Header Ads
Showing 18001 words to 21000 words out of 22047 words

Chapter 7 - TAKOBIN DAUKAKA complete .txt

Ads the beginning of article before Image

30 May 2024

340

Ads at the middle of Article

bazai bani kunya ba,


Dajin hakan sai boka Dayyubul-Barmas ya zare wani makami a jikin sa ya kunna kai izuwa cikin wani falo,


Sarauniya lasmirat, yaslir, Huzmal, Huruful-labarus da yaransa, da Sunaila tana mai gyara rawanin ta suka mara masa baya , jarumi shamsuddin a ƙarshe har yazamana sun basa tazara mai yawa,


Da shigar su izuwa cikin falon sai suka tarar yakasance makeken mai tsawo da faɗi ba'a iya hango ƙarshen sa, sai suka ci-gaba da tafiya suna kallon abubuwan ban al'ajabi iri daban daban


Yar gajeriyar tafiya suka yi suka iso wata ƙasaitacciyar fada,


Fadar an ƙawata ta da mau,ikan kayan ƙawa da alatun jin daɗin rayuwar duniya,


Ko ina a fadar a tsaftace yake, tunda karagar mulki har na yan majalisa babu kowa akai


Nan fa kowa ya cika da matukar mamaki bisa ganin ƙawatuwar fadar,


Musamman sarauniya lasmirat da take ganin cewa idan aka kwatanta fadar ta da wannan fadar ta tan bakomai ba ce face kango,


Koda koda a tarihi bata taɓa ganin fada mai ƙawatuwa da tsaruwa tamkar wannan fada ba,


Babu abin da yafi bawa su boka Dayyubul-Barmas mamaki kamar yadda aka shirya kayan ciye-ciye da tanɗe-tanɗe a bisa wani kayataccen teburin na azurfa, kamshin abincin ya mamaye fadar baki ɗaya, taimakar an haɗawa wani BASARAKE walima


Nan fa aljani Huzmal da Huruful-labarus suka fara tanɗar baki,har su na dalalar da yawu daga bakin su basu sani ba saboda tsananin kwaɗayi,


Kafin su farga ɗaya daga cikin yaran aljani Huruful-labarus mai suna Barbusa ya ya faki idanun su ya sunkuci wani katon faranti ɗaya mai ɗauke da wani farfesun naman tsuntsu yayi loma ɗaya dashi ya tanɗe bakin sa


Tabbas rashin sani yafi dare duhu inda ace Barbusa yasan abinda zai faru da yayi hakuri da cin wannan naman tsuntsu ya cigaba da dalarar da yawun sa saboda kwaɗayin abincin,


Domin haɗiye abincin nasa keda wuya sai kwatsam aka ga waɗansu jibga jibgan samudawan muridai suna ratsowa daga bangon fadar suna fito wa, hannayen su ɗauke da miyagun makamai, dangin gatari,al'amudi',majaujawa,takobi da mashi,


A dadin su yakai dubu hamsin da ɗoraya, Gaba ɗaya gurnanin muridan ya cika fadar baki ɗaya,


Muridan sun Kasan masu damatsa,suna rafka rafkan kawuna, suna da matukar kwarjini da muni,duk sa'adda dayan su ya ajiye lafceciyar ƙafar sa a fadar sai kaji ƙasa ta amsa saboda karfin takun,


Haƙika waɗannan muridai sun kasance ababan tsoro domin duk da irin dakewar zuciya irin ta Boka Dayyubul-Barmas, lasmirat,Sunaila , yaslir sai suka ɗimauce, tamkar ace ƙyat suka zura da gudu,aljani Huruful-labarus,saltir da Barbusa har sakin gudawa sukayi a wando saboda da firgici,


Shi kansa jarumi shamsuddin a matukar razane yake kawai saboda addu'ar da yake ne yasanya tsoro ya kau daga daga zuriyar sa ,


Nan fa nan fa aka fara kallon kallo tsakanin su Dayyubul-Barmas da muridan lokacin da muridan suka kammala yi musu kawanya sai suka buɗe wata hanya a tsakiyar su ta yadda mutum goma zasu iya tsaya a jere


Take wani gurnani ya dunga bayyana a hanyar gami da karfin takun sawaye,


Sannu a hankali sautin yana ƙaruwa jim kaɗan sai ga wani narkekeken muridi ya bayyana,


Shin dai muridin yafi sauran girma da kwarjini sannan ya na ɗauke da rigar sarauta a jikin sa alamun dake nuna cewa shine shugaban muridan,


Shugaban muridan ya karewa su Boka Dayyubul-Barmas kallo, kawai sai ya bushe da dariyar mugunta mai kama da haniniyar doki,


Sannan daga bisani ya murtuke fuska tamkar an aiko masa da SAKON MUTUWA


Sannan ya buɗe wawaken bakin sa daya fi kama da bakin rijiya saboda girman sa cikin kakkausar murya


" Lalle marhaban da zuwa fadar uban muridai KIRMALU IBN SHAMSHAN,


Yaku wadannan bil'adama kuyi sani cewa yau fiye da shekaru dubu shida babu wata halitta da ta taɓa zuwa tsauni na DARUL-SHAFRAS sai ayi


Na tabbata cewa abinda ya kawo ku baya rasa nasaba da Ruwan ma'ul Hayat


Ina so kuyi sani cewa kun kawo kanku gidan musiba da bala'o'i na rantse da gemun mai girma Baddadul-sihir ɗayan ku bazai sauka kasan wannan tsauni a raye ba,


Domin hakan ya zamo darasi ga bil'adama masu taurin kanki da wauta irin yaƙi,


Koda shugaban muridan duniya KIRMALU IBN SHAMSHAN yazo nan azancen sa Sai ya sake bushe da dariyar mugunta a karo na biyu


Koda can sai ya murtuke fuska kawai sai ya dakawa yaransa tsawa dake nuna su afkawa su boka Dayyubul-Barmas


Take yaran suka ɗauki kansu suna ihu da kururuwa mai firgitar wa


Nan fa ana haduwa aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matukar muni ban tsoro gami da tashin hankali,


























Al'amarin sarki Hamras kuwa tun sa,adda da ya tura hadimin aljanin sa wato Huruful-labarus domin ya ɗauko masa gashin kan sarauniya lasmirat da boka Dayyubul-Barmas sai ya shafe tsawon kwanaki ashirin batare da yaji ɗuriyar su ba


Sai kawai ya nutsa bisa halarar tsafin sa domin yaga abinda ke wakana,


Ai kuwa nan take ya ga dukkanin abinda ya faru tsakanin Huruful-labarus da jarumi shamsuddin, tun daga inda Huruful-labarus ya rusawa su sarauniya lasmirat wannan iska sihiri suka kamu da barci mai nauyin gaske,


Har kawo inda shamsuddin ya samu galaba akan Huruful-labarus a lokacin da suka fafata artabun,


Duk daga farko har karshe ya bayyana a cikin madubin tsafin sa,


Sa,adda Sarki Hamras yaga wannan al'amari a cikin madubin tsafin sa sai ya cika da matukar bakin ciki maral musaltuwa,


Kuma yasha alwashin cewa komai daren dadewa sai ya ɗauki fansa akan jarumi shamsuddin


Kwanaki nabin kwanaki mako nabin mako sai gashi sarki Hamras ya shafe tsawon kwanaki arba'in cif yana da tafiya


A ranar kwana na casa'in ne sarki Hamras yana tafiya a sararin samaniya cikin sauri yana mai keta gajimare cikin matsanancin gudu tamkar giftawar tauraruwa mai wutsiya


Yana cikin wannan hali ne yaji gajiya yafara kamashi


Kawai sai ya yanke shawarar ya sauka ya huta idan yaso sai ya cigaba da tafiya,


Koda gama kammala tunanin hakan sai kawai ya shafi wani gurin shafi a damtsen sa na hagu take yayo ƙasa sulu lu lu luh!


Ya dira a bisa turaba tamakar yakasance mai fuka-fuakai


Inda ya sauka yakasance daji mai ɗauke da manyan tsaunuka da bishiyoyi, duwatsu da ƙwazazzabai,


Hakika dajin yatara dukkan wata sifa ta kwarjini


Daga can nesa sai sarki Hamras ya hangi wani kerarran gida kwarya ɗaya jal a dajin


Al'amarin da yayi matukar basa mamaki kenan kuma ya ɗaure masa kai ya ce a cikin ransa


Shin ko wane ne. Mai mallaki wannan gida kawai sai ya yanke shawarar ya shiga izuwa gidan domin yaga ko mene ne a cikin sa


Koda gama yanke shawarar hakan sai kawai ya durfafi gidan gadan gadan


Idan ka ɗauke karar takun sawaye sarki Hamras dake haddasa motsawar busassun ganyayyakin bishiyun da suke zube a ƙasa babu abinda kunne keji


Wannan shi ne a binda ya faru ga sarki Hamras na mai mulkin Daular aljanu,


*****. *****. *****










































Lokacin da aka kacame da azababban yaƙi tsakanin su boka Dayyubul-Barmas da yaran Uban muridan duniya KIRMALU IBN SHAMSHAN


Sai yaƙin yazamo mai matukar firgici daban tsoro


Karar karafniyar ƙarafa ta cika tsaunin Darul SHAFRAS baki ɗaya


Suka wanzu suna kaiwa juna sara da suka cikin tsananin zafin nama JURIYA DA BAJINTA irin ta JARUMAN DUNIYA


Nan fa su boka Dayyubul-Barmas suka fara gane kuren su domin tsananin zafin naman muridan ya huce tunanin bil,dama


Kai iya hargowar muridan ta isa ta firgita duk wata halitta mai numfashi,


Abangaren jarumi shamsuddin kuwa wani abin mamaki ya faru domin dai gashi a zahiri muridan na kallonsa amma sai ya zamo basa iya ganin ballantana su tunkari inda yake,


Su kansu su boka Dayyubul-Barmas sai da suka cika da matukar mamaki da ganin hakan,


Abin da basu sani ba shine addu'o i da shamsuddin ke karantawa shine ya makantar da idanuwan muridan. Basa iya ganin sa


Sai da aka shafe tsawon dakika ɗari biyar ana fafata artabun babu sassauci


Yazamana cewa su boka Dayyubul-Barmas basa iya mayar da martani sai dai ƙoƙarin kare kansu kawai.


Al'amarin daya fusata muridan kenan kuma ya basu mamaki,


Domin a iya tsawon wanzuwar su a saman tsaunin Darul SHAFRAS basu taɓa yin gamo da halitta mai karfin damtse tamkar su sarauniya lasmirat,


Koda su kazo nan a tunaninsu sai suka sake zage damtse suna kaiwa mu hare haren bazato


Tabbas masu iya magana na cewa idan kiɗa ya canza dola ne rawa ta canza


Faruwar hakan keda wuya sai ya zama na cewa a wannan lokacin muridan sun fara samun nasarar kaftausu sara a sassan jikin su,


Duk wanda ɗaya daga cikin muridan ya kafta sara sai kaji ya tsandara ihu jini yayi tsartuwa,


Kuma ya kife a kasa yana nishin wahala,


Cikin abinda bai gaza dakika ɗari biyu ba muridan suka zubar da su boka Dayyubul-Barmas kasa babu wanda yake wani kwakkwaran motsi a cikinsu,


Sai nishi kawai suke yi numfashin su na fita sama sama


Koda samun wannan gagarumar nasara sai muridan suka bushe da dariyar mugunta suka shiga buga ƙafafuwan su a kasa,


Nan take sautin ɗariyar yayi sanadin sumewar su boka Dayyubul-Barmas,


A lokaci guda tamkar haɗin baki muridan suka tsuke bakunan su tamkar an aiko musu da WASIKAR MUTUWA kai kace basu taɓa dariya ba tunda Allah ya halicce su,


Sarkin muridan duniya KIRMALU IBN SHAMSHAN ya sake ratso wannan hanya ta tsakiyar yaran sa ya taka da kafafafun sa har izuwa inda su sarauniya lasmirat ke kwance,


Yaran sa nayi masa kirari suna cewa


Gaisheka KIRMALU mai duniya


Hadari sa gaban ka inda kake so!


Daji kake ba,a yi maka ƙyaure koda mahaukacin kafinta,


Kai gajimare mai zubar da ruwan musiba da bala'o'i


Kai ne. SARKIN SADAUKAI na duniya,


Sa,adda uban muridai KIRMALU yaji kirarin da yaransa ke yi masa sai ya wangale bakinsa yana mai ɓaɓɓaka dariyar farin ciki,


Duk wannan abu dake wakana jarumi shamsuddin yana tsaye a gefe guda yana kallo


A lokaci guda KIRMALU ya murtke fuska tamkar an aiko masa da SAƘON MUTUWA


Kawai sai ya zare wani mashi a gadon bayan sa mai baki biyu ya daga sama da nufin ya farka cikin sarauniya lasmirat da Sunaila,














Koda ganin abinda ke shirin faruwa sai shamsuddin ya falafala da azababban gudu izuwa kan uban muridai yana mai karanto waansu addu'o'i na musamman a cikin ransa tare da maimakon Ubangijin musulunci,


Yayin da rage saura taku goma tsakanin su, sai a sannanne muridan suke iya ganin shamsuddin da idanuwan su,


Kafin aya daga cikin su yayi wani yunkuri shamsuddin ya shammace shugaban muridan ya gabza masa wani wawan naushi a fuska,


Bisa mamaki sai aka ji uban muridai KIRMALU ya kurma wawan ihu sannan ya jefar da mashin dake rie a hannun sa,


Al'amarin da ya harzua zukatan sauran muridan kenan kuma fusata ainun suka afkwa shamsuddin da azababban yai suka wanzu suna kai masa miyagun hare haren


Shamsuddin ya wanzu yana karewa tare da zillewa harin muridan tare da maida martani cikin bakin zafin nama ta hanyar amfani da hannun sa da kafa wajen kai bugu da naushi,


Tabbas ikon Ubangiji ya huce tunanin an Adam domin abinda mutum yake ganin bazai yiwu ba sai kaga Ubangiji ya samar dashi,


Domin kuwa duk wanda shamsuddin ya nausa a cikin muridan sai kaji inda ya nausa in ya ya karye yayi kara as ruus, ya kurma wawan ihu,


Nan fa ihu da kururuwur muridan ta cika dodon kunne da tsaunin baki aya,


Duk inda shamsuddin ya sanya gaba sai dai kaga muridan na zubewa kasa matattu tamkar yana sassabe a gonar auduga jini yana kwaranya,


Wohoho Hakika duk wanda ya iya ya huta inda ace mutum yana tsaye a wannan waje yaga yadda shamsuddin ke hallaka muridan dola ne ya jinjina masa ya tabbatar dacewa ya cika SARKIN SADAUKAI,


Kafin shuewar dakika ari shamsuddin ya hallaka gaba aya muridan ya zubar da gawarwakin su,


Sa'adda uban muridai KIRMALU IBN SHAMSHAN ya yi arba da gawarwakin jama'ar da sai kawai ya mie tsaye zumbur yana mai kurma wawan ihu


Take wata irin gagarumar Iska ta dunga fitowa daga hancinsa da bakinsa wacce ta sanya gashin kan shamsuddin ya mimmike ,


Kuma tayi sanadiyyar farfaowar su sarauniya lasmirat daga dogon suman da suka yi.


Sa'adda sarauniya lasmirat,boka Dayyubul-Barmas, yaslir, Sunaila,saltir, Huzmal,Barbusa, Huruful-labarus, suka yi arba da gawarwakin muridan kwance cikin jini kuma jikin shamsuddin duk ya aci da jini muridan sai suka cika da matukar mamaki,


Suka ce a cikin ransa shin taya ya akayi shamsuddin ya samu gagarumin karfin da samu nasarar hallaka muridan


Amsar tambayoyin da suka kasa bawa kansu kenan kawai suka zuba idanu domin suga abinda zai faru tsakanin shamsuddin da uban muridai KIRMALU,


Uban muridai KIRMALU na kammala kururuwur sai kawai ya zare wata zabgegiyar adda a ugun sa mai kaifin tsiya ya falfala da azababban gudu izuwa inda shamsuddin yake duk sa'adda ya ajiye afarsa aya sai kaga kafar wajen ta tsage ta rufta izuwa ciki,


Koda ganin hakan sai shamsuddin ya zare takobin sa ya kwala kabbara da karfi ya ruga kan uban muridai don tarar juna,


Lokacin da ya zamo saura taku goma a tsakanin su sai shamsuddin ya zamo an wada agaban uban muridai tamkar an ajiye yanwa a gaban kare,


Lokacin da aka hau sai aka ruguntsume da azababban yai mai matukar firgici daban tsoro,


Shamsuddin ya wanzu yana kare hare haren uban muridai tare da mayar da martani cikin bain zafin nama JURIYA DA BAJINTA,


Duk sa'adda uban muridai ya kai masa hari da addar sa idan ya goce duk abinda takobin ta sauka a kansa sai kaga yayi bindiga ya tarwatse yazama gari koda kuwa gini komai warinsa, nan fa shamsuddin da uban muridai suka tashin hankalin duk wata halitta dake fadar,


Gaskiyar masu iya magana da suka ce fadan da yafi karfin ka sai ka zamo an kallo,


Kuma tabbas idan gwani da gwani suka hau, juriya da naci suka ci karo da juna dole ne yai ya zamo tashin hankali daban tsoro,


Hakan ne yafaru dasu boka Dayyubul-Barmas domin koda suka lura cewa duwatsun da su shamsuddin ke rusawa a fadar suna neman danne su sai suka rarrafa da afafuwan su izuwa bayan waansu duraku a fadar suka lae suna hangen abinda ke wakana


Sai da aka shafe tsawon sa,a aya cur ana wannan bain artabu


Shamsuddin bai samu nasarar koda lakutar jikin sa ba duk kuwa da cewar yana karanta addu'a na musamman a cikin zuciyar sa


Ana cikin wannan artabu ne uban muridai ya samu nasarar make takobin dake hannun shamsuddin a lokacin da ya daka tsalle da nufin ya hau kan kafadar sa


Kawai sai uban muridai KIRMALU ya canza salon faan sa a inda ya shiga kaiwa shamsuddin hari da karfin damtse bada makami ba ,


Shamsuddin ya wanzu yana zillewa harin tare da amfani da dubaru da hikimomi, yana mai kwala kabbara gami da neman taimakon daga sunayen fiyayyan halitta annabi Muhammad s,a,w,


Nan take wani irin gagarumin karfi ya shige sa kawai sai ya daka tsalle sama ai ku wa sai gashi a saman uban muridai tamkar an janye sa da ungiya,


Kawai sai ya dunkule hannayen sa biyu ya irawa uban muridai KIRMALU naushi a wuya,


Saboda arfin naushin sai da asusuwan wuyan sukayi ara ruus as!


Uban muridai ya kurma wawan ihu, Kafin ya sake wani yunkuri shamsuddin ya sake gira masa wani naushin.


Kawai sai akaga jikin uban muridai ya sandare ya yi asa zai fao,


Koda shamsuddin ya lura cewa zai rikito daga saman uban muridai sai kawai ya dako wani wawan tsalle naban al'ajabi da mamaki ya sauka abisa turba,


A lokacin da gangar jikin uban muridai KIRMALU ta fai asa rikica, tamkar an jefar da toron Giwa ko shurawa bai yi ba


Nan fa mamaki ya turnue su sarauniya lasmirat Bisa ganin gagarumar bajintar da shamsuddin yayi na hallaka uban muridai KIRMALU da yaran sa.










Al'amrin su shamsuddin kuwa sai da suka shafe tsawon kwanaki huu a saman tsaunin Darul SHAFRAS,kowa ya warke sumul daga raunukan dake jikin sa,


Bayan shamsuddin ya samu nasarar ebo ruwan ma,ul- hayat a wani bangare a tsaunin,


Sannan su aljani Huzmal suka sake aukar su aka cigaba da tafiya,


Ana cikin wannan tafiya ne a lokacin da rana ta take sai sarauniya lasmirat ta dubi Sunaila tayi gyaran murya sannan ta kawo gwaron numfashi ta ajiye tace " ya Sunaila inyi miki wata tambaya mana idan bazaki damu ba,


Sunaila tace " ina sauraren ki fai tambayar ki,


Lasmirat ta ce" A can baya lokacin da kika samu nasarar akan wannan aljana acan birni na lokacin da na tambaye ki labarin rayuwar ki kin faa mini cewa baban Burin ki shine ki sadu da mutane ma,abota addanin Musulunci, domin aukar fansa akan wani azzalumun sarki shin


Jarumi shamsuddin baya aya daga cikin mutanen da kike nema ne?


Koda jin wannan tambaya sai sunaila tayi murmushi


Duk da kasancewar fuskar ta na rufe da rawani sai da lasmirat taga alamun loawar kumatun ta a lokacin da tayi dariyar,


Sannan ta dubi lasmirat yace" ya yar uwa ta kiyi sani cewa bawai ina tantama Game shamsuddin ba ne tabbas yana daga cikin ma, abota addanin Musulunci da nake nema sai dai ina so na kammala haa waansu hujjoji ne sannan na kari Addinin sa,


Koda jin wannan jawabi daga bakin Sunaila sai lasmirat ta gyaa kai Sannan ta bui baki akaro na uku da fara wannan tattaunawa ta ce"Amma kina ganin Ubangijin shamsuddin bashine abinda dogaro ba kuwa ki dub kiga yadda ya samu nasara akan su aljani Huruful-labarus da uban muridai wanda boka Dayyubul-Barmas yagaza kare mu,


Koda jin wannan batu daga bakin lasmirat sai sunaila tace"Tabbas duk abinda kika faa akan shamsuddin haka ne harma ya huce haka inda ace kin taa karanta jarumi Hilal da irin nasarar da ya samu a rayuwarsa da ke kunshe a cikin littafin KARSHEN ZALUNCI,


da zaki tabbatar dacewa girma da sha,anin ma,abota addanin Musulunci ya huce yadda ake tsammani,


Koda jin wannan batu sai sarauniya lasmirat tayi ajiyar zuciya sannan ta kawo gwaron numfashi ta ajiye tace" Ta ijan idan kuwa har haka ne abinda shamsuddin yayi abaya bakomai bane. Face sharar fage domin ke gaban mu yafi na baya yawa,


Tafiyar kwanaki arba'in akayi aka iso kogon Garul- barzahu inda kubar miftahul-daryal take


Sai da shamsuddin yasha gwagwarmaya dakyar da taimakon Ubangijin halitta ya samu nasarar kashe miyagun halittun dake ciki,kuma ya samu nasarar auko kubar miftahul-daryal,


Hakika su sarauniya lasmirat sun ga iko da kudirar Ubangiji a wannan rana


Bayan kwanaki biyu sai aka sake cigaba da tafiya domin isa gidan boka Daryalu domin ebo ruwan koramar sa


Yayin da aka iso cikin koramar sai aka tarar tana auke da waansu irin halittu masu auke da fuka-fukai irin na jemagu suna da kawuna irin na bil,adama, suna wani irin

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads