Header Ads
Showing 78001 words to 81000 words out of 173834 words

Chapter 27 - MATAR MUTUM Document Complete by Samira Haroun.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1150

Ads at the middle of Article

*NA*




_SAMIRA HAROUNA_




*SADAUKARWA*



_GA DUKA_


*'YAN AMANA TA*




💫� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_�


� *[ T.M.N.A]* � 📖🖊�


https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/


_Bismillahir rahamanir rahim_




*30*






A tausashe ya rabka sallamar da tasa Salammatu amsawa tana kimtsa zamanta daga kallon tv, kamar zata nutse k'asa dan girmamawa ta shiga, gaisheshi, da girmamawa shi ma ya shiga amsa mata dan ba yarinya bace, cike da kulawa yace "Hajia tana ciki ne?"


Nuna mishi d'akin Mimi tayi tace "Ta shiga ciki zata dubata."


Da ido ya amsa alamar to tare da nufa d'akin, da kallo ta bishi da mamakin yanzu nan fa aka barshi da yarinyar can fitsararriya sai ka ganta da ciki wata rana, tab'e baki tayi tana mayar da kallonta kan tv da fad'in "Maza ho."


K'wank'wasa k'ofar ya fara yi daga ciki Hajia tace "Waye?"


A sanyaye yace "Ana."


Da fara'a tace "Shigo sheikh."


A hankali ya bud'a k'ofar tare da d'ora idonshi akan Hajiar dake tsaye, bai yarda ya kalli inda ya tabbatar tana nan ba saida ya gama gaisawa da Hajia, cikin sakin fuska take fad'in "Da na ga dare yayi ai na d'auka ba zaka zo ba, kuma dana tuna kai ne fa sai na sa a raina zaka zo komai dare."


Wani lallausan murmushi yayi tare da d'an shafa sajenshi yace "Hajiarmu kenan, sabgogi ne dayawa, har zan shiga gida kuma na taho."


Da fara'a tace "Allah sarki, Allah ya bada ladar d'awainiya."


"Ameen." Ya fad'a tare da d'an kaikata idonshi ya kalleta, da sauri ya ji zuciyarshi ta fara bugawa, doguwar riga ce a jikinta ta bacci mai laushi, kan ta kuma babu d'an kwali sai gashinta data d'aure, jibda ce take k'ara shafawa a jikinta gaba d'aya.


Tunda ya shigo bata kalleshi ba, kuma sam bata da niyyar zata kalleshi sai murzawa hannayenta jibda take, d'an cije leb'enshi yayi na k'asa kafin yace "Ya jiki?"


Sai lokacin ta d'aga kai ta kalleshi, a cikin ranta tayi k'wafa tuna abinda ya mata a asibiti da tunanin "Zan rama, sai na mayar da kai kamar *kakana*."


Sakin fuskarta tayi tace "Da sauk'i *malam*."


K'uri ya sake mata da ido da nanatawa a ranshi "Malam?"


Hajia dake ta murmushi tana kallonsu ne ta d'an gyara murya tace "Bari na baku wuri ko."


Da wani matsiyacin sauri Mimi ta kalleta tace "A'a Hajia, ba abinda zai min."


A lokacin shi ma yayi saurin juyawa cike da kunya yana fad'in "A'a Hajia, saida safenku."


Amma jin abinda Mimi ta fad'a sai yasa ya tsaya ya sake juyowa, sai kuma ya jinjina kai ya juya zai fita, bayanshi Hajia ta bi tana fad'in "Dama ina son magana da kai."


Da kallo Mimi ta bisu da addu'ar "Allah yasa ta masa maganar wayata, ina so na samu waya."


Suna fita a falon ta zauna a kan kujera, tunda ta ga ya zauna a k'asa ya tabbatar mata yau uwa ake da ita kenan, dan akwai ranar da zasu zauna kan kujera ita dashi, to ranar ana matsayin malami kenan, cikin dattako ta k'ara gyara zamanta tace "Sheikh, nasan nayi maka hawan k'awara a lamarinka a game da auren nan, saidai ka sani ba nayi bane dan na nuna na isa da kai, na tabbata auren nan zai zame maka alkairi insha'Allah, ina fatan baka k'ullaceni ba ko?"


Da sauri ya girgiza kai yace "Subhanallah Hajia! K'ullata kuma? Ko d'aya wallahi, na d'auki hakan a matsayin abu ne da dama Allah ya rubuta zai sameni, tabbas da ita d'in ba *matata* bace da ban sameta ba ko da kuwa ina son haka."


Jinjina kai tayi tace "Naji dad'in haka, yanzu maganar tariyarta nake so naji, yaushe ka tsara?"


Sunkuyar da kai yayi yana mai jin kunyarta sosai, to shi ya zai ce? Ya fad'i ranar da za'a kawo masa tsarar Aisha? Shiru kawai yayi ya kasa magana har saida Hajia tace "To idan ya maka mu barshi a sati d'aya, lokacin na tabbata ka gama gyara mata na ta b'angaren."


Numfashi ya sauke a sanyaye yace "Allah ya sa haka shi yafi zama alkairi."


"Ameen." Ta fad'a ita ma, d'orawa tayi da "Sannan sheikh dan Allah kayi hak'uri da yarinyar nan, kaga fa shekarunta k'alilan ne, dole sai kana kawar da kai da hak'uri, inba haka ba zatayi abu a cikin k'uruciya kai ka ga kamar wauta ce ko kuma da gangan."


Jinjina kai yayi yace "Insha'Allah za'a kiyaye Hajia."


Murmushi ta masa tace "Naji dad'i, Allah ya maka albarka, sai kuma magana ta gaba."


Jinjina kai yayi alamar saurare, d'orawa tayi da "Waya na ce me zai hana ka siya mata? Kaga zata dinga kiran iyayenta ai."


Da wani irin k'arfi ya d'aga kai ya kalli Hajia yana kiran "Waya kuma?"


Ita ma da mamakin yanda taga firgici a tare dashi ta amsa da "E, waya."


Iska ya feso tare da duk'ar da kanshi yana ambatar "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Shi ya siya mata waya? Yarinyar da baisan irin girma da mahimmancin data bawa waya a rayuwarta ba, idan fa ya bata ta ci gaba da rayuwarta data saba, har shi fa sai Allah ya hukuntashi dan yana da kamasho. Cikin nutsuwa da salon bayar da umarni Hajia tace "Zan jira zuwa gobe da safe sai ka kawo mata."


Lumshe ido yayi tare da d'an sinne kai ya jinjina shi alamar to, shiru babu wanda ya sake magana har saida ya d'an tank'ware k'afafunshi yace "Hajia."


Da kulawa ta amsa da "Na'am." D'orawa yayi da "Ki fara shirin aurar da jikarki Eesha, insha'Allah na mata miji kuma bana tunanin za'a d'auki lokaci mai tsayi."


Da fara'a sosai tace "A'a masha'Allah, wannan ai abun farin ciki ne, Allah ya sa alkairi ya nuna mana ranar."


A sauk'ak'e ya amsa da "Ameen." Jim ya d'anyi kafin yace "Hajia ni zan wuce gida."


Mik'ewa dan ta fahimci so yake ta mik'e kafin yayi tsaye a kan ta shi ma, a hankali ya mik'e sukayi sallama a mutumce tana fad'in "A gaishe min da mazajen kwabon nan."


Murmushi yayi yana amsawa da zasu ji ya fice kamar yace "Wayyo Allah." Hajia ta umarceshi ya siyawa Ryam waya, me zatayi da ita? Su wa zatayi mu'amula dasu? Ko dai ma ita ta ziga Hajia kan a siya mata wayar? Da tunane tunanen nan ya isa gida.






*Saminu*




"Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un!" Abinda ta fad'a kenan sakamakon ganin Saminu zigidir babu kaya a jikinshi da wayarta a hannunshi yana kallon hoton Mimi wanda sukayi ta d'auka ranar kamu, yana kallonta yana ta lailaya dokinshi a dole yake son biyan buk'atarshi daga kallonta, juyawa tayi hankali a watse zata fita, da gudu ya biyota ba tare da jin nauyin jikinshi ba yana d'aura towel d'in shi yana kiran "Maimuna, Maimuna tsaya kiji."


Juyowa tayi a hassale ta kalleshi tace "Me zan ji? Wannan wace irin rayuwa ce? Me kake aikatawa haka dan Allah?"


Fashewa tayi da kuka hankali tashe cikin son rarrashi ya rik'o hannunta, da k'arfi ta fizge tana fad'in "Karka k'ara tab'ani."


Da alamar rarrashi yace "Naji to shikenan, amma dan Allah ki saurareni, Maimuna ba abinda kike tunani bane, wallahi..."


Sai kuma ya rasa me zai fad'a, sake juyawa tayi ya yi saurin shan gabanta yace "Ina zakije Maimuna? Dan Allah ki rufa min asiri, na yarda nayi laifi ki yafe min kinji."


Cikin sako hawaye tana kallon fuskarshi tace "Dama kana sonta ne? Ko kuma dai gaske ne abinda nake ji a gari a game da kai na neman mata?"


Da sauri ya girgiza kai yace "Ko d'aya Maimuna, wannan jita-jita ne na mutane karki yarda, Mimi kuma kamar 'ya ko k'anwa take a garemu ai, ban tab'a jin haka a kan ta ba."


Cikin d'aga murya tace "To me yasa kake kallonta kana son dole sai kaji dad'i ta haka? Fuskarta ce ke birgeka ko kuma albarkatun jikin da Allah ya hore mata?"


Sassauta murya yayi yace "Ba haka bane, Maimuna ina da buk'ata ne kuma ke naga kina saurin gajiya dani, bana so na zama mai takura miki shiyasa ban nemeki ba."


Tsareshi tayi da ido tana kallon fuskarshi, ta jima haka kafin ta sauke numfashi tace "Alhaji zan daina maka k'orafin gajiya idan ka min alk'awarin ba zaka sake kula mata a waje ba."


Da sauri jiki na rawa yace "Na daina, dama kuma bana yi wallahi, yanzu muje to."


A sanyaye ta bi bayanshi suka koma d'akin, d'auke wayar yayi ya aje gefe tare da kwantar da ita akan gadon, saidai tsaf abinda bata sani ba yana saduwa da ita ne amma kuma a idonshi Mimi yake gani, zuciyarshi ta gama haska mishi ita tare da k'awata mishi ita, musamman idan ya tuna kwancin nan nata a asibiti, yanda nonuwanta sukayi carrr daga sama kuma yake iya hangen matashiyarsu jajir dashi, ga s'uwawunta da suka kwanta akan gadon su ma sosai. Da haka har ya samu biyan buk'atarshi saidai babu gamsuwa dan hankalinshi a wani irin yake.






*Ahalin Mimi*




Aje abincin tayi gabanshi tare da zama gefenshi tace "Malam gashi."


D'an zabura yayi ya kalleta da alamar nisa yayi a tunani, Yaseen da Amir da suke gefensu ne suka kalleshi Amir na fad'in "Abba kaga yau ma mama shinkafa ta dafa mana har da nama."


Kallonshi yayi yana dariya yace "Da gaske? To ka k'oshi dai ko?"


Da dariya shi ma yace "E, Abba."


Murmushi yayi tare da jawo kwanon gabanshi zai fara cin abincin, da sauri Mama ta mik'e ta koma gefe kusa da k'ofar shiga ban d'aki, durk'usawa tayi ta shiga kwaranya amai, mik'ewa yayi hankali ya tashe ya k'arasa gareta yana fad'in "Subhanallah, uwar uwata lafiya? Baki da lafiya ne dama?"


Kakarin aman ta take yi bata kulashi ba, saida ta gama ya bata ruwa ta kurkure baki, mik'ewa tayi ta zauna kan tabarbar tana dafe kanta dake ciwo, gabanta ya zauna yana fad'in "Rabi'atu, baki lafiya dama? Me yake damunki?"


A hankali cikin muryar galabaita tace "Ba komai, ba wani abu bane."


Da kulawa yace "To ko gajiyar bikin nan ce?"


Da sauri tace "E ita ce."


Yanda ta bashi amsar ya sa mishi shakku, kallon tuhuma ya mata yace "Uwar uwata, ko dai Amir zaki wa k'ane?"


Da sauri ta kalleshi tana rufe baki tace "Kai." Sai kuma ta kalli su Yaseen, su ma su suke kallo, cike da kunya ta mik'e ta shige d'aki, dariya yayi tare da bin bayanta ya sameta zaune, kusanta ya zauna yana fad'in "Masha'Allah Rabi'a, nagode miki kinji, hak'ik'a wannan abun alkairi ne da farin ciki, Allah ya rabaki da abinda ke cikinki lafiya."


Sunkuyar da kai tayi tace "Malam kunya nake ji wallahi, mun aurar da 'ya kamata yayi ace mun aje wannan gefe yanzu."


Da mamaki ya kalleta yace "Iyeeeh! Kaji min matar nan, me zamu aje gefe d'in? Haramun muka aikata?"


Turo baki tayi ta sake yin k'asa da kanta, mik'ewa yayi yace "Uwar uwata fito ki ci abinci kinji, bayan wannan ma idan da wani rabon ni zan antayo dashi zuwa duniya."


Baki wangale ta kalleshi tace "Inna lillahi! Rashin kunya."


Juyowa yayi ya nunota da yatsa yace "Ke Rabi fita idona in rufe, na lura take-taken iya shegenki ne duk uwata ta d'auka, har take kallona ni da sheikh take fad'a mana tsofaffi."


Dariya Mama tayi ta sunkuyar da kanta, fita yayi ya zauna ya fara ci abincin cike da farin ciki a zuciyarshi, Mama kuma bata sake fita ba a k'arshe ma Yaseen da kansu sukayi shinfid'a suka taka kujera suka d'aura gidan sauro.






*Mim-Sheikh*




Da yake ba mai son zama da hijabi bace yanzu ma haka ta fito daga ita sai riga da siket d'inta na leshe, simple d'inki ne mai rap-rap amma dake tana da jiki sai ya mata wani irin kyau ya zauna a jikinta, gashinta data d'aure tayi irin d'aurin daya fi birgeta wanda tsakiyar gashin ke fitowa ta zauna a gadon bayanka. Duk da ta hangeshi amma bai dameta ba, k'arasowa tayi a sanyaye tana furta "Assalama alaikum."


Da fara'a Hajia ta amsa da "Wa'alaiki salam, takwarata kin tashi?"


Da ladabi ta zauna k'asa kusan k'afarta tace "Na tashi, ina kwana?"


"Lafiya lau, ya jikin naki? Da sauk'i ko?"


Da fara'a ta amsa "Da sauk'i sosai." A hankali ta d'aga idonta ta kalleshi, karaf idonsu suka had'e dan kallonta yake a lokacin ganin wani wata arniyar shiga da tayi, da sauri ya janye na shi idon yana fad'in "Astagfirullah wa'atubu ilaikh."


Sunkuyar da kan shi yayi har sanda siririyar muryarta ta dakeshi tana fad'in "Ina kwana malam?"


Da sauri Hajia ta kalleta tana murmushi, saidai bata ga laifinta ba dan bata san abinda yake so ba da wanda baya so, kallon sheikh tayi da a lokacin ya d'ago matsakaitan idonshi ya zuba mata harara yace "Ban ganshi ba nima, kun had'u dashi ne?"


Kallonshi tayi sai kawai tayi mar-mar-mar da ido tace "Allah huci zuciyar gafarta."


Da sauri Hajia ta gumtse dariyaarta dan ta fahimci wata yar tsama ce ke numen kunno kai tsakanin d'a kuma sirikinta da sabuwar amaryar ta shi, kwalin wayar dake gefenshi ya d'auka ya jefo mata sai a cinyarta, da sauri ta kalleshi sai kuma ta d'auki kwalin tana dubawa, a zuciyarta ta furta "Samsung galaxy."


Muryarshi ta ji a d'aure yana fad'in "Hajia tasa na siya miki waya, ki kula ki kuma san abinda zakiyi da ita, wallahi na kamaki da wayar nan kina abinda bai dace ba jikinki zai fad'a miki."


Kallonshi tayi a raunane tace "Amma malam ai ka ce baka dukan mutum, ni fa banaa son duka wallahi."


Bud'e baki yayi da jinjina rashin kunyar Ryam, gyara zama yayi ya nunata da yatsa yace "Ki jaraba yin abinda zan dokeki ki gani, ke sai na d'aureki kafin zan sa a zane min jikinki da tsumagiya."


Galala tayi sai kuma ta kalli Hajia ta sunkuyar da kanta, cikin muryar son yin kuka tace "Ai Hajia ta ce ni amanarta ce, babu wanda zai dakeni ta k'yale mutum."


A d'an hassale yace "Ke..." Sai kuma yayi saurin kallon Hajia, jinjina kai yayi irin zamu had'u d'in nan, Hajia dake ta son kecewa da dariya rufe baki tayi, yau kam tana ganin ikon Allah, ko abokan wasa fa yanzu sun ajiye wasar gefe guda basa yin ta da sheikh, amma kaga yarinya yana fad'a tana fad'a, shi kuma har da wani biye mata wai kamar ba wannan mai taka tsantsan d'in ba?


A hankali Mimi ta yunk'ara zata tashi tace "Hajia ki masa godiya."


Rintse ido yayi yana addu'ar Hajia ta matsa daga gurin nan ya cabki wuyan yarinyar can, kai kutmelesi inji yan duniya, shi wai ake wa wannan iskancin? Da kallo Hajia ta bita tana jin wata irin k'aunar yarinyar na sake ratsa zuciyarta, dan abunda tayi yanzu sai ya nuna ba yarinta bace tayi ba kuma k'uruciya bace ko raini, aji ne, ajinta ta ja da kyau, dan har yanzu ita dashi basu keb'e ba bare su zama d'aya ta yanda zata zama mai arha a gareshi. Maido kallonta tayi ga sheikh da niyyar mishi magana sai taga ya bi Mimi da harara, saidai wani abu data k'ara fahimta a cikin hararar akwai kallon birgewa duk da shi baisan yayi ba, amma dai tabbas yanayin fuskarshi yanayi ne na shagala da kuma kallon birgewa da d'aukar hankali, idonshi ne kawai ke hararen suma gaba kad'an akalar hararan zata canza ba tare da sanin mai su ba.


Juyawa tayi ta sake kallon Mimi dake daf da shiga d'akinta tace "Mimi."


Juyowa tayi tace "Na'am Hajia." Dawowa tayi a nutse a sanda sheikh ya d'auke idonshi daga kallonta yana fad'in "A'uzu billahi mina shaid'ani rajim."


Tana zuwa kan tebur ta nuna mata tace "Je ki fara cin abinci ina zuwa yanzu."


Jinjina kai tayi tare da nufa kan teburin, sosai ya sunkuyar da kanshi yana son dole yafi k'arfin zuciyarshi ba sai ya kalleta ba, kallonshi Hajia tayi tace "Da wani abu da kake buk'ata sheikh?"


Girgiza kai yayi a hankali yana jin wani irin mutuwar jiki da kasala a lokaci d'aya, jinjina kai tayi ta mik'e tace "To muje ka ci abinci?"


Girgiza kai ya sake yi da k'yar ya iya cewa "Na k'oshi."


Jinjina kai tayi ta nufi teburin tana fad'in "Bari na ci abinci ni, kasan uclerta bata jurar yunwa."


Jinjina kai yayi alamar gamsuwa, so yake ya mik'e amma kallon fitinanniyar yarinyar can ya canza mishi yanayinshi, bayan kasalar da yake ji na sauko mishi har da wani shauk'i yake ji, a hankali ya d'an gyara zamanshi cikin dubara ya saki 'yar mik'a a zuciyarshi yana fad'in "La'ilaha ilallah Muhammadu Rasulullahi sallalahu alaihi wa sallam."


Mik'ewa yayi ya d'an k'arasa kusa da su, yanda take tsaye tana zubawa Hajia abinci sai yaji yana sha'awar k'are mata kallo, yanda ya ganta yar dagwai dagwai d'in nan ga kayan nan da suka mata kyau, a hankali ya kalli kwabar madubin dake geffen shi saidai Hajia ta bawa kwabar baya ne, tsaf ya hangota a ciki tana zuba abinci, take ya jefawa kanshi tambayar "Wai me yasa ta fitsare ne tun a waje?"


Haushin wannan tambayar da jin wani mahaukacin kishi yasa shi kallon Hajia yace "Sai anjima." Da sauri ya shiga takawa ya bar falon, Hajia da kallo da mamaki ta bishi har ya fita a gidan ma.








*Alhamdulillah*
7/22/21, 8:57 PM - Ummi Tandama😇: 👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩�����
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩����👨👩�����


*NA*




_SAMIRA HAROUNA_




*SADAUKARWA*



_GA DUKA_


*'YAN AMANA TA*




💫� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_�


� *[ T.M.N.A]* � 📖🖊�


https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/


_Bismillahir rahamanir rahim_




Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads