Showing 15001 words to 18000 words out of 20427 words
Chapter 6 - INDA BA KASA by Ummu Maher (miss green).txt
NA
*_®️UMMU MAHER(MISS GREEN)🍀_*
*_AREWA BOOK👉🏻_*
INDA BA ƘASA!!!:: https://arewabooks.com/book?id=63ce1eb0ec00e12124ce9eb0
---------------------------
*_WATTPAD👉🏻_*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
---------------------------
*_🔥GAWURTATTU UKU🤟2023_* ---------------------------
*_TALLAH TALLAH TALLA🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️_*
_A HAYYEH SAMAH MATAH💃💃💃💃💃🏻💃🏻_
*Ku shiga wannan link ɗin don zaɓar kaya masu rahusa👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻*
https://chat.whatsapp.com/G6BmHCxso0rDZyWVQGgYYj
----------
No
07067964894
*_INA KUKE MATAN KWARAI MATAN DA SUKA AMSA SUNAN SU NA MATA A DUNIYA KU GARZAYO KUZO M A C DON ZABEN NA KWARAI KI DAURA ASAN KIN DAURA SAI ATAMFA DA LACE DA SHADDA, MATERIAL WITH SHOE'S AND BAG WITH JEWELRIE DAGA MAMAN ANNUR COLLECTION._*
*_ANAN KWALIYA ZATA MAIDA KUDINTA GAREKI, KIFITO ASAN KIN FITO KIN FASA TARO SAI M.A.C AKAN FARASHI MAI RAHUSA SAYEN NAGARI MAIDA KUDI GIDA IYA KUDIN KI IYA SHAGALINKI🤝_*
*_TANA KANO TANA AIKAWA KO INA DA IKON ALLAH A CIKIN AMINCIN DA YARDAN UBANGIJI_*
*_YAN UWA INA MASU SON SUYI SANA,A BASU DA JARI TOH GA DAMA TA SAMU, INJI MAMAN ANUR DON ZAKU IYA DAUKAN KAYAN MU KU TALLATA KU DORA NAKU RIBAN SAMA ZAMU AIKA MAKU KAYA GA MAISHI DA SUNAN KU A DUK INDA CUSTOMER DIN KU YAKE BA TARE DA MUYI SAVING NO BASHI BA KUMA BA ZAISAN BA DAGA WURIN KI KAYAN YA FITO BA TAKEN MU GASKIYA DA AMANA, MUM ANNUR COLLECTION DA KARAMAR RIBA MUKA DOGARA SABODA NEMAN ALBARKA SAI KUN ZO 👏👏👏👏👏_*
Page⬜8
---------Da sassafe Halima ta tashi,ta shiga kitchen da kanta ta girka musu abincin karyawa,ƙamshi ya fara tashi kai kace gidan amare ne.
Ummita tana ganinta duk abinda take yi,ta cije leɓenta sosai ganin Har Halima ta sauke ferfesun kaza,wanda yake ta tashin ƙamshi gwanin sha'awa yasha kayan ƙamshi.
Halima ta sauke ta zuba komai acikin foodflask me kyau,wacce ba sai an gaya maka ba kasan ta masu kuɗi ce sosai,ta gama jera abincinta akan dining,sannan ta wuce ɗakinta don shiryawa don yau ma MD ya shaida mata da wuri zai fita,saboda ƴan jam'iyayya na nan suna jiransa ta shiga ɗakinsa don tayar dashi.
Ummita na ganin ta shiga ɗakin,tayi wuf ta fito ta shiga kitchen ta duba sosai ta samu gishiri,tayi wata irin muguwar dariya sannan ta ɗakkoshi ta cika chokali har guda biyu ta zuba a farfesun,ta ɗan juya kaɗan yadda babu wanda zai fahimci abinda aka saka.
Da sauri ta koma ɗakinsu,ta iske Khairat tana azkhar,jikinta Ummita yayi sanyi sosai ta sunkuyar da kanta ta wuce.
Khairat ta bita da kallon takaici,don tasan duk yadda akayi wani abin take son a'ikatawa,don tasan halin ƙanwarta aƙwaita da mugun hali.
Halima ta matse sosai acikin ƙananan kaya,tayi kyau sosai daman gata irin siraran mutane ne,irin ƙirar turawa silindium amman Halima nada shape ɗinta dai dai gwargwado.
MD ma yayi kyau cikin manyan kayansa,shadda fara sol sai walƙiya take,yadda kasan wata acikin zarah,Halima sai kallonsa take saboda yadda yayi mata mugun kyau.
Ya riƙo hannunta sannan ya hure mata idonta ya ce"habibty kallon yayi yawa haka?".
Murmushi kawai Halima tayi ta wuce ba tare da ta ce komai ba,suka zauna kan dining Halima ta buɗe komai,ƙamshi ya bugi hancin MD ya lumshe idonsa sannan ya ce"i'm really miss this delicious food Halima".ya faɗi hakan yana janyota zuwa kusa dashi.
A hankali ya fara kurɓar ruwan shayin,sannan ya fara cin farfesun cikin nutsuwa,sai dai yana kaiwa bakinsa yaji wani irin mugun gishiri me firgita harshe.
Da sauri ya furzar sannan ya goge bakinsa da tissue ya kalli Halima wacce itama shi take kalla saboda yadda taga hankalinsa a tashe,uwa uba ma bata san abinda yasa ya furzar da abincin ba.
Baban Baby lafiya kuwa ka zubar da abincin?ko baiyi daɗi bane?".ta faɗi hakan hankalinta a tashe.
Ganin hankalinta ya tashi ne yasa ya ce"next idan zaki zuba gishiri ko magi adanga kula,don gishirin yayi yawa Halima kamar zai cire harshe".
Da sauri Halima ta ce"gishiri kuma Baban Baby?wallahi ni ban ma zuba gishiri ba,magi ne kawai ma sanya?".
Ta faɗi hakan da tsoro fal akan fuskarta,don dai tasan ita bata zuba gishirin ba.
A hankali ya shafi kumatunta sannan ya ce"muje ki rakani Halima don mutanen nan sun dameni,don tun ɗazu suke ta bugomin waya".
Halima ta tashi ta wuce ɗakinta,ta ɗakko jalbab ɗinta ƙato har ƙasa sannan ta rakoshi har waje,sai da securities ɗinsa suka shir shiga motocinsu sannan ta dawo.
Jikinta har yanzu a matuƙar sanyaya yake,gani take tamkar cin fuska MD ke son yi mata,to idan banda cin fuska yaushe ma da ta saka gishirin ita kanta a girkin?saboda ja mata kunne da likitoci sukayi akan ta daina cin gishiri sam,saboda hawan jinin daya sako ta a gaba,sannam sunce matuƙar tana son ta samu ciki to ta ƙauracewa cin gishiri,don yawan cin gishiri yana kawo ruwan mahaifa,daga nan kuma sai kaga cikin yaƙi samuwa.
Ta tashi a hankali ta buɗe foodflask ɗin ta fara shan farfesun,da sauri ta furzar saboda mugun gishirin daya ziyar ce ta,ta goge da tissue tana kallon farfesun cikin mugun tsoro,don ita dai tasan bata zuba gishiri cikin abincinta ba.
Hankalinta ya tashi sosai,ta leƙa kitchen ɗin ta ɗakko gishirin tana dubawa,yana nan a yadda ta ajjesa,mamaki ya kamata sosai to ko dai ta zuba ta manta ne?.
Kasa tuna hakan tayi ta fito ta zauna shiru kan rantsatsun kujerun falon,tana cikin wannan halinne Baby ta fito daga ɗakinta,da kayan bacci ajikinta cikin shagwaɓa ta taho ta ɗora kanta akan cinyar Halima.
Baby ta ce"mom good morning"?.
Halima ta shafa kanta sannan ta ce"ɗazu kin shiga kitchen ne?".
Baby ta lumshe idonta sannan ta ce"No mom".
Halima ta faɗawa Baby duk abinda ya faru,Baby ta ce"Mom kuma su Ummita basu tashi ba"?.
Sai lokacin Halima ta tuno dasu.
Sannan ta ce"gaskiya ko da ace sun tashi bana tunanin zasuyi haka gaskiya,sai dai ina ganin ni ce na sanya gishirin na manta."
Baby ta ɗaga kai kawai,sannan ta shiga ɗakinsu Ummita dukkansu yanzu bacci suke,don Khairat tana gama Azkhar ɗin ta samu kanta a wani irin bacci,sai kuwa ta hau barci duk da tana tunanin tashi ta girka wani abin,amman kuma tana tunanin yin hakam tunda matar gidan bata bada dokar a dafa komai ba.
Baby taga suna barci don haka ta fito daga ɗakin.
Duk abinda ake Baby na jinsu,don har kitchen ɗin da Halima ta shiga ta ganta,sai dai da taji motsin tafiya sai ta koma da sauri,yanzu ma da taga Baby ne yasa ta koma da gudu ta fara barcin ƙarya,zuciyarta fes saboda ganin abinda ya faru,tsakanin Baban Baby da Halima.
Ta tashi ta rufe ƙofar sannan ta hau tsallen murna,tuni ta fara hango kanta acikin wannan tafkeken gidan a matsayin matar aure,matar ma kuma matar Baban Baby kyakkyawan soja,ne cikar haiba da ƙwarjini.
-----*****-----
. . . .Sailuba ta kalli Indo tana zaro fici ficin idanuwanta sannan ta ce"Na higa uku na ni Sailuba?me Sunusi yake shirin ɗakkomin daya fi mutuwa"?.
Indo ta ɗan juya tayi dariyarta son ranta sannan ta juyo..ta haɗe fuska tayi kamar za tayi kuka,ta kalli Bintu ta karkatar da baki gefe sannan ta ce"Bintu in faɗa?ni na kasa faɗa Bintu ke ki faɗa mata"?.
Bintu ta zaro ido waje,Indo na son jaza mata masifa don dai tasan ita bata san wani abin kunyar da Sunusi yayi ba?ita dai tasan tunda ya taɓa Indo baza ta barshi haka banza ba,sai ta horar dashi kafin daga bisani a gane manufarta.
Bintu ta kalli Indo da mamakinta sannan ta ce"ni Indo ban. . . ."
Da sauri Indo ta katse ta da ce wa"to na gane Bintu,kema bakyason faɗar wannan maganar,amman ni dole in faɗawa matarsa don kada abu yayi nisa."
Sailuba ta waro idanuwa tana kallon Su Indo.
Indo kuwa ta gyara zamanta sannan ta ce"daman ɗazu ne da muka taho muka ga Sunusi awajen Lami,suna taɗinsu Kuma ba wannan ce rana ta farko da muka ganshi ba,mun daɗe muna ganinsa kullum idan muka dawo daga Dandali,shine muka yanke shawarar zuwa mu gaya miki,don wallahi Lami iccen kabari ake ce mata,indai har ta shigo gidanka to fa sai ta lalata komai,sai ta sakaki kinyi yawo tsirara Allah idan baki tashi tsaye ba,kika bari aka auro miki ita to alƙur'an kin kaɗe har ganyenki".
Da sauri Sailuba ta tashi tsaye tana ƙunduma ashar kamar bamagujiya.
Indo ta miƙe tsaye tana cewa"to mu dai bari mu tafi,kada yazo ya same mu yace mun kawo miki gulma".
Indo ta faɗi hakan tana wa Sailuba gwalo,irin gwalon nan na sokuwa ce ke.
Sailuba ta ce"na gode muku sosai ƴammata,Allah yabar zumunci yau sai ƙauyen nan ya tashi baki ɗaya,don wallahi idan har na bari aka auromin Lami hegiya nake."
Su Indo suka fara shirin fita,sai kuma ta dawo da baya ta ce"am idan yazo ki faɗa masa Indo da Bintu ne suka gaya miki,don kada yace zai musa miki don nasan yanzu bazai yarda ba,gaddama zaiyi miki don yasan baida gaskiya.
Suna fito Indo ta tintsire da dariya sannan ta ce"a'i wallahi Sunusi zai san ni ya taɓo,da zai kama ni ya hau duka kamar ya samu jaka,a'i yanzu kinga haɗa masa abinda zai zo yana da nasanin yimin wannan dukan".
Bintu ta ce"ni dai ban yafe ba Indo,don me zaki dinga sanya ni acikin masifa?ke aka daka ko ni?da zaki dinga sakani cikin masifa?Allah ni dai Indo na kusa raba hanya dake don ni dai wallahi indai har baki canja hali ba,Allah zan yi hannun riga dake duk kuwa da son ƙawancen da muke.
Indo ta ce"to sai me Bintu?ga hanya nan a'i?ke da kanki ke son ƙawance dani don daman ke ce kika laƙemin kamar mayya,amman mi kinsan ko ajikina,tunda idan ma nayo tsokanar inada ƙarfin ƙwatar kai na."
Bintu tayi hanyar gidansu,don dare har ya fara yi don goma ma ta wuce. . . . . .✍🏾
*Ku nuna mana soyayya wajen share,tare da comments wannan ita kaɗai ce hanyar da zamusan kuna ƙaunarmu🙏🏼Allah kabarmu da masoyanmu na asali Amin.*
*Noticed!Noticed🗣️🗣️!!*👇🏻👇🏻
Gawurtattu uku,zasu buɗe aji na musamman da azumi,don koyar da girke girke na musamman na azumi don kun san mu mata ƴan adone,wajen yin girki in akace baki iya girki ba to tabbas mijinki fa kullum yana kan hanyar yawon restuarent,sannan idanuwansa suna kan ƴammata saboda ya samu sarauniyar girki,kada ki bari a barki a baya don gwangwaje me gidanki.
Domin nema ƙarin bayani,sai ku tuntuɓi waɗannan numbobin👇🏻👇🏻
07068606171
08104335144
08179523215
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*🤟GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARA TA 2023🤟*
*_Ina kuke masoyan gawurtattu uku ga su ssun dawo muku da wasu sabbin labaransu a wannan sabuwar shekarar, wannan karon salon gawurtacce ne, ku hanzarto kar ku sake ayi babu ku._*
_Sun shirya tsaf a wannan karon don kawo muku labaran da zakuyi fahari da su, tafiyar mai zafi ce sannan ta musamman._
*_Haziƙai kuma gawurtattu ukun sun shirya ne domin kawo muku gwarazan labaran da zaku yi alfahari da su._*
*MATA IYAYEN GIJI*
_Mrs Bukhari_
*INDA BA ƘASA..!*
_Ummu Maheer_
*KARO ƊAYA...!*
_Ummu Affan_
_LITATTAFAN GABAƊAYA AKAN FARASHI MAI SAUƘI DA RAHUSA 1K_
1 500
2 700
3 1000
_Kai tsaye zaku tura kuɗinku ta wannan account number ɗin._
2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith bank
_Don Allah wannan karon ba ma buƙatar katin waya, idan baka da account to kaje POS ka bada 50 kob 100 a cikin kuɗin a turo ta account number please._
_Ƴan ƙasar Niger kai tsaye zaku turo ta nan._ 0706 860 6171
*DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI A TUNTUƁI ƊAYA DAGA CIKIN LAMBOBIN NAN.*
0810 433 4144
0817 952 3215
0706 860 6171
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARAR 2023 SABON SALO SABON TAKU.*
_TEAM GAWURTATTU UKU 2023_
*MISS GREEN👉🏾👉🏻*
[27/01, 06:52] 🌈Ummu maher(miss Green)💚: *_✨INDA BA ƘASA...!!!_✨*
_(Littafi na 1📃)_
NA
*_®️UMMU MAHER(MISS GREEN)🍀_*
*_AREWA BOOK👉🏻_*
INDA BA ƘASA!!!:: https://arewabooks.com/book?id=63ce1eb0ec00e12124ce9eb0
---------------------------
*_WATTPAD👉🏻_*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
---------------------------
*_🔥GAWURTATTU UKU🤟2023_* ---------------------------
*_TALLAH TALLAH TALLA🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️_*
_A HAYYEH SAMAH MATAH💃💃💃💃💃🏻💃🏻_
*Ku shiga wannan link ɗin don zaɓar kaya masu rahusa👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻*
https://chat.whatsapp.com/G6BmHCxso0rDZyWVQGgYYj
----------
No
07067964894
*_INA KUKE MATAN KWARAI MATAN DA SUKA AMSA SUNAN SU NA MATA A DUNIYA KU GARZAYO KUZO M A C DON ZABEN NA KWARAI KI DAURA ASAN KIN DAURA SAI ATAMFA DA LACE DA SHADDA, MATERIAL WITH SHOE'S AND BAG WITH JEWELRIE DAGA MAMAN ANNUR COLLECTION._*
*_ANAN KWALIYA ZATA MAIDA KUDINTA GAREKI, KIFITO ASAN KIN FITO KIN FASA TARO SAI M.A.C AKAN FARASHI MAI RAHUSA SAYEN NAGARI MAIDA KUDI GIDA IYA KUDIN KI IYA SHAGALINKI🤝_*
*_TANA KANO TANA AIKAWA KO INA DA IKON ALLAH A CIKIN AMINCIN DA YARDAN UBANGIJI_*
*_YAN UWA INA MASU SON SUYI SANA,A BASU DA JARI TOH GA DAMA TA SAMU, INJI MAMAN ANUR DON ZAKU IYA DAUKAN KAYAN MU KU TALLATA KU DORA NAKU RIBAN SAMA ZAMU AIKA MAKU KAYA GA MAISHI DA SUNAN KU A DUK INDA CUSTOMER DIN KU YAKE BA TARE DA MUYI SAVING NO BASHI BA KUMA BA ZAISAN BA DAGA WURIN KI KAYAN YA FITO BA TAKEN MU GASKIYA DA AMANA, MUM ANNUR COLLECTION DA KARAMAR RIBA MUKA DOGARA SABODA NEMAN ALBARKA SAI KUN ZO 👏👏👏👏👏_*
Page🟨9
---------Ummita bata bar Halima ba,ta shiga shirya mata munafunce munafunce,duk don dai ta haɗata faɗa da mijinta,sai dai fa duk abinda tayi sai taga cikin lokaci ƙanƙani an manta komai,sosai abin ya baƙanta ranta har ta shiga wani hali,ta shiga yin zazzaɓi sosai a lokacin kuma MD yayi tafiya,daga Su sai halinsu Suka kai Ummita asibiti,sai dai tashi ɗaya likitan ya gano Ummita na da hawan jini.
Sosai Halima ta tsorata,ƴar wannan yarinyar da hawan jini?Bayan sun dawo gida Halima ta shigo har ɗakinsu Ummita,ta same ta a bakin gadonsu ta zabga uban tagumi.
Sosai tausayin yarinyar ya dirar mata,ta ƙarasa da karsashinta ta ɗaho fuskar Ummita sosai tana kallon nata face ɗin ta ce"Ummita don Allah ki faɗamin abinda ke damunki?bana son wannan abinda kike?tun da kuka zo gidan nan nake kula dake,bakya walwala ba kamar ƴar uwarki ba,ko bakya son nan gidan ne?ko kuwa wani abin ake miki wanda yake baƙanta ranki?".
Ummita taji Halima kamar ta soka mata wani irin mashi,taji tamkar ta shaƙe ta kallon fuskar Haliman da take,amman sai ta goge hawayenta ta ce"ba komai Anty kawai dai gani nake kamar kina cikin damuwa ne,saboda yawan tafiye tafiye da mijinki yake yi,dubi fa wannan zuwan da yayi bai fi sati biyu ba,amman har ya koma ya barki ke kaɗai?gaskiya maza ba suda tausayi".
Ummita ta faɗi hakan tana hararar Halima ta gefe,bata san ma me yasa yanzu take ganin Halimar muguwa ba,don gani take kamar tana yiwa mijinta asiri,saboda yadda ko da ta haɗasu faɗa sai taga kuma sun shirya.
Halima taji son yarinyar ya ƙaru acikin zuciyarta ta ce"Ummita dole zan damu mana,amman tafiyarsa itace mafi alkhairi agare ni dama shi kansa ɗin,saboda matsalar da muke ciki ni dashi".
Ummita ta zaro ido waje ta ce"wata matsala kuma Anty"?.
Don tana son jin matsalar da take haɗa Halima da romio ɗin mijinta MD,don a ganinsu babu abinda zai haɗasu kuma duba da yadda suke ƙaunar junansu,gwanin ban sha'awa don yadda suke soyayyar yana ƙona mata rai sosai,so take taga duk wannan son ya tafi sai kuma ƙiyayya don wani buri nata da take son cikawa.
Halima ta share ƙwallar da ta taru a idonta ta ce"Ummita mahaifiyarsa baza ta taɓa bari mu zauna Lafiya ba,kullum naje da problem ɗin da zata zo min dashi,Musamman idan taga yana gari amman yanzu kinga idan yayi tafiyarsa shikkenan."
Ummita na jinta,ta ɗan matso hawayen munafurci ta ce"Allah sarki Anty,gaskiya cikib matsala babba sai dai Allah ya fitar dake."
Halima ta ce"amin Ummita,yanzu dai tashi muje fali muyi hira tunda dai kin samu lafiya,kuma yau dai naji damuwarki".
Ummita ta ce"to Anty".
Amman fa ba don taso hakan ba,Halima ta wuce gaba itama ta biyo ta a baya,tana jin kamar ta tsire Halimar kowa ya huta.
Hira ake sosai,ammanfa ita hankalinta yaba kan wani ƙaton hoton MD wanda yayi kyau matuƙa gaya.
Khairat ta fuskanci abinda take kallo,ta juya ta kalli Halima da Baby taga hankalinsu baya wajensu,sai kuwa ta taso da sauri ta rufe idon Ummita,ta raɗa mata wani abu acikin kunnenta sannan ta buɗe mata idon.
Ummita ta galla mata harara,sannan ta tashi ta shige ɗakinsu don ita shi kansa gidan ma ta tsaneshi don bata samu abinda take so ba har yanzu.
Khairat na ganin hakan tabi ƴar uwarta ɗaki,tare da rufo ƙofar don kada ma su Halima su biyo su,duk tasan ba lallai suyi hakan ba don Halima bata fiya shiga ɗakinsu ba.
Baby ce daman me yawan shiga,don Baby aƙwaita da son hira sosai.
Ta harɗe hannayenta a ƙirji,tana tsaye bakin ƙofar ɗakin bayan ta rufe,tana hango ƙanwarta tayi ruf da ciki alamar tana tunanin nata da ta saba.
Ta ƙarasa har inda take sannan ta ce"Ummita wai meye ribar wannan halinda kika saka kanki ne?me yasa kike son janyo mana masifa haka?kina tunanin idan kika cigaba da hakan mutanen gidan baza su gano halin da kike ciki ba?ko kuma an gaya miki ba suda ƙwaƙwalwar da zasu gano hakan?gaskiya Ummita wannan ƙazamar rayuwar da kika jefa kanki tayi miki tsauri da yawa,ki sassautawa kanki ki cire mutumin nan aranki,tunda shi bai ma san kina yi ba abinda ya sani kawai shine matarsa da ƴarsa,kuma kinga alkhairan matar nan awajenmu bai kamata muci amanarta ba,mu zamo masu cika alƙawari ba masu Butulci ba". . . . . . . . . . . .
Tun kafin ta ƙarasa Ummita ta daka mata wata irin tsawa,wacce tasa Khairat gimtse maganar ba tare da tayi niyya ba.
Don ita a halin yanzu ma ta fara tsoron Ummita,tamkar dai Ummita ɗince yaya ita kuma ƙanwa,don daman can ba'a nunawa Ummita yiwa yayarta biyayya ba,saboda ita ƴar so ce shiyasa ba'a koya mata hakan ba.
"Khairat na gaya miki ki fita harkata ko?don me ba zanso shi ba?saboda matarsa?to bari kiji indai har kika ga ban auri Baban Baby ba to mutuwa nayi,don Wallahi kinji na rantse ko ta wata hanya sai na aure shi.
Khairat ta ce"Ummita kin san abinda kike faɗa kuwa?kina son ki jefa kanki cikin masifa ko?wannan wani irin so ne haka?don ni dai a tarihi ban taɓa jinsa ba."
Ummita ta juya abinta ta cigaba da aikin tunaninta,ta bar Khairat anan tsaye tana tunanin halin da Ummita ke ciki.
Suna hirar Halima ta neme su ta rasa,Baby ta ce"Momy aƙwai abinda kike nema ne?".ta faɗi hakan tana kallon Halima wacce ke ta kallon gefansu,don dai tasan anan ta bar su Ummita yanzu kuma taga ba ta gansu ba.
-----*****-----
. . . .Suna cikin hirar suka ga Sailuba ta fito daga cikin gidan cikin mugun fushi,daga ita sai ɗaurin ƙirji sai kuma zanin da ta goya ɗan ta,wanda yake barcinsa hankalinsa ƙwance.
Indo ta tintsire da dariya ta ce"haka nake so Sailuba,so nake taje ta tarwatsa wannan nishaɗin,ta haukace masa yadda zai kasa gane komai,ta yadda zan sanya musu rigima me ƙarfi a tsakaninsu,sai yazo ya