Header Ads
Showing 9001 words to 11148 words out of 11148 words

Chapter 4 - DARASI Book 1 Complete Document by Miss Green .txt

Ads the beginning of article before Image

10 Jun 2024

266

Ads at the middle of Article

kalli Sakinat ya ce"tashi ki koma ɗaki ki kwanta kinji Allah ya yi miki albarka".


da sauri Sakinat ta tashi kamar daman ta matsu ta tashi ɗin,Ammi tabi bayanta da kallo ta ce"Alhaji yanzu ya ya ka ke ganin za ayi"?.


"Insha Allah komai zaizo da sauƙi amman kafin nan zanyi shawara zuwa ko gobe fatanmu Allah ya tabbatar mana da alkhairi.




***


Ammar yana ɗakin motsa jikinsa yaji a jikinsa kamar ana kallonsa,da sauri ya juyo,Sakinat ce tsaye a kansa ta lu-la duniyat tunani,wata uwar tsawa ya buga mata ita kuwa tana cen kogin tunaninsa yadda gashin ƙirjinsa ya ƙwanta luf luf gwanin sha'awa ruwan gumin jikinsa ya jiƙa duk beauty ɗin skin ɗinsa abinka da ƙyaƙƙyawa sai ya yi wani ƙyau mai ɗaukar hankali.
Wani banzan kallo ya yi mata a karo na biyu sannan ya tashi ya yi tafiyarsa.
Sakinat ta bisa dana mujiya kamar za ta haɗiyesa tsabar so da ƙaunarsa.




"Ammar!"Alhaji muhammad ya faƊi sunansa cikin babbar murya ya ce"me sunan manya Ɗazu misalin Ƙarfe uku da rabi na rana an Ɗaura aurenka da wannan Yarinyar Sakinat abisa yardar waliyyanka da waliyanta don har garinsu na je muka taho da babanta".




Kansa a sunkuye tun da Alhaji ya fara magana baice komai ba,don iyayensu sun yi matuƙar ƙoƙari wajen basu tarbiyayya,idanuwansa sunyi jawur sosai jijiyoyin kansa sun tashi ruɗu ruɗu,ba Ammar ba hatta Khalisat sai da taji wani iri har a cikin zuciyarta.




Tunda Ammar ya Tashi daga wajen mahaifansa kai tsaye motarsa ya hau ya fita,wayarsa ya ɗauka ya kirawo Aliyu ringing na farko ya ɗaga yana tsokanarsa da ango don ɗazu yaji komai na game da auran da Dad ɗinsa ya yi masa.




Banza Ammar ya yiwa Aliyu ya cigaba da shaƙiyancinsa har ya yi shiru sannan Ammar ya ce idan har ka gama ka sameni a hill&vally.


Waje ne kyakkyawan waje wanda ya tsaru,an ƙawata shi da followers da bishi yu kala kala,ga sanyi da ni ima ta ubangiji,mutane da dama suna zuwa wajenne saboda shaƙatawa,ko kuma hutawa saboda zuciyarka ta samu reliep.


Yana zaune yana ta kallon ruwan da ya ke ta zubowa ta cikin ƙasa,shima wajen an ƙawata shi sosai gwanin ban sha'awa.


Tunani kawai ya ke yi a game da makomar aurensa shi da wannan mummunar yarinyar,sam ba irin kalar Sakinat ya ke buƙata a matsayin matar aurensa ba,gaba ki ɗaya ma dai ya tsani yarinyar sosai,har bai san adadin tsanar da ya yi mata ba.




Yana zaune kiran Amir ya shigo wayarsa ya ɗaga a hankali kamar ba soja mazan fama ba,nasiha mai ratsa jiki Amir ya dinga yi mai a game da auren da mahaifinsa ya yi masa,kada ya bijirewa mahaifansa ya yi abin da suke so wataran zai tsinci haƘurin a gaba.




Tnx kawai ya cewa Amir sannan ya kashe wayarsa saboda tsabar haushi,don shi haryanzu bai yarda zai tsinci wani alkhairi a gurin wannan fush girl ɗinnan ba.
Ammi ma ta rasa mai yasa tunda Mijin na ta ya yi mata albishir da ɗaura auren Sakinat da ɗanta ta tsinci kanta a mai mummunan faɗuwar gaba ta rasa me ya ke yi mata daɗi,ba wai auran ta tsana ba a ah kawai zuciyarta ce bata aminta dashi ba,musamman yadda taga Ammar gaba ki ɗaya ya canza alokaci ɗaya,ta tsani abinda zai ɓata ran Ammar tana yi masa wani irin mugun so da tausayinsa a matsayinta na mahaifiyarsa,Allah kaɗai yasan irin zaman da zasuyi shi da yarinyar,amman koma dai menene tana roƙon Allah ya kawo sauƙinsa cikin ruwan sanyi.
Sannan tana yi masa fatan samun zaman lfy . . ..


"Tunanin me ki ke yi Zulaihat"?.
da sauri Ammi ta cire tagumin da ta yi ta yiwa mijin na ta murmushi don kada ya fuskanci halin da ta ke ciki.




Murmushi ya yi sannan ya ce"Zulaiha na sanki tun kafin ki kai shekarun haka shekararki 14 aka auramin ke alokacin ni kuma ina da kusan talatin kuma ina matsayin soja a wannan lokacin,ki kayi haƙuri ki ka zauna dani a halin da na ke ciki na yaron soja don kowa yasan halin zuciyar soja awannan lokacin harma da yanzu,to me yasa ki ka kasa haƙuri akan wannan auren dana ɗaurawa ɗanki?aƙwai abubuwa da yawa dana duba kafin in haɗa wannan aure ba da ka na yi saba,wannan yarinyar ba tada gata sai Allah akan ɗanmu ta kamu da ciwon zuciya fa?idan ƴarki ce zaki so hakan ya faru da ita?to kinga ba zaki so ba."




Tun daga nan Ammi bata sake haɗe ranta ba kullum cikin yiwa ɗanta nasiha ta ke,tare da addu'ah.






Tafiya ce ta kamasi zuwa bauchi garin aminin Alhaji Muhammad,da ammi za aje amman kuma sai ta ce ta fasa tana da buki,da Khalisat da Sakinat aka yi tafiyar sai Alhaji don shi uban gayyar Ammar yana Abuja.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.


Aranar bayan sun tafi kan hanya sukayi hatsari aka nufi dasu asibitin da ke kusa,shi dai Alhaji abin sai addu a,Sakinat da Khalisat kuwa ɗan kukkurjewa ne kawai.




Aka kirawo su Ammi a waya cikin tashin hankali tazo,yadda taga mijinta abin sai addu'a,ta kirawo Ammar tana kuka ta ce yazo ta faɗa masa halin da suke ciki,kai tsaye daga Abuja ya taho hankalinsa a tashe.


Da ƙer Alhaji ya fara magana yana yiwa Ammar nasiha akan Sakinat,kuka kawai Ammar ya ke na ganin halin da mahaifinsa ya ke.






*Miss green ce*
*✨🌈DARASI!!!🌈✨*
(Topic)
*` _``a love&```_ destiny story*




By
Ummu Maher(Miss green)🍀💚




*Littafin na kuɗi ne ban yarda ki karanta mun baki biyani ba,Gamai buƙata n cigaban labarin zai biya ₦300 normal* group...Vip group
₦500... Special₦1k....zaku iya Turo da katin MTN ta wannan number 07068606171
ko kuma ku tura ta wannan account number 2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith Bank.




*Free page*


18/19




Maganar ƙarshe da mahaifin Ammar ya faɗa shine"Ammar kada ka wulaƙanta wannan yarinyar kada ka juya mata baya,don kaga bani da rai,kada ka taɓa rabuwa da ita ma'ana ka saketa matuƙar ka saketa to ka saka a ranka babu ni babu kai."




wannan maganar ita ce ta ƙarshe da ya faɗa ya fara wani irin tari mai sarƙe maƙoshi daga nan rai ya yi halinsa,babu irin kukan da Ammar bai yi ba na rashin mahaifinsa ga abu goma da ashirin wai kada ya yarda ya saki Sakinat,shi ya rasa me yasa ma ƙwata2 ko kallonta ba yasan ya yi,yadda kasan wata mujiya haka take a wajen Ammar amman ya zamar masa dole ya fara sakin jiki da ita ko don nasihar mahaifinsa.






Bayan wata biyu rannan Sakinat tana zaune suna hira da Ammi,aka yi sallama da gudu Sakinat ta rungume Falmata ƙawarta ta yarinya ta,sosai taji daɗin zuwan Falmata don tunda ta yi aure ko dangin mahaifiyarta basu zo ba,don basu san ma ta yi auren ba.




Kalle2 Falmata ta shiga yi sosai irin kallon tsaf ɗinnan,Ammi sai kallonta take tana mamakin hali irin na wannan baiwar Allah.




Sai da Sakinay ta ɗan dunguri Falmata sannan ta dawo cikin hayyacinta,tana harar bayan Sakinat don gani take Sakinat bata dace da wannan gidan ba ita ce ta dace dashi,don haka ko ta halin ƙaƙa sai ta zauna itama a wannan gidan kuma ta fitar da ƙawarta Sakinat.




Tunda Falmata tazo gidan babu abinda take sai zuga Sakinat akan cewa wai tsabar baya sonta har yanzu yaƙi ya kaita gidanta ya barta a gidan iyayensa,wani lokacin kuma ta ce kinga gidansu kamar aljannar duniya ko ina gwanin sha'awa,duk yadda akayi komai shi yake a gidan kuma yana jin maganar mahaifiyarsa.




Da ya ke Sakinat sokuwa ce sai maganganun Falmata suka fara tasiri aranta har ta fara ganin ayanzu za ta iya fito na fito da Ammi don tun ba yau ba tana ganin irin abubuwan da Ammar ya ke wa Ammi,yana matuƙar girmama maganarta don har yafi jin maganar mahaifiyarsa da ta mahaifinsa.




Acikin satin Ammi babu irin rashin kunyar da ba ta gani ba awajen Sakinat kuma ta lura Falmata ce ke ƙara zugata,don haka duk sai ta watsar da su ta cigaba da sabgoginta,don dama Khalisat tana boarding Ammar kuwa ya yi tafiya zuwa ƙasar England wani aiki.






Ƙwanan Falmata biyar ta haɗa kayanta don tafiya gida,ta tambayi Sakinat ina ne ɗakin Hajiya,babu musu Sakinat ta nuna mata ta ƙwanƙwasa alokacin Ammi tana azkhar.
Ammi ta buɗe mata ta shigo tana gaida Ammi,ta amsa tana mamakin ganinta bata gama mamakin ba ta jiyo Falmata tana ce wa.




"Da man gida zan tafi shine na ce bari inyi miki sallama sannan in faɗa miki wata magana don nasan baki sani ba,lulluɓin biri aka yi muku.




Da mamaki Ammi ta ke kallonta tana mamakin hali irin na Falmata na munafurci,wato don taga ƙawarta ba ta nan shikkenan sai kuma ta yi gulmarta.




"Hajiya Sakinat fa kafin ta auri ɗanku sai da aka cire mata ciki har sau biyu,kuma wallahi har yanzu bata daina bin maza ba".




da sauri Ammi ta ɗaga mata hannu sannan ta ce cikin tsawa"get out in my room".




da sauri Falmata ta fito har tana haɗa hanya tana da na sanin zuwa wajen Ammi don yadda kasan zaki haka ta juye mata.




Akan hanya suka haɗu da Sakinat sannan ta rakata har bakin gate,tana mamakin sauyin Falmata lokaci ɗaya.








Ammar yana dawowa Ammi ta sakashi a gaba da ya tafi da Sakinat sabon gidansa na Abuja,babu yadda ya iya haka ya tafi da ita ransa baiso ba.






Wannan tafiya itace ta zamewa Ammi wannan mummunan tabo a rayuwarta don tun daga ranar Ammar bai sake zuwa wajen mahaifiyarsa ba,don tun bayan komawarsu da Sakinat ta ga Ammar ba ya ko kallonta ballan tana ta saka ya yi mata magana.


Da kanta ta nemi Falmata suka haɗa kai aka raba tsakanin ɗa da uwa Ammar da Ammi.














*Cigaban Labari*


*Fahima*
-------------------


A yanzu Amma ta matsamin wai acikin mane ma na wai in fito da mutum ɗaya don ita ta gaji da kallona babu aure,abin har mamaki ya ke bani don har yanzu ko shekara sha biyar ba amman ake min zancen aure.




A cikin masu sona aƙwai wani Alhaji Tasi'u mai nera,shine wanda Amma tafi don yana matuƙar jiƙata da kuɗi.




Ita kuwa Fahima ta yi mugun tsanarsa don mutumin mugun ɗan iska ne duk ranar da yazo sai ya nemi daya taɓa jikina ni kuma in ƙi yarda.


Kuma kamar maye gobe ma sai ya dawo,kuma a ƙalla ko da baiyi shekara hamsin ba to kaɗanne.








*miss green ce*
*DARASI!!*




Free page 20/21




Rabiatu Bashir
(ummu maher)miss green.




*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu ta online zasu biya 2k*






Sakinat ce a zaune tana waya da Falmata, kana ganin Sakinat kasan ranta a ɓace ya ke ta ce"Falmata yau watanmu biyar da zuwa wajen bokannan amman har yanzu banji wani chanji ba da zaisa in gane ina da ciki,abin yana damuna Falmata ni dai idan babu hali kawai mu chanja wani bokan kawai ina ganin zaifi ko"?.




shiru Falmata ta yi tana mamakin hali irinna Sakinat don duk bin bokaye irin na Falmata bata ka ma ƙafar Sakinat ba,ko da ya ke Sakinat ta yi mata zarra a fannin kuɗi dole ta fita fitowa gari.




"Eh aƙwai wani boka da na ke tunanin zai iya wannan aikin wanda matuƙar ya yi miki aiki to fa shikkenan,zaki ganki da ciki a jikinki ko da na aljanu ne kuwa".




da sauri Sakinat ta ce"haba Falmata ya zaki ce wai ko da na aljanu ne,idan na samu cikin aljanu ai an samu matsala lafiyayye na ke son haifa".




Ƴar dariya ce ta kusa kufcewa Falmata don tasan duk wannan yawon da suke yi ba lallai ne ta haihu ba,don tun tana budurwa ta gama zubarda abinda tun a waje".




Ƙalubale gareku ƴan mata ku daure ku riƙe mutuncinku domin shi mutunci madara ne,kuma daga inda namiji ya yi amfani da ke ko da ciki bai shiga ba to kin gama cutar kanki,gwara duk rintsi ki daure ki kaiwa oganki(mijinki)budurcinki na ƴa mace,wallahu a 'alam.




Nan dai Sakinat da Falmata suka shirya zuwa har Ghana wajen wani tsohon mushriki don Sakinat ta samu Haihuwa,washe gari da wuri suka ɗauki hanya don ma jirgi zasu shiga sai Accra(Ghana).




Sun sami layi sosai don haka suka jira har layinsu yazo,suna shiga Sakinat ta fara toshe hancinta don wani irin mugun warin da wannan mushrikin bokan ya ke,Falmata ta riƙe hannun Sakinat tana janta don ta daina rufe idon,don idan bokannan ya zuciya zai iya gamaw dasu duka ya shanye musu jini.
Tun kafin su faɗi abinda ya kawosu Bokan ya fara faɗa musu duk abinda suke so ayi musu,ya janyo wani glass yana nuna musu abinda ke ciki.


Wata yarinya suka hango kyakkyawar Bafulata na suka hango yarinyar ba za ta wuce 13zuwa14 ba,cikin tsoro Sakinat ta ce"boka wannan kuma wacece?menene haɗinmu da ita?"


cikin sauri bokannan ya buɗe mushen bakinsa ya ce"ita wannan yarinyar ita ce za ta kawo ƙarshen matsalarki."










Alhmdh.




Anan na kawo ƙarshen book 1,kuma na gama free page idan ka tashi biyan kuɗinka ka neme ni ta wannan number.




07068606171






Ga
Details


*Littafin na kuɗi ne ban yarda ki karanta mun baki biyani ba,Gamai buƙata n cigaban labarin zai biya ₦300 normal* group...Vip group
₦500... Special₦1k....zaku iya Turo da katin MTN ta wannan number 07068606171
ko kuma ku tura ta wannan account number 2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith Bank.


*Miss green ce*

Ads At the End of Article
2
3
4

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads