Showing 12001 words to 15000 words out of 33516 words
Chapter 5 - ABIN CIKIN KWAI By Ummu-Maheer Miss Green .txt
1k
*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*
Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.
Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
...........🥚👩❤️👨💥🌎....
*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*
*miss green ce*
[01/09, 13:29] my no: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_
📃Littafi na 1
By🪶
*Ummu maher(Miss green)🍏*
*GAWURTATTU 5*
---------------------
masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi.
*SIRRINMU*
Mu kasance masu tsarkakkiyar zuciya,kada mu dinga hassada ko baƘin ciki.
9🟨10
. .. ."Rashida gaskiya irin wannan zaman da mukeyi a tsakaninmu dasu Nadiya bai kamata ba,ko da ace ma bamu san juna ba ai ya kamata ko gaisuwa ta dinga haɗamu?".
"Hmm Khairat kenan ni ina mamakin hali irin na ki wallahi waɗannan mutanen fa babu abinda suka sani illa su zageki su baƙanta miki,to me ye amfanin zuwa wajensu?ranki ne kawai zai ta ɓaci a banza wallahi,amman ni bazan hanaki zuwa wajen ƴan uwanki ba,amman ni dai ba zanje ba idan kinga ke zakije ga ki gasu amman ni dai La-La-La ina da abinyi ne ni dai."tana faɗar hakan ta yi shigewarta banɗakin da ke jikin ɗakin ƙwananmu.wata ƙawarmu mai suna Hasiya tana zaune tana karatun wani novels ta juyo tana kallona ta ce"gaskiya ne abinda Rashida ta faɗa miki duk da ni ba ƴar'uwarku ba ce amman zan faɗa miki gaskiya ku fita daga harkarsu nadiya dasu iman saboda wallahi yanzu kaf ma skull ɗinnan babu wanda bai san grp ɗinsu ba,yanzu haka suna da grp mai zaman kansa a makarantar nan na ƴan lesbian so be careful da waɗannan duk da su Nadiya babanku ɗaya amman idan zan baki shawara idan har kun koma gida ki sanarwa da mahaifinku duk abinda ya ke faruwa idan da hali ma ayi musu aure kawai shine zai kawo ƙarshen komai".ta faɗi hakan tana kallona.
Tabbas wannan abinda Hasiya ta faɗa min ya girgiza tunani na sosai,an daɗe ana faɗamin abinda su Nadiya suke a skull sam basa karatu yanzu,daman tunda muka shiga makaranta suka haɗu da ƙawaye suka hure musu kunne shikkenan suka ƙara tsanata da hantara ta tunda ni dai a kullum gaskiya na ke gaya musu.
Jikina a sanyaye na tashi na cire kayana na faɗa banɗaki bayan Rashida ta fito,ko a wajen wankan ma tunani kawai na ke na yadda zan ɓullowa lamarinsu Nadiya don idan wani yaji wannan maganar a gidanmu to tabbas zasu shiga tsaka mai wuya don hatta kashi ma sai ya fisu mahimmanci a gidanmu.
Bacci ma da ƙer ya ɗaukeni saboda tunani,ni mutunce mai saka abu arai musamman wannan abin daya kasa gogewa a zuciya ta,a duk tsahon rayuwata ban taɓa saka wani abu araina irin Yaya Bilal ba sai kuma wannan maganar tasu Nadiya.
Da sassafe muka tashi muna shirin tafiya assembly don yau litinan(monday)uniform ɗinmu kalar baƙi da fari wato black&white riga da hijab duk fari wando baƙi kamar kalar kayan likitoci,munyi ƙyau sosai acikin kayan na mu muka jero mu uku ni da Rashida da Hasiya don daman mu uku ne acikin ɗakin.
Ta ƙofar hostel ɗinsu Nadiya muka biyo abin mamaki su haryanzu basu fito assembly ɗin ba,na kalli Rashida cikin dakiya da nuna kulawa na ce"Rashida don Allah mu shiga wajensu Nadiya mana mu duba su".?kallon tsaf ta yi min sannan ta ce"Hmm gaskiya Khairat kina da matsala wallahi yanzu ko jiya ma fa sai da mukayi maganar nan,bana son ki jefa kanki acikin matsala garin gyara kuma ku ɓallowa kanki matsala,don kin san grp ɗinsu ɗaya da big girl kuma kin san daman tana harinki a skull ɗinnan don ki zama lalatacciya irinsu,to kinga idan kina zuwa wajensu komai zai iya faruwa da ke".ta faɗi hakan tana kallona sosai fuskarta alamun jin tausayina.
Hasiya ta da fa kafaɗa ta ta ce"Khairat bama son abinda zai taɓa rayuwarki ki yi haƙuri don Allah ki taho mu tafi,ki dinga taya su kawai da addu'ah kuma ki yi amfani da shawarar dana baki jiya,ko da kun koma gida kada ki manta wannan shawarar dana baki".
gyaɗa kaina na yi kawai na bisu don hankalina nima bai ƙwanta da zuwan na wa ba,abin mamaki sai da aka kusa gama assembly sannan suka shigo suna wani bubbuɗawa duk idanuwansu sun kumbura alamar basuyi bacci ba,Rashida ta ce"Allah dai ya shirya wallahi sun ƙwana suna lalacewarsu ai dole ido ya kumbura,iyayenmu na cen suna tattalin rayuwarmu da bamu tarbiyya amman su ƴan rashin kamun kai suna nan suna lalacewa."
nima ganinsu da na yi sai da gabana ya faɗi saboda ganinsu a cikin wannan halin don ko da ba'a gaya maka ba kasan abinda ya faru,na ji wata ƙwalla mai zafin gaske ta zubomin na saka hannaye na na sharesu Rashida tana kallona ta ce"iska tana wahalar da mai kayan kara".
rai na duk babu daɗi har aka gama assemly ɗin muka shiga aji,muna fitowa muka koma hostel ɗinmu muka fara girki ƴar ƙaramar wayar Rashida ta fara ƙara ta ɗaga tana ce wa waye?".shiru akayi kafin daga bisani taji ance "abdullahi ne don jakar ubanki".tsalle Rashida ta yi ta ce"Hajiya kaka daman kina duniya"?.da sauri na amshe wayar harda ƴar ƙwallah ta ka fin inyi magana ta ce a bawa ABIN CIKIN ƘWAI,in dai kaji kaka ta faɗi wannan sunan to tabbas dani take.
Rashida ta ce"to ai tun kafin ma in ba ta ta amshe ita me kaka".ina jin kaka tana ce wa"to ke kuma da ba kakar ki ba ce sai ki siyo a kasuwa".riƙe kai Rashida ta yi Hasiya tana ta ɓaɓɓaka dariya don ita dai Allah ya saka mata son tsohuwar aranta.
"Hmm Abin cikin ƙwai ni dai ina ganin baƙin ciki a gidannan wallahi?idan suka isheni wallahi tattara kayana zanyi in koma uman wajen ƴan uwan mahaifina ko kuma in tafi Bauchi".tana faɗar hakan ta tintsire da kuka.
Haba ai Rashida dariya harda tsalle tana ce wa"Hajiya kaka yasin kin kusa margayawa ki yadda kawai,amman in banda tsufa ba'ayiwa mutum komai ba sai ya tattara kayansa yabar gida".?
kaka na juyo ta ta ce"shegiya jinin fulani muguwa kawau to babu inda zanje sai inga ta dariya,daman uwarki ce ta ɓata min ran wai akan Sadiq ɗan wajen auwalu ya ce yana son nusaiba shikkenan tsohuwar ƴar bokon nan uwarku ruƙayya ta kafa ta tsare wai ita bata son auren dangi,yanzu don Allah idan banda baƙin hali ita da ubanku ba auren dangi bane?".
Haƙuri na fara bawa Hajiya kaka ta ce"ai wallahi da ce wa na yi tafiya ta zanyi tunda ita dai bata san kara ba".Rashida da ke jinmu tana kallona alamun dai bata ji daɗin zagin da kaka take wa mahaifiyarta ba.
Nima da ba uwata aka zaga ba tabbas banji daɗi ba,in banda abin kaka ai nusaibar nan dai ƴar ta ce ko?amman kuma ta ce bata so saboda nusaiba yarinya ce har ayanzu bata rufa sha 15 ba a s.s.1 take mu kuma muna da 17 aduniya yanzu kuma muna s.s.3 muna shekararmu ta ƙarshe. Nan dai Hajiya kaka ta gama faɗanta daga baya ta kashe wayar,muna gama wayar na kalli Rashida na ce"kai kaka aƙwaita da fi'ili wallahi kamar dole sai ta haɗamu auren dangi haka fa kema da yaya mohd ta da ge sai ya aure ki,don Allah yanzu me ye amfanin auren."?
"Khairat kenan ita fa wannan tsohuwar haka take ni wallahi har Allah Allah na dingayi mu taho saboda yadda tsohuwar nan ta sakani a gaba wai sau na auri yaya mohd,kuma ni wallahi na fi son har inyi jami'a kafin inyi aure."
da fa kafaɗarta na yi sannan na ce"ki yi haƙuri don Allah Rashida akan wannan maganar ki cigaba da addu'a kinga dai yadda kaka ta dage yaya Mohd zaki aura shima kuma ya dage ke ya ke so,to kinga addu'a ita ce mafita don kinga duk su Baba da abinda kaka ta faɗa musu suke amfani don haka kawai sai dai ki yi haƙuri."
"Khairat ni fa wallahi bana sonshi wallahi,ke kin sani idan yaya Mohd yana da ƙyau yana da kuɗi amman ni wallahi matsalar mahaifiyarsa ita ce kawai za ta takuramin ko da bayan anyi auran ne?.
"Tabbas matar Baba tijjani tana da babbar matsala sosai don ko yaya sulaiman babban ɗanta daya auri ƴar gidan Baba Bashir haka ta takura mata zagin yau na gobe daban,don ma kaka tana ta ka mata burki da abin sai ya ɓaci sosai."
"to kin gani khairat to a haka zan auri Yaya Mohd daman kuma duk ƴaƴanta ta fi sonshi sai kawai ace shi zan aura in auri masifa,Allah ni fa bazan aureshi ba gaskiyar magana".tana faɗar hakan ta tashi ta bar wajen.
Na bita da kallo ita sonta ma ake ina ga kuma ni da ba son na wa ake ba shisshigina kawai na ke,yadda yaya Bilal ya tsane ni kamar mutuwarsa,ni kuma na nace sai shi,tabbas idan ban auri yaya Bilal ba to wallahi ni nasan ko da wani ya aure ni to gangar jikina ya aura don bazan taɓa sonsa ba zuciyata da komai na wa yana ga yaya Bilal,ina ma zai soni ko da bai kai yadda na ke sonshi ba,da ranar har azumi sai na yi saboda jin daɗin hakan.
Mun fara exam ɗin second time wacce zamu tafi hutu sannan mu dawo zana jarrabawar waec da neco,muna ta karatu sosai ba mu da lokacin kanmu sam sai na karatu muna dawowa daga class zamu yi bitar haddarmu ayanzu muna izu hamsin da biyar baƙara ce kawai bamuyi ba itama kuma mun iyata.
Rannan malamarmu bata da lafiya mai koya mana karatun qur'ani da asuba aka turo wai inzo zan ƙarawa wasu hadda,abin mamakin ko da nazo su sai naga ƴan ajin su Nadiya ne gabana yana ta faɗuwa na zauna har na ɗakko qur'anin sai na ji Nadiya na ce wa"Hmm wai arasa wacce za ta ƙara mana karatun sai wannan tuban muzurun har yanzu fa wasu daga dangin uwarta basu musulunta ba,adanginsu uwarta ce kawai ta fara musulunta sai manyan arna kakanninta suma suka musulunta kakanta fa babban fasto ne sai ace kuma wai ita ce za ta koya mana karatu?".
wasu zafafan hawaye ne suka fara zubomin ba tare da na yi tunanin tare su ba saboda hawayen daman na ke son yi ɗin,dariya sosai suke min big girl oganniyar cikinsu ta ce"au shine kullum ake wani yawo da ƙaton hijab na munafunci?to yau sai mun buɗe hijab ɗin munga abinda ake ɓoye mana?.
ban san ta zo kaina ta tsaya ba,ɗaga kan da zanyi naga big girl akaina tana neman ciremin hijabij jikina,da sauri na tashi na matsa lungu idona ya yi jawur ta ƙara matsowa tana ce wa,ai yau Khairat baki da wajen guduwa a hostel ɗinnan muradina na shekaru kusan biyar yau saina cika sa akanki."
tana faɗar hakan ta riƙe hannun da na riƙe hijabin ta yi wa su Nadiya fito da sauri suka taho suka rirriƙeni ni kuwa sai kuka na ke ina ihu,wani wawan mari big girl ta yimin sannan ta ce"duk ihunki da wani fizge fizgenki yau wallahi sai na wulaƙanta ki a skull ɗinnan don daman haushinki na keji sosai na karɓemin saurayin da ki ka yi sir Kamil don haka yau sai na rabaki da abinda ki ke tutiya dashi.
Sosai na ke kuka ina roƙonta da ta yi haƙuri amman sai naga kamar zugata na ke ita dasu Iman duk sun yayyaga min hijabina ya yi kaca kaca dashi bakina duk ya fashe saboda tsabar shan bugun da ya yi,amman har yanzu ban daina kukan ba,sunyi nasarar cire min hijabina na riƙe rigata sukayi sukayi duk yawansu su cire amman suka kasa wani ƙaton abu Nadiya ta ɗakko tana ce wa"tunda kin ƙi ta daɗi bari muyi miki mai gaba ki ɗaya.
Saukar abu na ji akaina,nan da nan na fara ganin wani iri duk sun komamin bibbiyu,ana cikin haka wata secutyn skull ɗin tazo wucewa ta hango duk abinda ke faruwa da dauri ta kaɗa ƙararrawa sai ga duk securityn sun bayyana suka biyota cikin ajin don ganin abinda ke faruwa.
Da sauri suka sakeni suna wani wiƙi wiƙi da idanuwa alamun rashin gaskiya,ai kuwa suka cafkesu alokacin ni tuni na yi suman wahala don ban san inda kaina ya ke ba,duk sun yayyaga min rigata,da sauri ɗaya daga cikinsu ta cire hijabin da ta saka ta rufemin sutura ta,don samana duk a buɗe ya ke har hawaye sai da matar ta yi don ba ƙaramin ba ta tausayi na yi ba.
Daman sun daɗe suna jin labarin yaran da kuma ta'asar da sukeyi na lalata ƴaƴan mutane amman aka ƙi ɗauƙar mataki akansu ana tunanin sharri ake musu.
A ruɗe Rashida da Hasiya suka fito daga Hostel ɗinmu,daman duk sun damu da rashin dawowa ta da wuri don har sunyi mana abincin karyawa amman ban dawo ba.
Alokacin an fito dani kamar matacciya zuwa ƙaramin asibitin da ke cikin skull ɗin na mu,su kuma su Nadiya aka wuce dasu ɗakin hukumar makaranta.ɗalibai kowa ya yi cirko cirko masu saurin kuka sai yi suke.
Rashida kuwa har bakin ƙofar da aka shiga dani ta shiga tana ta kuka tana ce wa"shikkenan sun kashe khairat wallahi nima bazan taɓa barinku ba nima sai na kashe ku".haka take ta maganar kamar ta ɓaɓɓaɓiya.
Hukumar makaranta suka kirawo Abbanmu a waya daman duk shine ya sakamu a skull ɗin don haka hankalinsa a tashe yaje ya tashi yayansa ya ke faɗa masa anyi masa kiran gaggawa daga makarantarsu Khairat.
Shima hankalinsa atashe suka fito a hanya suka haɗu da Baba tijjani da Baba Auwalu suka shaida musu abinda ya ke faruwa,suma ka sa tafiya aikin sukayi suka ce zasu bisu makarantar don suma hankalinsu duk a tashe ya ke.
Bilal ya fito daga shi sai wandon aikinsa na sojoji da ƴar fal maram itama ta sojojin ce,sunyi masa ƙyau kayan kamar don shi aka yi su,saukarsa kenan awajen iyayen na sa duk yaji abinda ke faruwa don haka kai tsaye ya bisu ko ajje kayansa baiyi ba.
Anyi min allurar bacci wani baccin wahala ya ɗaukeni,duk inda naji ciwo kuma an daka plasta an mannesa.
Ko da su Nadiya sukayi ido huɗu da yaya Bilal au fitsari sai da sukayi ga shi belt ɗin jibga na jikinsa,ai kuwa ko da yaji abinda ya faru jijiyoyin kansa har wani tashi suke idanuwansa sunyi jawur kamar gauta.
Baba Tijjani kuka kawai ya fashe dashi jin ƴaƴansa har guda uku acikin wannan mummanar rayuwar,Baba na ma da ya ke mai dauriyar zuciya ne baiyi kukan ba amman fa hankalinsa ya yi matuƙar tashi ƴaƴansa har guda biyu a cikin wannan ƙazantacciyar rayuwar.
*Miss green ce*
*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*
1, *MU GANI A ƘASA..🔥*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5_ *AUREN WATA TARA👩❤️👨*
_Miss Hajo_
Guda ɗaya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huɗu N700
Guda biyar 1k
*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*
Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.
Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
...........🥚👩❤️👨💥🌎....
*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*
[01/09, 13:38] my no: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_
📃Littafi na 1
By🪶
*Ummu maher(Miss green)🍏*
*GAWURTATTU 5*
-----------------------
*Wattpad user name*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333
-------------------------
*Arewa book user name*
https://arewabooks.com/u/rabiattu0444
----------------------
masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi.
*Sirrinmu*
Manzon Allah(S.A.W)ya hanemu da cin naman mutane,ma'ana gulma ka yi gulmar mutamin da baya wajen Allah ya tsaremu amin.
-----------------------
13🟦14
........sosai sukayi mamakin kalamin kakar ta su,wai su za'a mayar ƴan aiki ko kuwa?bata ƙara kallonsu ba ta yi wucewarta,don ta yi alƙawarin sai ta koya musu hankali har kuka sai da ta yi don jin abinda jikokinta suke ai'katawa.
Washe gari a babban farlon gidan aka haɗu na cin abinci ƙaton teburine wanda ake haɗuwa duka family aci abinci don ƙara zumunci,kowa ya yi tsit baka jin ƙarar komai sai ƙarar cokali,wasu suna ci amman kamar suna cin kashi don hankalinsu a tashe ya ke da wannan haɗuwar wasun kuwa ba wasu bane illa su Nadiya,iman,samira,unaisa,khalisat,intisar,raudar,amina.
Duk hankulansu a matuƙar tashe ya ke don sun san har wanda bai san abinda sukayi ba to yau sai ya sani don wannan kakar tasu sai ta faɗa.
"To kunyi zungui zungui kuna kallona kamar baku sanni ba?to daman mun haɗune anan don wani gangarumin taro,don haka kowa ya buɗe kunnuwansa yaji."
Kowa kallon kaka ya ke saboda sun san aƙwai wata a ƙasa aƙwai wanda ya ke da rabon shan wulaƙanci shiyasa kowa ya kama bakinsa daga su har iyayensu,itama kakar kallonsu take azuciyarta ta ce yau kowa sai ya gane kurensa don wallahi baza'a janyo musu ɓarna har acikin gidansu ba.
Su kuwa ƴaƴanta babu wanda baisan abinda kaka za ta faɗa ba,don jiya da daddare sunyi meeting akan hakan,Hajiya kaka ta kalli Baba Abdullahi ba tare da ta ce komai ba,sanin abinda take nufi ne ya yi gyaran murya ya fara jawabi kamar haka.
"Abisa yarjejeniyar da muka yanke tsakaninmu da mahaifiyarmu mun ɗaukar mata alƙawari kuma ayau zamu cika mata shi,ba neman shawarar kowa muke acikinku ba a'ah saboda haƙƙin kune a faɗa muku,mun yanke shawarar haɗa aure ga ƴaƴanmu don ƙara ƙulla zumunci."
gaban jikokin na su ne ya yanke ya faɗi karma ace maka su Nadiya sukayi tsiru suna kallon iyayen na su don jin waɗanda aka haɗa auren,ko har dasu oho?kai har dasu ɗinma tunda dai sune ƴan matan gidan,tuni cikinsu ya bada sauti ƙuuu alamun gudawa.
Baba Abdullahi ya cigaba da ce wa"to mun yanke shawarar gaɗa,Aliyu aure da Nadiya".zaro idanuwansu sukayi waje daga Aliyun har Nadiyar.
"Salimat kuma da Abbas,Amina da munir,khalisat da Sadiƙ,intisar da Hafiz,iman da Irfan,unaisa da maher,samira kuma da Arman."
dukkansu tashi sukayi tsaye suna kallon ikon Allah don basu taɓa tunanin wannan abin ba unexpected.babu wanda ya basu damar ce wa komai Baba malik mahaifinsu Khairat ya