbune fuska kamar an aiko masa da WASIKAR MUTUWA.


Cikin kakkausar murya ya ce, "Tabbas na yarda da kai ya kai Huzmal ina mai tabbatar maka da cewa da zarar burina ya cika na ganin bayan sarki Shardasu da gimbiya Lashmira a gobe za a yi nadin sarauta ta tare da yi maka wazirina,


Koda jin hakan daga bakin sarki Barsus sai Huzmal ya sake zubewa kasa ya kwashi gaisuwa,


sannan ya tashi ya juya ya ficc daga cikin turakar zuciyarsa cike da farin ciki,


koda ficewar Huzmal sai sarki Barsus ya janyo kofar turakar ya rufe ta ruf,


ya kashe fitulun da ke ciki, sannan ya kwanta bisa kan gadonsa domin ya samu ya huta.






Sa'adda gimbiya Lashmira ta yi arba da fuskar mahayin sai ta cika abin mamaki mamaki, ba komai ne ba ya ba ta mamaki ba sai bisa ganin gimbiya Shuraima 'yar


sarki Husubul Dinar,


Kallo ne ya wakana tsakanin gimbiya Lashmira da Shuraima na dan wani lokaci,


har Lashmira ta budi baki da kyau ta ce wani abu sai Shuraima ta matso daf da ita ta rike hannunta ta tashe ta tsaye,


ta yagi wani yanki a tufafinta ta goge mata jinin da ya zuba a bakinta suka shirya juna. Sannan Shuraima ta budi baki cikin tattausar muryar ta ce,


"Ya Lashmira ina ncman afuwarki bisa ZUBAR DA JININ da na yi miki tabbas ban yi hakan domin kaskanta daraja da martabarki ba sai domin kare zuciyar ki daga kudurun da ke tattarc a al'adar.


ki yi sani ccwa na san ba wani abu ne ya fito da ke a cikin wannan dare ba fuskantar tsananin soyayyar bawa Hilwas da ta addabi zuciyarki.


Tabbas, matsalarmu irn daya ce, domin ni ba komai ne ya fito da ni a dai-dai wannan lokaci ba sai bisa kamuwar da zuciyata ta yi da kyau kaunar bawa Kahzib, irin son da ban taba yuwa wani da namiji ba,


Saboda haka kinga yanzu tsakaninmu sai dai mu hada kai domin saduwa da masoyanmu kafin wayewar gari.


Koda jin wannan doka daga bakin gimbiya Shuraima sai Lashmira ta saki tattausan murmushi, a gare ta sannan ta budi baki cikin annurin fuska ta ce


"Ya ke Shuraima ki yi sani cewa tabbas na gamsu da dukkan bayaninki domin na san a cikin sarakunan da suka halarci GASAR JARUMTA mahaifin ki ne kadai ba shi da wani mummunan kudiri a zuciyarsa a kaina da abbana.


Amma sai dai kafin mi ci gaba da tafiyar mu ina so ka amsa mini tashin tambayoyi kamar haka: -


Shin kuna yakinin cewa bawa Kahzib zai amince da soyayyarki?


Tambaya ta karshe ita ce a ina ki ka samu irin tufafin da na sanya?






Adabi24.com.ng






Da jin wannan tambayar sai Shuraima ta yi murmushi ga Lashmira sannan ta dube ta ta hanyar gyaran lallausan muryar ta kawo gwauron nunfashi ta ajiyc ta ce,


"Game da tambayarka ta farko, ki yin sani cewa duk da cewa bawa Kahzib bai furta min cewa yana kaunata ba tabbas na ga alamun hakan a kan fuskarsa,


a lokacin da muka hada idanuwa da shi a filin gasa,


kin san masu iya magana na ccwa LABARIN ZUCIYA a tambayi


fuska

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads