Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 11148 words

Chapter 2 - DARASI Book 1 Complete Document by Miss Green .txt

Ads the beginning of article before Image

10 Jun 2024

264

Ads at the middle of Article

ina ki ke Nusaiba"?.


"Yaya daga talla na ke,ban siyar da wuri bane shine wani mutumi yanzu ya siye duka yace gobe idan na ɗakko in kawo mishi wani kango zai siye duka,kinga na huta da dukan Amma".


Ƙwalla ce mai zafi ta zubo daga ƙwarmin idanuna na ce"Nusaiba daga yau ba zaki sake talla a gidannan ba wallahi",ina faɗar hakan naja hannunta tana wai gawa ko zata ga Amma don dukkanmu tsoranta muke sosai.


Gidan Inna na kaita inda na baro yanzu, har ta ja ƙofarta za ta rufe sai ta ganmu ni da Nusaiba mamaki ya hanata magana amman fuskarta fal ta ke da mamakin ganinmu.




"Inna don Allah don Annabi ga Nusaiba nan ta dawo wajenki da zama,saboda zamanta wajen Amma babban hatsari ne babba",na fashe da kuka Inna tana rarrashi na.




Nan na ƙwashe duk abinda ya faru tun daga farkon tallan Nusaiba har kawo yanzu,shiru Inna tayi tana tunanin hali irin na ƴarta wato Amaturrahman.




A yanzu hankalina ya ƙwanta sosai don riƙon Nusaiba ya koma gun Inna har ta saka ta a makarantar islamiya da ta boko,sai dai fa har yanzu aƙwai sauran Rina a kaba don yanzu Amma ta ƙara ƙaimi wajen kaini aika tau daman ga haushin na kai Nusaiba gidan Inna wai tunda ni ce na kaita dole yanzu in dinga yin tallan Nusaiba na kayan miya,da yamma kuma tallan taliya da mai da yaji,babu yadda na iya dole ne inyi abinda Amma tace don ni a yanzu daɗi na ke ji da riƙon Nusaiba ya koma gun Inna.






*** *** ***


Jirgin ƙarfe 10 ya hayo daga Tunesia zuwa Abuja,kana ganin yadda ya ke tafiya kasan bashi da cikkakiyar lafiya ajikinsa,don Ammar fari ne daman ƙal mai matsaicin jiki don haka duk wanda ya sanshi zai tabbatar da tabbas ba lafiya ya ke,motoci ne sun kai biyar suka zo tararshi a Airport ɗin suka shiga daskarewa suna sarawa ogansu wato general Ammar.




Kai tsaye ɓangarensa ya nufa sakamakon da sashen Sakinat ya ke fara zuwa amman yau sashensa ya nufa,babu wanda ya faɗawa zuwanshi Nigeria hatta da aminansa basu san da maganar dawowarsa ba.


Sai da daddare bayan yasha baccinsa tare da mafarkin aminsa,ya fito zuwa sashen Sakinat tsit kamar babu kowa sai masu aikinta suna ta kai kawo,da Lantana ya fara haɗuwa sabuwar mai aikin da ta yi,ta durƙusa har ƙasa tana gaisheshi cikin girmamawa ya amsa ba tare da ya kalli inda ta ke ba,sai jin muryarta yaji tana cewa"ranka ya daɗe ai Hajiyar bata nan yau kwananta 4 kenan".




Cak yaja ya tsaya sai a lokacin ya jiyo,Lanta ta haɗiyi wani yawu 'maƙut' don tsabar tsoronsa da ta ke yi,ƙyaunsa da ƙwarjininsa yana ƙara ninkuwa a azuciyarta.


"Kika ce ta yi tafiya?".


"eh yallaɓai" ta faɗi hakan cikin tsoro da fargaba.


Wucewarsa ya yi sama bai ƙara bi takanta ba,har ya zaro wayarsa zai kirawo ta sai kuma ya fasa ya sakko zuwa ɓangarensa yana tunanin hali irin na Sakinat,a shekara 8 ɗin da sukayi da Aure zai iya ƙirga sau nawa Sakinat ta tambayesa zuwa unguwa duk sanda ta yi niyya kawai tafiyarta ta ke yi,har zuwa wasu ƙasashen ma,a kullum tambayar kansa ya ke me yasa duk abinda Sakinat ta ke yi mai bai taɓa tsawatar mata ba duk da yana da matuƙar zuciya amma ta zama ta banza,duk izzar da ya ke da ita in dai ya shigo gida ko baya tsoron Allah to ya zama dole ya zama bawan Sakinat don mugun tsoronta ya ke.


Sakinat ce zaune gaban boka tsidau tana cewa"boka so na ke nima in haihu ko ta halin ƘaƘa ne don ba zan yadda wannan dukiyar da na ke gani ta tafi a tutar babu ba,ayi duk abinda za'ayi ko nawa ne zan biya matuƙar dai nima zan samu abinda na keso."


wa wa keken bakinsa ya buɗe ya ce"ni boka tsidau na yi miki alƙawarin haihuwa a gidan multibuloniya Ammar,akwai abinda zamuyi miki matuƙar kika yi to tabbas za ki samu Haihuwa don haka ki saka aranki ma kin samu". sai ya bushe da wata irin dariya mara daɗin sauraro.


"Tashi ki biyoni kin samu Haihuwa kin gama".


dariya ce ta kama ƙawar Sakinat wato Falmata don tasan abinda bin boka tsidau ya ke nufi,ɗan jiyowa Sakinat ta yi ta kalli ƙawarta da ayar tambaya a bakinta sai dai babu ikon yin maganar don boka tsidau tuni ya yi gaba cen ƙarshen dutsen inda wata ƴar ƙaramar bukka ta ke.


Wa iya zubillah wannan boka aranar sai da sukayi alfasha da Sakinat kuma ya tabbatar mata cewa buƙatar ta kamar ta biya ne.
Masha Allah Ammar shirye ya ke cikin wata tsadaddiyar shaddarsa ruwan arsh ya gyara gashin kansa wanda ya ƙwanta luf luf irin na asalin fulanin usul,fatarnan sai walƙiya ta ke yasha agogonsa na rolex ya yi matuƙar ƙyau,wani irin nishaɗi ya ke ji don ayau zai ga Amminsa bayan shekara 5cif ba tare da sun haɗuba.


Yana shiga motar dieban yaja sauran motocin suka biyosa ya rufe idanunsa kamar mai jin bacci daman kuma aƙidarsa ce kuma haka Allah ya halicce sa baya mintina ba tare da ya yi hakan ba,hakan baƙaramin ƙara masa ƙyau ya ke ba,ga waɗanda basu sanshi ba sai suce iyayi ne.








Wata muguwar harara Sakinat ta bugawa ƙawarta Falmata ta ce"gaskiya Falmata baki da mutunci da ki ka haɗani da wannan bokan gashi yanzu ya haɗa jiki dani in banda wari da hamami babu abinda ya ke,ni wallahi Allah ya isa kawai kuma yanzu ba sai
Anjima ba Zamu je hospital a dubani".
Dariya Falmata ta yi bata ce komai ba suka cigaba da tafiyarsu har suka kai bakin titi suka tari mota suka tafi,duk jikin Sakinat ciwo kawai ya ke.


Ko da aka duba ta lafiya ƙlau babu wata cuta sai anan taji wani babban abu ya wuce a maƙogoranta ta amshi ruwan sanyi ta kora,suka hau mota Falmata ta wuce gida ita kuma Sakinat ta wuce Adamawa wajen mahaaifinta.






Jiniya ce ta cika titin baki ɗaya ko da ba'a gaya maka ba kasan wani mai babban muƙami ne zai wuce don haka sai matsawa a ke.




Salati Sakinat ta yi ganin motocin mijinta G.A M wato general Ammar Muhammad.










*Ummu Maher ce*
*DARASI!!*




Free page 4/5




Rabiatu Bashir
(ummu maher)miss green.




*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu ta online zasu biya 2k*










04/05




. . . . . Sakinat aranar ta koma Abuja Don firgici da tsoro,duk hatsabibancin Sakinat tana matuƙar jin tsoron Ammar don shima hatsabibin kanshi ne,wannan asirin da ta yi mishi ma da wani babban jigo ta haɗashi har aka samu abinda a keso.




Har gudawa Sakinat ta yi don ta tsorata da ganin Ammar a Adamawa,to yaushe ma ya dawo ba tare da ya sanar mata ba?kuma me yaje yi Adamawa?abin tambayar ta shine ba dai gidan mahaifiyarsa yaje ba?da sauri ta tashi daga zaunen da ta ke,tana girgiza kai tana cewa"no.no.no ba zai yiyu ba ace yaje wajen mahaifiyarsa ba,don tafi kowa sanin cewa farraƙu ta saka aka yi musu a tsakaninsa da mahaifiyarsa.




Har dare Sakinat tana sukuku gashi ta kira aminiyarta Falmata ringing yafi goma bata ɗaga ba,ƙarshe ma taji an kashe wayar wayar.


"Wato ma kada in dame ta shiyyasa ta kashe wayar ko?shegiya mayya kawai ai nasan tunda ta ce baƙo za tayi to lallai tana cen tare dashi"ta yi wurgi da wayar hankalinta a tashe,ga ta da tarin tambayoyi amman kuma babu mai amsa mata.
Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.




Sai kusan ƙarfe uku sannan bacci ya ƙwashe ta daman babu halin yin sallar asuba don Sakinat sai taga dama ma take yin sallah,wa iya zubillah.








Ammar kuwa yana isa Adamawa ya kira Aliyu babban abokinsa mazaunin Adamawa amman wani lokacin yana Abuja Babban gidan da Ammar ya sai mishi,yana kiransa bugu ɗaya ya ɗaga yana tsokanarsa da angon sakinat,"mlm bar wannan tsokanar kana cikin gari ne?kazo zaka yimin jagora wajen AMMI."


"Welldone aboki na ina yiwa Allah godiya da ya karkato da hankalinka akan mahaifiyarka,insha Allah yanzu zanzo.


Sai da Ammar ya jira yazo sannan suka tafi suna ta hirarsu ta abokai,daman su uku suka tashi Amir,Ammar,sai Aliyu,ana kiransu da first A.
Khalisat tana tafe tana bitar karatunta na hadda alokacin ta fito kenan za taje islamiyya,sauri ja da baya ta yi don ganin motoci kala sunfi goma a bakin gate Ɗin gidan kana ganin motocin ba sai an gaya maka ba kasan sun haɗu sosai.


Aliyu ne ya fara fitowa yana kallonta cikin murmushi,itama murmushin ta mayar masa tana sake kallon motocin gabanta yana faɗuwa.


Ƙafar sa ya fara sakowa kafin ya fito,da sauri Khalisat ta ja da baya kamar za ta faɗi badon tsohuwar motar Ammi ta tare ta ba da tuni ta faɗi.


Ya.ya.ya.ya.sai kuma ta zunduma da gudu ta yi cikin gida tana kiran Ammi!ammi!!Ki fito kiga wani abu,kafin ta gama rufe bakinta tuni Ammar ya shigo shi da amininsa Aliyu.


Kusan daskarewa Ammi ta yi a tsaye tana kiran sunan Allah tare da godewa Allah daya dawo mata da farin cikinta wato ɗanta Ammar.




Da gudu ya rungume Amminsa yana kuka yana kiran"ilove u my Ammi na ki yafe min don Allah,na tuba bazan sake ba ya haɗa hannayensa alamar neman yafiya.


Ita ma kukan ta ke tana "son na yafe maka Allah na gode maka da ka dawo min da farin cikin raina".




aranar waɗannan Familyn suna cikin farin ciki sosai,ya yiwa Ammi alƙawarin sai ya yi sati biyu kafin ya koma don ya samu hutu,sosai Ammi taji daɗi tana ƙara saka mishi albarka,don tasan duk abinda ya yi ba da sanin sa bane asiri ne.
Tunda Ammar yaje bai kira Sakina ba,hankalinta ya tashi sosai ta dinga kiransa a waya amman yana gani yaƙi ɗaukar wayar ƙarshe ma ya kashe wayar.




Suna zaune da daddare suna cin abinci Khalisat ta kalli yayanta,ta ɗauki ruwa ta fara sha ai Ammar yana ganinta ya yi saurin ƙwacewa yana ce wa"inye lallai Khalisat kin samu sarari yanzu ruwa ki ke sha kina cin abinci?.
"Wallahi Yaya" ranƙwashi Ammar ya kai mata yana ce wa"me ɗan ƙaramin baki kawai.


Murmushi Ammi ta yi tana kallon ƴaƴan na ta cikin so da Ƙaunar su,tana roƙon Allah ya bar maya ƴaƴanta guda biyu da ta mallaka a duniya.














*** *** ***

Amma ta ƙara matsamin sosai yanzu don talla na ya ƙaru yanzu inyi na safe inyi na rana inyi na dare,bani da lokacin hutu Baba na babu yadda zaiyi don yanzu ma har ya fara shiru da bakinsa,tunda ita dai amma ba dai na wa za ta yi ba,don haka ya tattara ta ya watsar da ita don rashin kunyar da ta ke mishi abin yana damunsa.


Ni daman ba a zancen arabi ballan tana boko kullum ina yawo a gari gayyar talla.







Rannan da daddare ina tafe tsoro fal a ciki na don ban taɓa yin dare irin na yau ba,don nasan idan na koma gida sai Amma ta yi gunduwa2 dani.




Wani kango nazo wucewa naji wari kamar nawiwi,na toshe hancina ina kakarin amai,kawai sai naji wani yana ce wa"kai Ba-ba waccen yarinyar me ta ke toshewa hanci ne?".


"oho bari muje muji me ta ke toshewa hanci. . . ...








Anan zan tsaya don rashin comments.






*Miss green ce*
*DARASI!!*




Free page 6/7




Rabiatu Bashir
(ummu maher)miss green.




*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu ta online zasu biya 2k*
06/07



. . . . .har nazo ƙwanar layinmu sai naji kamar ana bina a baya,ga warin taba dana wiwi ya haɗe waje ɗaya suna bada wani irin ɗoyi me wari,sauri na fara yi ina waiwayansu don tun ina hangosu daga nesa yanzu kurkusa na ke hango su.




Gudu sosai na fara yi amman kun san gudun mace dana miji ba iri ɗaya bane dai gashi sun cimma ni,kuka na farayi ina basu haƙuri amman ko sauraro banga suna yi ba,don ko ɗigon tausayi babu a fuskarsu,abinda naga ɗaya daga cikinsu yana shirin aikatawa ne yasa na buɗe bakina na taƙarƙare na rusa uban ihu,yana zuge ta zugen wandonsa yana lasar
Baƙin bakinsa wanda ya gaji da shan tabar wiwi.




Wata shaƙa babban nasu ya kawo min tare da duka na akai nan da nan na daina ganin komai sai duhu,saurin ɗaukata suka yi da ya ke dare ne babu wanda ya gansu suka shiga dani wani kango.
"Kai ba-ba ya zamuyi da wannan yarinyar kada fa a kamamu".?




"au tsoron kamen ka
Ke kai" ?,kawai mu ƙwashi rabonmu mu mu wuce mu bar ƴar talla masu son kuɗin jaraba ai daman ƙarshen son kuɗi kenan",ya faɗi hakan yana lashe bakinsa.




"Haba Amma ta ya ya zaki ƙwanta ki yi ta bacci amman kuma ƴarki bata dawo ba har yanzu?ki duba agogo ƙarfe goma na dare fa?gaskiya Amma wannan mummunar ɗabi'ar da ki ka ɗakko ba za ta haifa miki ɗa mai ido ba",yana faɗar hakan ya yi hanyar waje yana cigaba da mitarsa kamar zai cinye ta,amman matar nan Ƙara juyawarta ta yi tana baccinta har da minshari,Haruna ma da ya ke ƙarami kuka ya dinga kuka ganin Fahima bata dawo ba,don ya saba ita ke kaishi ya yi fitsari.


A hankali ya ke tafiya yana ɗan duba lungu2 na layinsu,ƙwatsam ya hango wani lungu,ci ke da ƴan daba suna shawarwari a tsakaninsu akan su aikata mata ko kada suyi.


Shahada ya yi yaje wajen ya haskosu da babbar fitilarsa,da sauri suka jiyo dukkansu kana ganinsa kasan shine mahaifin yarinyar nan don har hasken da ƙyau irin na fulani duk na shi ne.


"Aha kace kazo ne ka karɓi ƴar ka ko"?.


sai suka tuntsire da wata mahaukaciyar dariya suna nuna baban Fahima.


Kukan kura ya yi ya bige mutum biyu Alokaci guda da ya ke sun bugu sosai suka zube a wajen,saura mutum biyu,da sauri ya yo kansu suma suka fita da gudu,ya tsugunna yana hawaye har sun fara yagawa Fahima kayanta abin tausayi.


Kawai sai yaji saukar wani abu a bayansa tun daga nan bai ƙara sanin inda ya ke ba.










*** *** ***


Da wuri Sakinat ta dira a garin yola babban birnin adamawa,tana sanye da glass baƙi no respect wanda ya gaji da haɗuwa yana sheƙi da walwali.


Ta saka ƙananun kaya komai na jikinta ana gani ita daman ƙirar slindium ne da ita babu cinya babu sharaɓa sai fari wanda har yawa ya yi mata saboda bleaching.


Chewin gum ne abakinta tana taunarsa yana ƙara ƙara ras-ƙara ras,alamar za ta yi rashin mutunci kenan .
Bata sha wahalar gane gidansu Ammar ba don rabonta da zuwa shekara shida kenan,kallon gidan ta ke tana ya mutsa fuskarta,taja trolley ɗinta tana wani yauƙi da yanga kamar mutanen gidan suna kallonta.


Hanan tana sama tana hango ta,da sauri ta sauko don ba ta son Ammi tasan abinda zai faru don wallahi ba za ta bari wannan matar ta shigo musu gida ba,suna cikin farin cikinsu ta kawo musu baƙin ciki.


"Ke makira ina zaki"?.


Hanan ta faɗi hakan tana ɗaga mata gira tare da tare hanya.


Wani banzan kallo Sakinat ta yi mata ta cire gilashinta tana kallonta ta ƙasan glass ɗin, sannan ta ce"Hmm Hanno ki ke ko wa?to ma dai ko me ye sunanki?,ko wannan siririyar bafulata na bata isa ta ce za ta hanani shiga wannan ruɓaɓɓan gidanba wanda ko albarkacin fenti ba ya samu.


Idanun Hanan suka yi jawur jin zagin rashin mutuncin da Sakinat ta ke musu,da sauri ta nuna Sakinat da hannu ta ce"Hmm da ba asan asalin balbela ba da sai ta ce daga misra ta ke,ke kin manta gidan na ki uban ko albarkacin siminti bana tunanin ya samu"?.


"kuma kinga gidannan kaf babu siriri sai wannan makauniyar uwar ta ki wacce har ta mutu bata gani saboda baƙin cikinki dana wannan baƙin basa muden uban na ki,kuma kaf gidan na mu babu wanda ya fito ba ta hanya ta halak ba,wani kuwa sai da a kayi cikinsa sannan aka yi aure. . .




Cikin matsanancin fushi Sakinat ta kaiwa Hanan wani mari,Hanan ta shafa wajen da hannunta ta ce"ko yanzu Sakinat na fiki cin ribar zance tunda gashi har kinyi mari saboda fusata,amman fa baki mari banza ba don ba a marin wannan ƙyaƙyawar fuskar tawa a zauna lafiya ko mijinki ne kuwa ballan tana ma ke."


wani mari Hanan ta kaiwa Sakinat wanda sai da yasa ta riƙe hannun ƙofar shiga farlon,wata shaƙa Sakinat ta kaiwa Hanan,ta kama maƙogoron ta Hanan ta kama kararin mutuwa,Ammi ta fito za ta gidan barka ta hango abinda ya ke faruwa.


Da sauri ta ƙaraso tana rabasu tana mamakin ƙarfin hali irin na Sakinat,sa ƙer Ammi ta ɓanɓare Hanan ta ƙwanta luf a hannun Ammi kamar ba ta numfashi.


Sakinat tayo kan Ammi za ta haɗasu duka,suka jiyo sallama Ammi na kallon tsinanniyar shigar da Sakinat ta yi wai a matsayin matar Aure matar ɗanta tilo.


Amir ne da matarsa har da ƴaƴansa biyu,sosai sukayi mamakin ganin Sakinat a gidansu Ammar don sun san takun saƙar da ke tsakaninsu.


Amir ya ce"Ammi lfy me ya samu Hanan ɗin?wani abu ne ya same ta?."


gaba ki ɗaya ya tambayeta,Ammi ta shaida masa duk abinda ta gani a lokacin da tazo,bata gama ƙarasawa ba me gayya me aiki ya fito yana sanye da kayan motsa jiki don bai san abinda ya ke faruwa ba,yana zuwa Sakinat ta saki kuka ta faɗa jikinsa kamar ƴar yarinya.
*** *** ***


A wajen mahaifin Fahima ya faɗi baya motsi,ƴan patrol suka zo wucewa suka hango ƴan daban nan suna Ɗaukar Fahima,da sauri suka zo wajen suna zuwa suka arce da gudu amman an kama guda ɗaya.


Aka kai su Fahima asibiti aka fara yi musu

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads