Showing 6001 words to 9000 words out of 33516 words
Chapter 3 - ABIN CIKIN KWAI By Ummu-Maheer Miss Green .txt
ba.
"Wallahi yau bazan yarda ba,bari Malik ɗin yaxo idanma shine ya ɗaure muku gindin dukan jikata yau zanji,wannan wani irin rashin imanine kamar an samu ƙato,duk cikinku wa ubanta ya taɓa duka?ku gaya min tambayarku na ke"?.
babu mai bawa Hajiya Kaka amsa,don idan kaka na abinta kowa shiru ya ke idan ba haka ba sai a dawo kansa.
Ƙasim kaka ta kalla ta ce"kai uban son gulma kirawo min ɗana Malik,yanzu duk abinda ya ke ya dawo gida don bazan yarda ba wallahi sai an karɓarwa jikata ƴanci don har hukuma yau sai munje wallahi".
ai suna jin maganar hukuma suka tsugunna har ƙasa suna ba ta haƙuri amman fir Kaka ta ce bata san zance ba".
yana ɗauka kaka ta warce wayar ta ce"kai Malik uwarka ce ke magana duk abinda ka ke ka yi hanzarin dawowa gida,don wallahi yau sai dai ka zaɓa ko ni ko ƴan iskan matanka Iklima da Xeenatu".
yana jin hakan ya ce"ganinan zuwa Umma".ƙit ta kashe wayar ta jehowa Ƙasim,ya yi saurin cafkewa don sauran ƙiris wayar tasha ƙasa.
Mintina kaɗan sai ga shi don daman ba nisa ya yi ba,suna meeting ne a gidan gomnati,tunda ya sauka a mota ya hango ɓangaren na su a cike an ɗaga labule yasan Hajiya Kaka ce da wannan aikin don in dai za ta yi faɗanta ɗaga labule take.
Yana zuwa kowa ya fita don suna matuƙar jin tsoronsa don sam bashi da wasa ko kaɗan balle wargi soja sak a haka ma idan ya juya sai ka ɗauka Bilal ne don suna matuƙar kama da Bilal ɗin.
A hankali ya zauna sannan ya gaida kaka amman ko amsawa bata yi ba ta ce"yo ta ina zan amsa maka ana neman kashe min jikata,janyo ni ta yi ta gurfanar gaban Abba gabana sai faɗuwa ya ke don muna matuƙar jin tsoronsa,duk da wataran yana sakar mana fuska.
Abba ya kalleni sosai ya kalli kuncina ya kalli kaka da mutanen wajen ya ce"waye ya yi mata wannan bin cikinku"?.
Dukkansu har Mamana sai da hankalinta ya tashi don cikin kakkausar murya ya yi maganar,idanuwansa sun kaɗa sunyi jawur jin babu wanda ya basa amsa sai ya ce"babu wanda zaiyi magana acikinku?tunda duk kun rainani ko?".
"yo ta yaya za'ayi suyi magana munafukan banza da wofi kawai,to idan baza ku faɗa ba ni bari in faɗa ka ga wannan ƴar me tallan ƙosan da waccen almurar ƴar fillon dajin suka haɗu suka mari Khairat a fuska ka ga yanzu sun janyo maka asara don ko babu komai ka kashe kuɗi a asibiti."
"umma babu sisin kobon dazan kashe wallahi,su dai da suka aikata abinda sukayi su zasu kaita asibiti sannan kuma daga yau zan kafa mummunan sharaɗi akan cin zarafin Khairat da kuke don wallahi bazan lamunta ba,khairat ta shi ku tafi Asibiti ke da Kaka dasu azzaluman."
sai Hajiya Kaka ta riƙe baki ta ce"A ah wallahi bazani asibiti ba yinin ƴar gidan gaji zanje daman Ƙasimu zai kaini alfarma ɗaya zanyi musu su shigo motar Ƙasimu ya saukesu a kan hanya amman ni baxanje ba,ai sai jikinsu ya gaya musu wallahi don har gado ya kamata a bawa Khairat don wannan zaluncin ya yi yawa,sai ka ce ja ka ni dai wallahi maganar nan ma bata mutu ba dole aje wajen hukuma don su ƙarɓawa yarinya ƴancinta ko wacce muguwa ta ƙwana a cell taji idan da daɗi mugunta."
shiru Baba ya yi sannan ya ce"kaka ki yi haƙuri abar maganar cell ni kenan bani da right agidana dole subi dokokin da zan sharɗanta musu don na isa da gidana".
"ka ga Malik ni fa na gaji da wannan muguntar idan kai abin baya damunka to ni billahil azim yana damuna,don nasan zafin mari don rabona da a mareni tun ubanka yana zafi zafinsa ya mareni ranar kuwa baiyi baccin ƙwarai ba,don sai da na azabtarsa nima,don wallahi fuska itace babbar kadara a jikin ɗan adam."
kunya ta ishi malik amman ya rasa me zaice haka dai ya lallaɓa Kaka muka tafi asibitin,ai kuwa ce wa ta yi a bani gado atake likita ya ce to aka rubuta sannan aka bani magani harda allura sannan bacci ya ƙwasheni,Kaka saboda mugunta asibiti me mugun tsada ta ce Ƙasimu ya kaimu ai kuwa dai me tsadarne don tashin farko dubu talatin aka nema kuma duk ƙwana ɗaya dubu talatin kuma ce wa ta yi ƙwana uku zanyi sai na warke tsaf sannan zan koma,kuma ta ce su zasuyi jinya ta,kuma duk abinda ya samu jikarta sune a rubuta a ajje,bayan wannan kuma idan muka dawo gida sai sun bani tarar kuɗi har na dubu hamsin.
Sosai abin ya bawa kowa mamakin jin furucin Kaka,ƴan gulma ana ta zuwa dubani Kaka kuwa duk wanda yazo babu abin dubiya sai ta sillesa tsaf,Yaya Bilal baya nan tun ranar da abin ya faru sai yau ya dawo ake faƊa masa duk abinda ya faru.
Ransa ne ya yi mugun Ɓaci nan da nan ya wuce sashen kaka alokacin ta fito daga wanka kenan tana duba mudubi tana rangaƊa Ƙwallinta,sai ga shi ya taho kamar daga sama,tsabar tsoro sai da kaka ta yarda mishiyin Ƙwallin tana kallon bilal Ɗin ta ce"oh ni Ƴatsu soja me ye xaka shigomin Ɗaki babu sallama kamar wani na'adaren sarki".?
"ba gwara ba'adaran sarkin ba,kawai don an mari yarinya shikkenan sai ki ce wai sai an biyata diyya kamar waɗanda sukayi wani kisa,haba kaka kidanga abu mana da sense amman kawai yarinya ta yi ta haɗaki da jama'ah kina ci musu mutunci suma fa ƴaƴane kamar na ki ƴaƴan su ma kuma iyayensu suna sonsu. . ."
Tun kafin ya ƙarasa cikin faɗa ta ce"to ita Khairat ɗin sai aka ce maka daga sama ta danno ta fito,itama ai uwarta da ubanta na sonta,wallahi soja bazan yarda suci banza ba kowacce baƙar muguwa sai ta gane kurenta don wallahi bazan yarda ba ehe idan ma sun turo kane don ka yimin rashin mutunci ni ba zan yarda ba,kaima da ka yimin rashin kunyar Ruƙayya uwarka ka yi wa ba niba,don ni ba sallamammiya ba ce".
tana faɗar hakan ta yi ficewarta tana ce wa"yanzu ma asibitin zan tafi don yau za a sallamota kuma a sibitin zasu bani kuɗin in karɓe in bawa yarinya ta yi shagalin gabanta,idan kuma aƙwai wanda zai karɓe bismillah ga ni gashi".
tafiyarta ta yi ta barshi a wajen ya ce aransa lallai tsohuwarnan yau za ta san ta taɓa soja ba dai asibiti za ta ba,mu zuba mu gani.
*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯♀️👎👇👇*
1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5, *AUREN WATA TARA*👩❤️👨
_Miss Hajo_
Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300
*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.
Domin tura shaidar biya👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇
0817 952 3215
Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩❤️👨
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*miss green ce*
[01/09, 08:22] my no: _*🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!*_
📃Littafi na 1
By🪶
*Ummu maher(Miss green)🍏*
*GAWURTATTU 5*
---------------------
*Wattpad user name*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333
---------------
*Arewa book user name*
https://arewabooks.com/u/rabiattu0444
-------------
*Sirrinmu*
manzon Allah(S.A.W)ya hanemu da saka turare idan zamu tafi don yaɗa xinar idone,don haka mu kiyaye.
------------------------
7🟩8
. . . .Tun ka fin ta ƙarasa bakin gate ɗin taga duk babu motocin gidan,ta ce"oh mu dai Allah ya tsaremu da mugayen mata yanzu tsabar baƙin ciku don zanje nemawa jikata ƴanci shine za a ƙwashe motocin gidan a ɓoye."
Ammar ta hango ɗan gidan Baba ƙasim me bin baba auwalu,da sauri ya fara neman wajen Ɓuya tunda yasan halin kakar ta su,da sauri ta ce"Zo nan Ammaru ko Ƙasimu ubanka bai isa ina masa magana ya ƙi zuwa ba,saboda uwarka ƴar borno tasha ruwan babur na baƙin hali shine ina magana zaka ɓoye?".
ɗan shafa kansa ya yi sannan ya ce"haba kaka wane ni na'isa kina magana in ɓuya,ai ban isa ba yanzu dai me ki ke so?".
"ayyo to na ɗauka rashin mutuncinne ta motsa tunda kasha nonon babur ƴan maiduguri".kallon kakar ta sa ya yi sannan ya ce"wai ke kaka me yasa kullum sai kin zagar mana iyaye sannan ki ke jin daɗi ne?don Allah ki daina yadda ki keson ƴaƴanki muma haka mukeson na mu".ta ɓe baki Hajiya kaka ta yi sannan ta ce"to rasai ai dole inyi zagi tunda kasha nonon rashin kunya,yanzu dai ni dai ina duka motocin ƴaƴana aka kaisu"?.
kallon ɓangaren da Bilal ya ke Ammar ya yi yana jingine a jikin gate ɗin yana kallonda dramar da kakar ta sa ta ke yi,Ammar ya ce"to kaka ni kuma da ba ma hawa motar na ke ba Dady ya hanani ta ina kuma zan san wanda ya fita da motar ni motar Hajiyata kawai na ke hawa a gidannan".
"to me Hajiya tunda dai bakasan inda motocin suke ba shikkenan ba sai ka gaya min kai ɗan hajiya bane,tunda ni dai ba ƴar hajiyar ba ce to shikkenan,bari inje in hau motar haya in tafi abuna ni dai yau babu me hanani zuwa ƙwatarwa jika ta ƴanci duk baƙin cikin mutum ma sai dai ya yi don ya yi ta banzar.
Tana fitowa waje ta dinga tsare adaidaita amman suna ƙin tsayawa,cen ta hango Bilal yana ɗaga mata hannu cikin motarsa ya yi gaba abinsa.
"Kai amman yau muguntar fulanin bauchi ta tashi ai Bilal kasha a maman ruƘayya uwarka dole ka Ɗagomin hannu a mota,yau zanga wanda ya Ɗaure maka gindi a gidan,cikin gidan ta koma tana ta banbaminta ta wuce saahen Mahaifiyar Bilal tana zuwa kuwa ta sameta a farlo tana cike wasu takaddu,da sauri ta ajje aikin da ta ke Rashida da Nusaiba suna tayata aikin da sauri suka kalli kakar ta su don sunsan aƙwai abinda ya kawota.
"Yanzu Ruƙƙaya ke ce kika bawa ɗanki Bilal damar wulaƙantani a idon duniya ko?ki ka sakashi ya ƙwashe motocin gidan ya ɓoyesu don kada inje in karɓarwa jikata ƴancin ta ko?".
"haba Umma ta yaya zance ya aikata hakan?wallahi ban san komai a game da hakan ba,don Allah ki yi haƙuri idan ya dawo zan samesa muyi maganar".
"ikon Allah ki ma samesa kuyi maganar ba ma ki hukuntasa akan ɓata min ɗin da ya yi ba ko Ruƙayya?tunda shi Bilal ɗin shine ya haifeki ba ke ce ki ka haifesa ba ko? to shikkenan idan shi Abdullahi ɗin ya dawo ya yi masa faɗan tunda ke tsoronsa ki ke ji?".
tana faɗar hakan ta yi tahowarta,Rashida ta ce"ni fa daman nasan ba alkhairi ya kawo wannan tsohuwar ɓangarenmu ba?ke dai umma kada ki yi magana don wallahi idan ki ka ce wa yaya Bilal hajiya kaka tazo nan kin san zuwa zaiyi suyi ta ɗauki babu daɗi don haka kawai ki saka musu idanu,idan ba haka ba wa ke shiga tsakanin kaka da Yaya Bilal?.
shiru dai Hajiya Ruƙayya ta yi kanta na yi mata ciwo ta ce"Nusaiba ɗakkomin paracetamol insha kaina ciwo ya ke".da sauri nusaiba ta ɗakko mata a wani ƙaramin kid tasha sannan ta haɗa kayan ta koma ɗaki.
Nusaiba na ganin mahaifiyar ta su ta tashi ta ce"Anty Rashida gaskiya kaka ba ta ƙyautawa wallahi kawai daga abu ya haɗota da Yaya Bilal sai ta ƙare akan Mama ai bai kamata ba wallahi,ki ga fa abinda ta kewa mamansu Khairat kulli yaumin sai ta goranta mata wai ita tuba ce?ai bai kamata ba tunda har ta musulunta."
"hmm ke dai bari nusy wallahi matar nan ta tsayamin a ƙahon zuciya jira kawai na ke wataran ta taɓoni tasan ta taɓoni don abinda ta kewa iyayenmu ya isheni wallahi".
"hmm Anty Rashida gwara dai abi a sannu mu rabu lafiya tunda ta kusa sheƙawa ma kowa ta huta wallahi da jarabar mafaɗaciyar tsohuwa,ai Yaya Bilal ɗin shine dai dai ita kaf gidannan,yanzu ba ta ce wai za ta faɗawa Baba ba wallahi muna nan da ke baza ta faɗa masa ba,don ni nasan irin son da takewa Yaya Bilal,suna cikin hirar ya shigo don haka suka tsuke bakinsu suna yi mai sannu da zuwa,yasha mur ya ce"ina Mama take?".da sauri nusaiba ta ce"tana ɗakinta yanzu ta shiga don kanta na ciwo".
Shigewa ɗakin mahaifiyar ta sa ya yi ya barsu anan,Nusaiba ta ce"Anty wai me yasa Yaya Bilal ya fimu ƙyau ne?shiyasa magana ma sai ya ga dama ya ke mana mu dai sai fari kamar zabaya amman kuma ya fimu ƙyau."
"Ke ni dai rabani da maganar wannan bawan Allah kinfi kowa sanin kunnensa yanzu ya iya dawowa ya ɓata mana rai don haka ni dai ki bar maganar".
hajiya kaka ranar har kuka ta yi wai Soja ya hanata fita a gidan don yasan shi soja ne,duk wanda ya shigo ɓangarenta sai ta faɗa masa ai soja ya wulaƙanta ta.
An sallomoni daga asibiti na yi garau dani kamar ba ni ba,Baba kuma ya kafa musu tsauraran sharuɗa akaina don haka kowacce ta kama mutuncinta arabu lafiya.
Sanda aka sallamo ni Yaya Bilal ya koma da daddare na nufi sashensu ina zuwa na tarara da Abba da Hajiya na gaishesu na wayance na shige wajen Rashida har ta fara bacci na tasheta tana mitar waye ya tashe ta sai ta ganni ta ce"gaskiya Khairat ba ki da mutunci kinsan yau yini na yi aiki sai da wannan ɗan wahalar ya tafi sannan muka huta".
mamaki ne sosai kam fuskata na ce"waye kuma ɗan wahala Rashida?".banza ta yi min ta shiga banɗaki ta fito tare da ɗauro alwala ta kalleni sannan ta ce"wa ye kuwa daya wuce yaya Bilal?".harararta na yi sannan na ce"gaskiya Rashida wallahi baki da kunya yanzu yayan namu shine ɗan wahala?ni zuwa ma na yi in gansa inji sanyin a zuciyata ashe kuma ya tafi".?
sheƙeƙe ta yi tana kallona sannan ta ce"lallai khairat wai ke haryanzu yaya yana ranki baki ciresa ba?gaskiya idan har zan baki shawara ki haƙura da yaya don wallahi aƙwai matsala babba idan har ki ka ce zaki so yaya,saboda idan ma baki sani ba yau ki sani yaya ya wuce duk yadda ki ke tunanin mata da yawa suna kawo kansu waɗanda suka amsa sunansu mata masu ji da kuɗi da mulki amman wallahi ko kallo basu ishesa ba,wai shi har yanzu bai ga macen da ta ƙwanta masa ba,don haka ina mai baki shawara khairat ki yi haƙuri ki ciresa daga zuciyarki,ga maza masu mulki masu komai suna sonki ammanke kin dage sai yaya gaskiya ki yi haƙuri ki zaɓi ɗaya a cikinsu musha biki".
wasu hawaye ne masu zafi suka zubomin,nasa bayan hannuna na sharesu sannan na tashi zan tafi duk jikina a saɓile,janyo hannuna Rashida ta yi sannan ta ce"yi haƙuri khairat wallahi ban san abin zai ɓata miki haka rai haka ba ƴar uwata,insha Allah daga yanzu bazan ƙara faɗa miki haka ba,zan taya ki da addu'ar Allah ubangiji ya baki Yaya Bilal".tana faɗar hakan ta rungumeni tana kukan tausayina i'tama.
****
Kamar yadda kuka sani part 12 ne agidanmu kuma duk ƴaƴan Hajiya Kaka ne su da ta haifa da mijinta,Baba Abdullahi shine na farko sai Bananmu Abdulmalik,Baba Tijjani,Baba Kamalu,Baba Sagir,Baba Bashir,Baba Ali,Baba Auwalu,Baba Ƙasim,Anty Zulaiha,Baba usman,Anty Aisha.
Waɗannan sune Ƴaƴan Hajiya Kaka,Abdullahi yana da yara biyar ya aurar da biyu mata saura mata biyu namiji ɗaya
Yaya Bilal,Babanmu kuma yana da Yara 8,Tijjani 9,kamalu 6,Sagir 5,Bashir 10,Ali 4,Auwala 9,ƙasim 6.Zulaihat 7,Usman 2,Aisha uku.
Waɗannan sune jikokin kaka waɗanda adadinsu ya kai 74,dukkansu mazan a gidan suke da ya ke gidane mai yalwa sosai kuma daman tun kafin mahaifinsu ya rasu ya riga daya ta nadar musu waɗannsn filayen kowa da nasa,matan kuma sun ce sun barwa yayyinsu,amman duk da haka sai da suka basu kuɗi masu yawa saboda suna tausayin ƴan uwansu saboda tun suna ƙanana an koya musu tausayin ƙannensu saboda haka tunda suka taso da son junansu suka tashi shiyasa babu wani talaka acikinsu don dukkansu duk wanda ya ke samu zai janyo ɗan uwansa a kusa dashi sosai,kuma kaf ɗinsu mutum biyu ne masu kuɗin,Malik da kuma Abdullahi amman duk sai da suka ja ƴan uwansu a jiki duk abinda suka samu na ƴan uwansu ne.
Hajiya kaka ita da mijinta ƴan asalin jihar baushi ne fulanin usul,amman mahaifiyar Hajiya kaka ƴar zaria ce babanta ne ɗan Bauchi.
Mijin Hajiya Kaka sojane tun zamansu a bauchi sukayi sa,amman ana yi musu transfer sosai daga gari gari,har Allah ya kasu garin kano suka fara zama a gidan haya daga baya ya yi na sa,amman zaman kano ɗin ya fi yi musu daɗi,don unguwar da suke unguwa ce mai ƙƴau unguwar jan bulo,Allah ya azurta su aƙwai filaye sosai a kusa dashi ya dinga siya yana ajjewa har Allah yasa ya siya filaye a kusa dasu sunfi 15,kuma a waje ɗaya suke kusa da gidansa suna zaune a kano ƙwatsam aiki ya mayar dasu a kaduna unguwar malali.amman suna zuwa kano akai akai.
Hajiya kaka tafi son zaman kano don haka ya barta anan ya ɗakki mata ƙanwarta suke zama tare,ƴaƴansu sun fara girma yanzu don haka ma bata fiya zuwa kaduna ɗin ba.
Waɗannan filaye da ya siya ya siyawa yaransa ne,ko kafin yabar duniya ƴaƴansa sha 11,sanda ya mutu bata ma san tana da ciki ba sai daga baya ta haifi autarta Aisha.
Wannan shine taƙaitaccen tarihin rayuwar Hajiya kaka.
*Washe gari*
babu wacce bata shirya a cikin mu ba,saboda ayau