Header Ads
Showing 66001 words to 69000 words out of 173834 words

Chapter 23 - MATAR MUTUM Document Complete by Samira Haroun.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1131

Ads at the middle of Article

fassara, ta d'auka mutumci ne kawai ashe abinda ke ransa kenan?


Mimi ce ta d'an tsamiketa a cinya hakan yasa ta fad'in "Washhhh!" Da sauri ta kama bakinta tana kallonta, da ido Mimi ta mata alamar ki amince mana, ita kuma ta mata alamar ni a wa? D'an tsaki tayi tare da yin kamar zata daketa, hakan yasa Asma'u jinjina kai tace "To zanyi tunani ko?"


Cikin murmushi Sadeeq yace "Ba matsala, zan jiraki har kiyi tunanin."


Bud'e baki sukayi da mamakin ashe ya ji me ta ce, da hirar raha da nishad'i har suka isa katafaren gidan daya had'u sosai aka k'watashi saboda hidimar da za'ayi.


Tabbas gidan ya cika mak'il da mata manya da yara ga kuma yan mata, saidai maganar gaskiya sun zo ne ganin zahiri da idonsu, tabbas su d'in ahali ne masu ilimi da sani sosai, amma fa suna da wani abu da saika rantse gidan jahilai ne, maganar talaucin gidansu Mimi a yanzu ba shine gabansu ba kamar da aka fad'a musu su waye iyayenta, sai suka zo tabbatarwa da tambayar kansu dame yarinyar tafi na su yaran da dayawa daga ciki aka so had'a Asas dasu amma ya k'i. Yan matan kansu suna so suga yarinyar ne dan su mata kallon hadarin kaji idan da hali ma har su yaga mata rigar mutumcinta.


Ai kuwa yamma na k'ara yin sanyi sai ga motocin angaye sun aje dangin Mimi, yanda suka fara shigowa harabar d'aya bayan d'aya yasa duk akaa kafesu da ido, su Shapi'a ne a gaba suka fara shigowa, hakan yasa wani gungu na 'yan mata kecewa da dariya ganinsu dunk'ul dunk'ul kamar yara amma kuma da fuskar dattijai, ajiyar zuciya Sahura ta sauke tace "Allah gamu gareka, nagode Allah da Mimi bata wurin nan da anyi b'atacciya."


Shapi'a ce tace "Ni kam fatana yanzu ta zo dan naga yanda zata ci uwar yarinya idan aka nemi wulak'anta mu."


Ido Sahura ta zaro tace "Rufa mana aisri Shapi'a, kai tsaye fa zata ce ta fasa auren d'an uwan nasu."


Cike da rashin dana sani Shapi'a tace "Idan tayi haka ma ai sai ta birgemu, wannan ai rashin sanin darajar d'an adam ne kamar ba gadon ilimi Sharif ya bar musu ba."


Murmushi Sahura tayi tace "Ya bar musu gadon ilimi, amma yayanshi kuma sun bar musu gadon dukiya, hakan ya jawo dayawa daga ciki dukiyar ce tafi aiki a tunaninsu."


Tab'e baki tayi tace "Allah ya kyauta musu."


Dogaye da gajeru ne suma haka duk suka samu wuri suka zauna ana d'an gaggaisawa sama sama, hakan ya jawo kowa ware nashi ya koma gefe ana k'us-k'us-k'us, tubarkallah farfajiyar ta cika har kujeru na neman yin k'aranci duk yawansu, dan kuwa kafatanin ahalin Sharif duk sun hallara, kama daga iyalin Aliyu Sharif, Usman Sharif, Salmanu Sharif da sauran abokan arzik'i, sosai Hafsat ke k'ok'arin ganin an samu sanayya da kuma fahimtar juna tsakanin danginsu da dangin Mimi, hakan yasa take ta nunawa iyayensu su Shapi'a a matsayin iyayen Mimi, wasu suna sakin jiki su karb'esu a gaisa, wasu kuma gaba da gaba suke yatsina fuska suna musu yak'e, hakan bai ma Hafsat dad'i ba amma ya ta iya, sharesu tayi ita ma tana fama da cikinta da wunin yau ta ji bai motsa mata ba ga wata muguwar kasala, jefi-jefi kuma sai taji gabanta ya fad'i kawai ba dalili, saidai bata bar ambaton ubangiji ba a bakinta da haka take jin sanyi sanyi a ranta.




Sanda motocinsu suka tsaya angayen ne suka fara fitowa suna shigowa filin, sai k'awayen Mimi da suka jera gwanin sha'awa suka sakata tsakiya tare da Asas dake ta doka murmushi, Mimi kan kanta na k'asa tana fama da rik'e jakar hannunta rigarta kuma na jan k'asa.


Kowa sake waro idanu yayi dan tabbatarwa kanshi abinda yake gani, dangin Mimi da dama sun san kayansu ba daga nan ba indai wajen d'aukar wanka ne da iya gayu, saidai yanda ta zama tamkar wata balarabiya ya k'ara birgesu da kashesu a game da ita.


Inda yan matan nan kuma suka shiga tamtama wai dama haka yarinyar take, sam babu wata makusa a tare da ita da zasu kushe, duk da kwalliya tana canza hallitar mace ta gyarata amma dai sun tabbatar zata yi kyau, na farko tana da dogon hanci ga ta jar fata, su kam idan aka barsu sai su ce wata baralabiya ce, duk sai suka kasa motsawa a wurin dan kwarjini ma suka ji tayi musu yarinyar, sai yan matan amaryar ne da angaye da suka dage suna ta d'aukarsu hotuna, da haka aka isar da Mimi kan kujerarta sai su Asas da suka bar wurin dan dama fa anyi ba dasu za'a yi hidimar ba.


A cikin taron yan matan nan akwai guda d'aya wacce ita ba fa abinda ya kawo kowa ya kawota ba, na ta k'udirin babba ne daya girmi na kowa dan kuwa sak'on Muttak'a ta zo isarwa, tasan kasada zatayi amma kud'in daya bata tare da yi mata alk'awarin aure yasa ta ji zata iya yin koma menene, tun shigowarsu Mimi ta mik'e ta shige zak'ewa akan komai tana kamkamba kamar wata yar uwa. Dangin Mimi kallonta suke yanda rawar kanta yayi yawa suna tunanin wata yar uwace makusanciya ta Asas. Inda suma dangin Asas suke kallonta wata marar hankali daga b'angaren Mimi take, da wannan kallon da duka kusurwoyin ke mata aka kasa samun wanda zaiyi mata maganar shishigewa da take musamman ta b'aangaren abinci.


Magriba na gabatowa Hafsat ta gabatar da masu ruwa da tsaki ayi kamun amaryar, ana idawa Hafsat tasa Aisha da su Fanna suka kawo cake dan ta yanka tunda ba wani abun ci aka ware mata ba ita, da taimakon Asma'u ta yanka Asma'u ta d'an saka mata a baki aka musu tapi ana dariya, *Feena* ita tayi babakere ta d'auki lemu ta tsiyaya a cup na glas, a hannunta dama akwai k'aramar k'waya babu wanda ya kula da tsiyarta bare ya lura har ta saka, mik'awa Asma'u tayi ita kuma ta mik'awa Mimi, amsa tayi ta d'an kurb'a zata aje Feena ta sake fad'in "Ki k'ara mana, ko ruwa baki sha ba fa."


Dayawa kallonta sukayi sai Mimi da take kallonta a matsayin dangin wanda zata aura, wannan kunyar tasa ta d'an k'ara kurb'awa kafin ta aje, Feena kam murmushi tayi duk da bata ji dad'i ba da bata sha sosai ba, amma dai tunda Muttak'a ya bata tabbacin guba ce mai had'ari sauta share kawai, a hankali ba tare da lurar kowa ba tayi kamar tana amsa waya ta fita a wurin.


Ana kwad'a kiran sallah magriba su Asas na dawowa d'aukar amarya, Hafsat ce ta rik'e hannunta saï Asma'u a gefenta sauran yan mata a gaba wasu a baya suka nufi hanyar fita, Mimi dake jin matsanancin murd'awar ciki da jin kamar an rik'e mata numfashi ba tare da ankarewar kowa ba ta tafi baya luuuu! Ta fad'i a wurin, da sauri Hafsat ta kalleta tare da sakin hannunta tana furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un! Mimi."


Asma'u ma da sauri ta durk'ushe tana kiran "Mimi, Mimi lafiya."


Take aka rufe wurin ana tambayar lafiya, cikin tashin hankali Hafsat ta d'ago kanta ta kalli Aisha tace "Eesha kira Asas a waje."


Mayar da kallonta tayi kan Mimi, a hankali ta lura da jinin daya fara b'ullowa ta hancinta, cikin tsananin tashin hankalin da take jin bata tab'a riska ba ta daure ta d'ora hannu a kai tace "Na shiga uku, me ya sameta?"


Da gudu Asas ya shigo tare da rakiyar zaratan mazan a bayanshi, suna zuwa suka bud'a musu hanya, da sauri ya durk'usa yana fad'in "Me ya sameta? Me aka mata?"


Shapi'a ce tace "Ba abinda aka mata, ni fa ina ganin ko mayya ce ta kamata a wurin nan?"


Dayawa daga cikin mutanen suka kalleta sai wata mace mai aji sosai da tace "Nan ciki akwai wanda ya miki kama da maye ne?"


Hafsat ce tace "Bana tunanin haka, mu kaita asibiti jini ne yake fita a hancinta fa."


Wata dattijuwa ce tace "To ko tana da iska ne?"


A sukwane Asas ya mik'e tsaye tare da tattara k'arfinshi ya d'auki Mimi cak ya fita da ita da gudu, duk rufa masa baya akayi hankali tashe da tunanin miye zai faru, yana sakata mota yaja da gudun tsiya zuwa asibitin sheikh data fi kusa dasu har da ma gidanshi duk yana kusa da masaukin bak'in na shi, duk tarin tilin motocin dake wurin kad'an ne suka bi su zuwa asibiti dan su san halin da take ciki.








*Gobe d'aurin aure fa*�






*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:54 PM - Ummi Tandama😇: 👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩�����
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩�����


*NA*




_SAMIRA HAROUNA_




*SADAUKARWA*



_GA DUKA_


*'YAN AMANA TA*




💫� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_�


� *[ T.M.N.A]* � 📖🖊�


https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/


_Bismillahir rahamanir rahim_




*26*




Ana gama d'aurin auren ya lumshe idonshi yana jimk'e hannunshi kamar zai naushi wani, kabbara aka d'auka a masallacin dan shi ne aure na k'arshe da aka d'aura tsakanin *Maryam Adam Shehu* da kuma *Abdul Waheed Salman Aliyu Sharif*, duk mik'ewa mutane sukayi ana fita da magana a baki, wasu hakan ya musu daidai da son zuciyarsu, wasu kuma hakan bai musu ba ko kad'an, sheikh kam bai motsa a wurin ba haka aka dinga bashi hannu ana mishi addu'ar fatan alkairi, su Abba ma fita sukayi yana kiran gida ba'a samu, dan haka mijin Sahura da suke tare ya jaraba kiranta kuma aka samu, shi ne fa suka sanar musu dan karsu ji abun daga sama kafin su isa gida. Saida yaji masallacin yayi shiru alamar ba mutane kafin ya d'aga kan shi, ai kamar wanda aka kora da gudun tsiya sai kuwa yayi wuf ya mik'e yana sab'a babbar rigarshi ya fita shi ma su Alhaji Ibrahim da Saleh suka rufa mishi baya tare da jami'anshi.


Duk motocinsu suka shiga inda sheikh ya kalli dreba yace "Dan Allah kayi sauri, gidan Hajia zamu je."


"To sheikh." Ya fad'a yana sake murza sitiyarin da kyau, ji yake an k'i kawowa gidan, gaba d'aya gani yake ba'a sauri kamar ya fita yaje da gudu a k'afarshi, tambayar "Anya kuwa Hajia tasan wa ta bani?" Yake yi, numfashi kawai yake saukewa lokaci zuwa lokaci, da wannan tashin hankali suka isa gidan daya k'ara kaurewa da mutane maza da mata, a k'ofar gidan motar ta tsaya sheikh ya fita, duk da hankalinshi a tashe yake kuma sauri yake sosai, amma tafiyar a nutse yake yin ta cikin hankali, gaisheshi ake da girmamawa kamar wani sarki shi kuma yana amsawa da murmushin yak'e a fuskarshi, har suka shiga cikin gidan ya fara hango Hajia a b'angaren Asas zaune a k'ofar shiga falon, mutane duk anyi cirko cirko wasu zaune wasu kuma tsaye babu mai magana.


Da sauri ya isa garesu saida ya kai daf dasu ya fahimci matar Alhaji Ibrahim ma tana tare dasu Kubra da matar Saleh sai Hafsat zaune kan ta a k'asa, kallonta yake yana karantar yanayinta, sosai ta bashi tausayi dan alamu sun nuna tasan abinda Hajia ta aikata musu.


Kallon juna sukayi da Hajia cikin rikitacciyar murya yace "Hajia ya haka? Ina Asas?"


Sake rumgume hannayenta tayi tace "Yana ciki likita na dubashi."


Sake kallon Hafsat yayi, matsawa yayi kusanta ya durk'usawa ya kamo hannayenta cikin na shi, da k'yar ta d'aga idonta ta kalleshi tana mai danne abinda ke zuciyarta tare da dakatawa da karatun suratul nisa'i data shiga tunda abun ya faru dan ta tunawa kanta cewa hukuncin Allah ne fa, shi ne ya hukunta musu suyi, da k'yar ta k'ak'aro murmushi da shi yana gani yasan bai kai ciki ba tace "Barka, ina tayamu murnar k'ara girma, ina tayaka murnar k'ara samun wanda zaka ciyar fisabilillah, Allah tayaka rik'o sheikh."


Yanda muryarta ke rawa yasa ta dakatawa dole dan bata so tayi kuka, girgiza kan shi yayi tare da d'ora hannunshi a cikinta shi ma kamar zaiyi kukan yace "Kin tabbatar kuna cikin k'oshin lafiya?"


Saida ta d'ora hannunta akan na shi ta jinjina kai tace "Eh, ba komai."


Girgiza kai ya sake yi yace "Da komai Hafsat, zamuyi magana a gaba kinji."


Mik'ewa yayi tare da sakin hannunta ya kalli likitan daya fito, yanda suka zuba mishi ido yasa shi girgiza kai yace "Saidai kuyi hak'uri, Allah ya gafarta masa."


Da sauri ya rab'ashi ya wuce d'akin haka Alhaju Ibrahim da Saleh ma da kuma Sadeeq da suka samu a nan, tabbas dai abinda kowa ke gani shi suma suka gani, a hankali ya zauna bakin gadon yana k'arewa fuskar Asas kallo, lallai duniya *budurwar wawa*, jiya suna tare da bawan nan har safe ma haka, kai har k'arfe 10:45 suna tare dashi yana mishi mitar ya bashi jaka d'ari biyu shi babu kud'i a hannunshi, kuma banki a lokacin yasan ba zai samu ba dan juma'a ce, shi ne yanzu kwance haka a gabanshi baya motsi.


A sanyaye ya sauke wani numfashi kanshi k'asa yace "Zamuyi mishi sutura yanzu, bayan sallah la'asar insha'Allah saimu kaishi gidanshi na gaskiya."


Jinjina kai Saleh yayi tare da kallon Sadeeq da idonshi zasu tabbatar maka kuka yayi yace "A samo mana abinda ya dace a mishi wanka."


Jiki a sanyaye ya fita yana sako da wasu hawaye, a kullum Asas fad'i yake "Aure na shine silar warakata." Ashe wannan warakar yake nufi? Duk tunaninsu zai warke ne daga ciwon ashe warkewa ta har abada yake nufi, bayan wani lokaci ya dawo gidan a lokacin kowa yayi zugum anyi zaune kan tabarmi an shirya zaman makoki, yana kawo musu abubuwan buk'ata sheikh ya mik'e yana aje hularsa akan gadon, cire babbar rigar yayi tare cire machette na wuyan hannun rigar ya aje ya tattare hannayen, cire agogo yayi da takalminshi haka ma safar k'afarshi fara tas, sunkuyawa yayi ba tare da jin nauyin gawa ba ya tallabi Asas kamar yaro ya shiga dashi ban d'aki, akan tabarmar da Saleh ya shinfid'a ya aje shi a hankali kamar k'wai.


Farin towel babban ya rufa mishi daga k'ugu zuwa gwiwanshi kafin yayi dubara ya cire mishi singlet d'in daya saka da wandon shaddar da kuma na ciki k'arami, fararen ruwan masu kyau da aka jik'a da ganyen magarya ya d'iba ya fara da bismillah zai mishi tsarki. *Kamar* jira ake dama a zuba mishi ruwan sai kuwa Asas yayi *zunbur* kamar dukanshi ne aka yi, abun ka ga namiji mai zuciya sam sheikh bai girgiza ba bare ya tsorata saidai idonshi kawai daya zaro yana kallon Asas daya mik'e haka kamar wanda aka maidowa rai da k'arfin tsiya.


Kallon juna suke sosai Asas yana so yayi magana bakinshi ne yayi nauyi, hannu sheikh ya kai ya tab'a goshinshi yaji babu wani sanyi k'alau, a hankali ya kamashi ya mik'ar dashi tare da d'aura mishi towel d'in a k'ugu, d'aukar kayanshi yayi ya bashi yace "Saka wannan."


Karb'a yayi hannayenshi sunyi mugun nauyi, lura da haka yasa sheikh kamo hannunsa hakanan suka fito zuwa falon, da k'arfi Saleh ya mik'e yana fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un."


Su ma mik'ewa sukayi har saida ya zaunar dashi bakin gado, kallon kallo suka shiga yi babu wanda yayi magna, sun jima haka kafin Asas ya d'aga kai ya kalli sheikh, kamar mai koyon magana yace "She..ikh...Au...rena,,,an d...aura?"


Ruf sheikh ya rufe ido da kunyar kallon Asas yace ai kanshi aka maida auren, a hankali ya rab'a Asas ya zauna gefenshi tare da dafe gaban goshin shi, Alhaji Ibrahim ne ya kalli Sadeeq yace "Kira mahaifiyarsa."


Da sauri ya fita inda Saleh kuma ya karb'i kayan dake jimk'e hannun Asas har yanzu ya saka mishi rigar, aje k'amarin wandon yayi ya durk'usa ya zura mishi dogon, yana cikin d'aure mishi zariya Hajia da Hafsat suka shigo tare, da farin ciki Hajia ta fad'a jikin Asas tana fad'in "Allah nagode maka, Allah ka yaye mishi wannan ciwo dake rabashi da rayuwa idan ya taso."


Kamar baya fahimtar me ke faruwa haka ya kalli Hajia data d'ago yace "Hajia, Mimi...aure...an d.aura?"


Tarrr! Hajia ta sauke ido a kan shi, saidai dake ita d'in ba masu kwalo kwalo bace sai tace "Ai tunda muka ganka kwance kamar gawa muka d'auka shikenan, har za'a fasa d'aura auren sai kuma na ce kar ayi haka ko dan ita yarinyar, shiyasa na ce a d'aura auren da d'an uwanka sheikh."


Shi ma dai wani kallo ya bita dashi duk da ya gane hausar da tayi, amma sai yaji yana neman k'arin bayani a sauk'ak'e, ya jima haka kafin ya iya cewa "Hajia matata sheikh ya aura?"


Girgiza kai tayi ta kamo hannunshi tace "A'a autana ba matarka ya aura ba, da matarka ce ai da bai aureta ba."


A sanyaye murya na shak'ewa yace "Hajia matata ya aura, ni ne fa zan auri Mimi."


Had'e fuska tayi tace "Ashraf Mimi dama *ba matarka* bace, baka ga gaba d'aya numfashinka saida ya bar gangar jikinka ba kafin ya auri *abar sa*? Ko kana so ka ce min baka yarda da hukuncin Allah bane? *Maryam matar sheikh* ce shiyasa ka lek'a lahira kafin ka dawo aka d'aura aurensu."


Kamar zai fashe da kuka yace "Hajia hakan ba daidai bane, wannan hukuncin bai yi ba sam, ina son matata, ina son ta Hajia dan Allah a bani matata tunda dai ban mutu ba."


Wata tsawa ta daka masa tana fad'in "Kai kanka d'aya kuwa? Ya auri matar ne zaka ce a mayar maka da matarka? Ita d'in yar tsanace ko wata abar wasa? Ko kumaa auren kake so kayi wasa dashi?"


Alhaji Ibrahim ne yace "Maryama ba haka za'ayi ba." Kallon Asas yayi yace "Kai Ashraf zauna kaji."


Cikin sako hawaye ya juya ya kalli sheikh da kanshi ke k'asa yana ta matse tafukan hannayenshi, shi kanshi fatanshi shine su amince ya sauke wannan nauyin dake kan shi, dan ba zai iya d'auka ba, ba zai yarda ya fara zaman aure da yarinyar da har ga Allah yake jin

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads