Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 33516 words

Chapter 2 - ABIN CIKIN KWAI By Ummu-Maheer Miss Green .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

gidana don ba zan lamunci cin fuskar kowaccenku akan mahaifiyata ba.


Muryarta na rawa zata yi magana da sauri ya ɗaga mata hannu ran tsohon soja ya tashi ya fita yabar mata ɗakin,ya koma wajen mahaifiyarsa ya cigaba da lallaɓa ta,don yana fatan ya gama da ita lafiya.
Kuka sosai ta yi awajen kafin ta tashi ta fita,tana tunanin ta yadda za ta gayawa ƴan uwanta wannan maganar garinsu da sai a yini a kusan ƙwana ana tafiya sannan sai da yamma ta yi sannan za a ce su koma da yamman nan ko kai amarya ba ayi ba sunga gida.


Ɗaki ta koma tasha kukanta sosai,a hankali na buɗe ƙofar ɗakin mahaifiyata halin dana ganta a ciku shine ya ƙara jagula min tuna nina,na ƙarasa kusa da ita hankalina atashe ganin fuskarta ta jiƙe sosai da hawaye cikin daburce wa na ce"Mama lafiya me ya faru da ke?"
Bata iya ce wa komai ba ta tashi ta fita,binta na yi da kallo ina hasashen abinda ya faru tabbas hajiya kaka ce ba wani ba,don tun ina ƙarama na sha kama mama tana kuka kuma ba kowa ne musababin kukanba sai hajiya kaka,sam bata san mama na ban san abinda ta yi mata ta tsaneta haka ba.nima bani da zaɓi daya wuce in fito daga ɗakin don haka na yo waje don ƙawayenmu duk sunci ƙwalliya don kai amarya,ina fitowa Rashida ta ce"lafiya naga fuskar mama duk ta canza?ko ke ce kika yi mata wani abin".


"hmm Rashida ni kuwa me zanyi wa mama da za ta yi fushi dani haka?kawai dai kin san tsakaninta da hajiya kaka ina ganin wannan ne amman ba ni ba ce."


"kin san Allah Khairat matar nab gaba ki ɗaya ta ishemu a gidannan,ni na rasa dalilin daya sa duk iyayenmu suke cikin gidannan kamar dole,ita kuma ba bari take a zauna lafiya ba,kullum sai faɗa ni wallahi matar nan ma na matsu ta margaya mu huta da jarabarta.


Saurin rufe mata baki na yi na ce"wallahi Rashida ki kiyayi wannan bakin na ki kinsan dai matar nan kakarmu ce,babu yadda zamuyi da ita suma iyayenmu haƙuri suke da ita,muma ya kamata muyi haƙurin ko?"


Iman da Salimat da suke juyo hirar da su Khairat suke sai kuwa suka ce"Hmm Rashida wallahi ki cigaba da maganarki kada ki biyewa wannan wacce bata san inda ya ke mata feeling ba,don haka ko muma wallahi mun tsaneta wallahi tunda bata san iyayenmu mu ma dole ne mu tsaneta".


ni dai fitowa na yi babban hall ɗin da ake hidimar bikin abin mamaki duk babu ƴan uwan mama na awajen abin ya ɗaure min kai sosai,yanzu fa na gansu awajen amman har na nemesu ban gansu ba.




Aranar dangin mama na duka suka koma ba tare da sun tsaya sai washe garin ba,hankalina ya tashi sosai na fito na yi sashen hajiya kaka,tana zaune ita da wata ƙawarta Hajiya Inna,na gaisheta tana tsokana ta tana ce wa saura na mu muma,kunya ce ta rufeni sai kuwa na ji Hajiya kaka na ce wa"Hmm Hajiya Inna kema dai kya faɗa wallahi wataran idan na ga yaran nan suna shiga suna fice agidannan su kusan ashirin duk ƴan mata,sai in shiga ɗaki inyi ta kuka sai ta buɗe injirnta ta ce"kinga duk inda na yi ƙashin wuya saboda yarannan duk dun tsotseni wallahi".


duk da ina cikin tashin hankali sai da na yi dariya sannan na ce"Hajiya kaka kina da masaniyar dangin mamana duk sun bar gidannan acikin wannan daren ko kai amaryar basu yi ba sunga gidan brother".


"brozo na ce ungo ƴar nema. to sai me don sun bar gidan ai ni sauƙina ne don wallahi idan na fito naga waɗannan samudawan mutanen har zazzaɓi na ke wallahi don ni bana son ganin ire iren inya murai sam agidannan itama uwar taki darajarku take ci wallahi da tuni ta daɗe da barin gidannan".
Da sauri Hajiya Inna ta kalleta ta ce"haba Ramatu ashe har yanzu baki manta da wannan abin ba?Har sun tara zuri'ah Da Ɗanki yanzu da aurensu ya kai shekara 30 Fa amman ai yakama ta a manta da komai tun sanda malik ya auro yarinyar nan shekararta 13 har yanzu da take kusan shekara 43,amman ace haryanzu ba a manta da komai ba?gaskiya bai kamata ba Ramatu ki sani kema fa ɗiyanki suna gidan miji fa?bakya tsoron ayi musu haka?don Allah Hajiya Ramatu wannan abin ya wuce in banda yarinyar nan tana da haƙuri ne da irin ƴaƴan yanzu ne da babu abinda zaisa ba zasu yi miki rashin kunya ba,don kin zagar mata uwa a gabanta.


Har hawaye ya fara wanke min fuskata na tashi na fita daga ɗakin,wai ita hajiya kaka me take so ne da mamana?wacce irin tsana ce haka".


ji na yi kamar na buge da abu da sauri na juyo saboda buguwar da goshina na ce"wash".


sosai gabana ya faɗi ganin Yaya Bilal,da sauri na take xan gudu ya janyo bayan rigata tas tas ya kifamin maruka har biyu,na dafe ƙuncina hawaye na ƙara fitowa a idanuwa na ya ce"stupid girl kawai ke bakya kallon gabanku ne da zaki bugeni?to wannan shine last warning matuƙar na biyo hanya to ki kada ki biyo don na tsani kallon wannan dirty face ɗin ta ki,don haka ki kiyaye."


maimakon ya bani haushi sai ma ya ƙara burgeni sosai,abin tausayi wato shi so hana ganin laifi.


Ƙamshin tureransa ya ƙi barin wajen sai da na ɓata minti kusan talatin sannan na tashi na tafi,wajen daya mareni ɗin na shafa hannayensa duk sun fito a kumatuna,ina ta shafa wajen maimakon inji haushi a'ah daɗin marin ma naji don ko babu komai ko madubi na k
Da sauri Hajiya Inna ta kalleta ta ce"haba Ramatu ashe har yanzu baki manta da wannan abin ba?Har sun tara zuri'ah Da Ɗanki yanzu da aurensu ya kai shekara 30 Fa amman ai yakama ta a manta da komai tun sanda malik ya auro yarinyar nan shekararta 13 har yanzu da take kusan shekara 43,amman ace haryanzu ba a manta da komai ba?gaskiya bai kamata ba Ramatu ki sani kema fa ɗiyanki suna gidan miji fa?bakya tsoron ayi musu haka?don Allah Hajiya Ramatu wannan abin ya wuce in banda yarinyar nan tana da haƙuri ne da irin ƴaƴan yanzu ne da babu abinda zaisa ba zasu yi miki rashin kunya ba,don kin zagar mata uwa a gabanta.


Har hawaye ya fara wanke min fuskata na tashi na fita daga ɗakin,wai ita hajiya kaka me take so ne da mamana?wacce irin tsana ce haka".


ji na yi kamar na buge da abu da sauri na juyo saboda buguwar da goshina na ce"wash".


sosai gabana ya faɗi ganin Yaya Bilal,da sauri na take xan gudu ya janyo bayan rigata tas tas ya kifamin maruka har biyu,na dafe ƙuncina hawaye na ƙara fitowa a idanuwa na ya ce"stupid girl kawai ke bakya kallon gabanku ne da zaki bugeni?to wannan shine last warning matuƙar na biyo hanya to ki kada ki biyo don na tsani kallon wannan dirty face ɗin ta ki,don haka ki kiyaye."


maimakon ya bani haushi sai ma ya ƙara burgeni sosai,abin tausayi wato shi so hana ganin laifi.


Ƙamshin tureransa ya ƙi barin wajen sai da na ɓata minti kusan talatin sannan na tashi na tafi,wajen daya mareni ɗin na shafa hannayensa duk sun fito a kumatuna,ina ta shafa wajen maimakon inji haushi a'ah daɗin marin ma naji don ko babu komai ko madubi na duba zan ga tafin hannayensa a kumatuna.


Ban samu kai amarya ba don har sun tafi,sashen Anty ƙarama na je matar baba usman ƙaramin ƙaninsu babanmu.


Turaren wuta ta kunna a burner mai shegen ƙamshi ta kalleni da fara'arta ta ce"ah wata sabon ganin yaushe rabonda na ganki a sashennan har na manta?"


Ɗan murmushi na yi na ce,"to maman arman gani na zo".da mamaki ta kalli kuncina ta ce"ikon Allah ke kuma Khairat wani mugunne ya mareki haka?".






ɗan shafa wajen na yi na ce"am daman faɗuwa na yi ɗazu".
"ƙarya ki ke wallahi Khairat ba faɗuwa ki ka yi ba ki faɗi gaskiya dai?wannsn marine ga yatsu biyu biyar nan sun fito raɗa-raɗa.


Hawaye ne ya fara fitomin na saka tafin hannuna na rufe don kada ta gani,janyo ni ta yi ta rungume ni sannan ta ce"ki faɗa min gaskiya Khairat nasanki da haƙuri da kawaici waye ya mareki haka?".


ban sanda na ce mata ba"maman arman yaya Bilak ne ya mareni waidon na biyo hanyar da ya ke".sai na fashe da kuka don ban san abinda yasa Yaya Bilal ya tsaneni ba".?


"caɓɓi jan lallai yaron nan ba shida mutunci yanzu shi ne ya yi miki wannsn marin na cin kashi da wulaƙanci.? Da sauri na riƙe hannayenta na ce"don Allah maman Ammar kada ki faɗawa kowa wannan maganar wallahi ina sonshi bana son tun yanzu ya ce ina haɗasa faɗa da ƴan uwa.






*Miss green ce*
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇*




1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_


2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_


3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_


4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_


5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨
_Miss Hajo_




Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300


*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇


0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.


Domin tura shaidar biya👇


0810 433 5144


Masu tura katin MTN👇


0814 179 9224


Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇


0817 952 3215


Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f


*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨




*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*


Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -


*Enter your name:* (Cikakken sunanki)


*Enter your mail:* (Email ɗinki)


*Enter an username* (Sunanki)


*Enter your password:* ( misali 12341234)


*Confirm password:* (misali 12341234)


Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.


*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.


*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.




*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*


https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3




Masu iPhone


Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
[01/09, 08:07] my no: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_


📃Littafi na 1








By🪶
*Ummu maher(Miss green)🍏*




*GAWURTATTU 5*
-----------------------
*Wattpad user name*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333
-------------------------


*Arewa book user name*
https://arewabooks.com/u/rabiattu0444
----------------------
*Sirrinmu*


manzon Allah(S.A.W)ya hanemu da yiwa ƴaƴanmu zane kamar,kalangu,tattu da sauransu.domin canza halittar ubangiji.




5🟦6




. . .ture hannuwa na ta yi sannan ta ce"amman gaskiya khairat baki da hankali wallahi saboda me shi bai sonki ke zaki ringa tusa kanki,Allah ya yi miki halitta mai ƙyau duk da ke ba fara bace kamar sauran ƴan gidannan amman kaf ɗinsu kin fisu komai ilimi,haƙuri,ƙanƙan da kai,biyayya,tarbiyya,wallahi duk kin fisu wannan abubuwan dana lissafa,to me zaisa ki zaɓi wanda baya sonku?idan fa ki ka auresa ba zai taɓa baki haƙƙinki ba,kuma harga Allah bashi da laifi tunda ba shine ya ce yana sonki ba,dole aka yi masa kinsan dai Hajiya kaka tana ji yanzu ko yana so ko baya sonki saiya aureki don yadda take matuƙar sonki aduk cikin jikokinta,don Allah Khairat ki cire Bilal a zuciyarki don ba alkhairi ba ne kinji?na fi son ki auri wanda zai kula da ke sosai ba wanda zai zakunce ki ba".


kuka sosai na ke yi sannan na ɗago idanuwana da suka jiƙe jagab da hawaye na ce"ummu arman don Allah ki bani goyon auren Yaya na Bilal wallahi duk yadda ki ke tunanin irin son da na ke masa to duk ya wuce hakan,ina jinsa ne har cikin ƙoƙon xuciyata duk sanda zanyi numfashi to tabbas sai na tuna da Yaya Bilal,don Allah ki bani goyon baya duk gidannan babu wanda zan tunkara da wannan maganar idan ba ke ba,don Allah ki fuskanci yadda na ke ji don Allah".tana faɗar hakan ta ruƙo hannun Ummu Arman ta ɗora sai tin zuciyarta ta ce"Ummu Arman aduk sanda ki ka ji zuciyata tana irin wannan bugawar to tabbas Yaya Bilal na ke tunawa,na so in cire wannan mayen son da na ke masa amman abu ya ci tura,saboda da sonsa aka haifeni kuma har na girma dashi cire wannan son a zuciyata tamkar cire numfashi na ne".sai na rungume Ummu Arman na fashe da kuka mai tsananij gaske.


rungume ni ta yi tana dukan baya na a hankali itama hawayen yana fitowa sosai acikin idanuwanta,tabbas tana matuƙar son Khairat don tun tana ƙaramarta ta ke sonta kuma tun tana ƙaramar Allah ya jarabce ta da son Yayan na ta,tana tausayawa yarinyar sosai yadda ya kamata saboda Khairat yarinya ce mai haƙuri,tabbas da za ta iya da tuni ta sakawa Bilal son Khairat don da ya ke mutuminta ne bayan wajen Kaka akaf gidannan babu ɓangaren da ya ke shiga ya yi hira idan ba sashenta ba,tasha yi masa nasiha akan yaso mai sonshi kanar khairat amman abu shiru kamar ma turasa ta ke yi wani lokacin,idan ta yi masa maganar Khairat ba zai sa ke shigowa sashenta ba,har sai ta je ɓangarensa ta basa haƙuri sannan komai zaiyi dai dai.
Jikina babu ƙwari na koma ɓangarenmu don ƙwana biyu bana zuwa sashen Hajiya Kaka tunda munyi faɗa,ina shiga Hajiya Iklima da Anty Zeenat suka kalleni sheƙeƙe sannan Hajiya Iklima ta ce"ke zo nan tunda baki iya ganin mutane ki gaishesu ba".


ina zuwa ta ɗaukeni tas da maruka har biyu sannan ta ce"na yi maganin mara kunya wuce ki bani waje da wata uwar baƙar fuskarki wacce uwarki inyamura tuban muzuru ta shafa miki".


Sosai abin ya yi min zafi zuciyata tana ƙuna bansan sanda wani kuka mai ƙarfin gaske ya zomin ba,daman abokin kuka na ke nema don daman a cikin matsala na ke yanzu gashi kuma an to noni.




Mama da ke ɗakin Abba tana gyara masa shimfiɗa ta jiyo ihuna ta fito da saurin gaske har tana tumtuɓe ta ce"ke Khairat lafiya me ya faru?".


ban iya ba ta amsa ba da sauri na rungumeta ina shesshaƙa kamar zan haɗiye zuciya,ta gane me ya faru don haka bata ce komai ba taja hannuwa na muka koma ɗakinta.


"Da mana ayi magana in zageki tsaf kema don daman akanki na ke son hucewa,da anyi magana sai miji ya ce Zulaiha! zulaiha!wai ita ga ta matar so,ko uban waye ba matar so ba oho".


Anty Zeenatu ita ce ta tsakiyar da ya ke matan babana uku mama na ce Amarya sai kuwa ta ce"Hmm Iklima ai mu da sauƙi tunda asalinmu musulmaine munsha ruwan musulunci ita kuwa fa,tuban muzuru ne fa".


ashe wannan ihun da na yi Hajiya Kaka ta ji alokacin Ƙasim ɗan Baba Auwalu zai kaita unguwa sai kuwa ta ce"kai Ƙasimu ni kukan wa na ke ji ne?".


"gaskiya Kaka ki daina ce min Ƙasimu haka kawai da suna na Aqasim mai daɗi sai kuma a ɓata min,gaskiya a kiyaye?".




"don ubanka ko Auwalu bai isa ya bani doka da order ba,don ba shine ya haifeni ba ni ce na haifesa,don haka ka ki yaye wallahi,ko inci uwarka mai ƙosan siyarwa,ni dai Ƴaƴana sun ɗebowa ruwan dafa kansu daga taimako sai kaga sun auresu ni kuma azo ana gasa ni,akan me ban hana aurensu ba sai kuma ni ace za a takuramin,to wallahi ni babu ruwana gaskiya tana zuwa zan faɗa sai dai mutane suji haushi".




tuni har Ƙasim ya shige mota yana hango Kaka tana ta surutanta don shi bai ma san abinda ta ke ce wa,ya kalli jakar da tasa ka shi riƙewa wai ita daman cen idan zasu fita da mijinta kakansu shine ya ke riƙe mata jaka,duk da kasancewarsa soja baya jin kunya haka ya ke riƙewa,Ƙasim ya yi tsaki yana wani hararar Kaka.


Har ta fara tafiya sai kuma ta ƙara jiyo sautin ihun da ya ke sashenmu ne akusa dana Kaka,don haka duk wasu abubuwan ana iya jiyo su.


Da sauri ta yi sashenmu tana ce wa"wani mai son aci mar mutunci ne ya saka jikata kuka?".tana faɗar hakan tana shigowa farlon da ƙer don ya yi ɗan tsayi tudun farlonmu.


Dukansu shiga taitayinsu sukayi suka haɗe fuska suna gaishe da Kaka amman ko kallonsu ba ta yi ba ta ce"waye ya saka Khairat kuka a cikinku?".sunkui da kai suka fara yi suna ƴan muzurai tare da sosai ƙeya don duk abinsu suna matuƙar jin tsoron Hajiya Kaka don aƙwaita da tonon asiri.


"Ba daku na ke bane ku ke wani sunkui da kai kamar baƙin ɓarayi"?.da ƙer Anty Xeenatu ta ce"da man Hajiya Kaka Khairat ce ta yi wa Hajiya Iklima rashin kunya to shine". . .


"shine me?".


Babu wanda ya ce kanzil duk kawunansu a ƙasa,dai kuwa Kaka ta ƙwala ƙara tana ce wa"Zulai ke Xulai wai kina ina ne kizo ana son kashe miki ƴa".


da sauri muka fito daga ni har Mama fuskata ta kumbura sosai ga marin Yaya Bilal ga kuma na Hajiya Iklima sai abin ya yi min yawa kumatun na wa suka kumbura sosai abin tausayi.



"La ha ila ha illallahu muhammadur rasulullahi sallallahu alaihi wasallam,Khairat me na ke gani a kuncinki kamar mari rututu haka?,ɓoye fuskar na yi ina muzurai don nasan tunda Kaka ta zo to tabbas ko wa sai ya taru agidan,don Kaka aƙwai son jikoki tun ma ba ni ba.
Dukkansu tashi sukayi tsaye suna bawa Kaka haƙuri don sun san ko da basu ma tashi ba to yanzu zasu tashin don sai ta tara musu mutane.


Ko kallonsu ba ta yi ba,tana ta faman girgixa ƙafafu alamar yau aƙwai masifa a gidan.


Ko da Ƙasim ya gaji da jiran Hajiya Kaka sai ga shi ya biyota sashenmu ya tarar ana dirama,gurin zama kawai ya nema ya zauna don yasan wannan tsayuwar da kakar ta sa ta yi sai akai dare ana abu ɗaya,don kaka bata san ta yi abu ɗaya ta yi shiru ba.


Tun ana abun tsakanin ɓangarenmu har ƴan sauran ɓangaren sashen suka fara tururuwar shugowa har ana ƴan rige rige.


Umma ce kawai bata shigoba mahaifiyar Bilal don dawowarta daga makaranta kenan,don ita ce headmaster a makarantar ƴan matan da take.
Kowa ya baza idanu ya ji abinda zai faru,masu dariya na yi masu jin haushi suma ba a barsu a baya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads