Showing 21001 words to 24000 words out of 27098 words
Chapter 8 - SANADIN BESTY Complete Hausa Novels by hubby .txt
yi cike da jin daɗi, Allah-Allah ta ke yi ya jefa ƙwallo a raga ta ji ya yake, shima gaba ɗaya ya gigice a haka ya rabata da komai na jikin ta ya ci-gaba da ma ta wasanni masu tada hankali, ganin ba za ta iya jurewa ba ya sa ta fara mayar mai da martani, bai ma kula da abin da ta ke mai ba saboda gaba ɗaya ya fice a hayyacin shi, ga wani soyayyarta da ke ƙara ƙaruwa, a haka ya samu ya shige ta, sai dai ya tsaya jimm jin ƙofar a buɗe, ko da an yi wasu kwaskwarima hakan ba zai hana shi gane macen da aka taɓa buɗewa ba, wani nauyi ya ji a zuciyar shi, ji ya ke kamar ya fasa ihu amma ina ya kasa ƙarasawa, haka ya zare jikin shi, kamo shi ta ƙara yi suka haɗa ido, nan da nan- ya ji komai ya gudu a ƙwaƙwalwarsa, ci gaba ya yi da sarrafa ta yadda ya ke so ita kuma sai jin daɗi ta ke yi na ganin komai ya tafi yadda ta tsara..
Taimakon gaggawa likitan ya fara ba ma Fadeelah, sai da suka kwashe tsawon awa ɗaya sannan aka samu numfashinta ya dawo, ban da kuka ba abin da Anty ta ke yi tana faɗin:
"Shikenan Fadeelah kin cuce ni, yanzu sakayyar da za ki min kenan? Duk irin yadda na ke faɗi-tashi a kanki amma sai da kika ɗauko mana abin kunya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Allah na tuba ", haka Anty ta ke ta maimaitawa cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya, ita kaɗai ta san me ta ke ji a cikin zuciyarta, da ƙyar wata nurse ta ja ta gefe ta rarrashe ta sannan ta tsagaita da kukan, jira kawai take yi Fadeelah ta farka ta faɗa ma ta wanda ya aikata ma ta wannan aika-aikar, ko da ya ke ai ba laifin shi ba ne, da ba ta ba da kanta ba ai hakan ba za ta faru ba, ga shi yanzu ta ja musu masifa suna zaman-zaman su cikin rufin asiri. Sai da Fadeelah ta kwashe awanni wajen biyar sannan ta farka, cikin firgici da ihu, bubbuga gadon take yi tana miƙewa jin hakan ya sa Anty da ke bakin ƙofa ƙarasowa da sauri, tana shiga ta tarar da ita a wannan yanayin tsawa ta daka ma ta tare da faɗin:
"Dalla ki mana shiru munafuka, koma mene ne ai ke kika jawo, tun da kin zama ballagaza jaka, wallahi Fadeelah kin cuce mu", ta ƙarasa maganar kuka na kufce ma ta, ita ma Fadeelah kukan take yi ta na cewa:
"Tabbas Anty na cuci rayuwata, Adnan ya cuce ni, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun wannan wace irin masifa ce?" Matsowa Anty ta yi gadan-gadan kamar zata dake ta ko me ta tuna kuma sai ta fasa, juya wa ta yi ta tsaya a dai-dai saitin window hawaye na zubowa a idanunta, yadda take ji a zuciyarta ko ta daki Fadeelah ba hucewa za ta yi ba, babban abin takaici ma wai wannan ɗan iskan yaron mai ido a tsakar ka, yaron da ba ya ganin mutuncin mutane, ita kam ina zata saka rayuwarta? Haka dai ta yi ta saƙe-saƙe a cikin zuciyarta, ganin ta rasa mafita ya sa ko kallon inda Fadeelah take kuka ba ta yi ba ta fice gaba ɗaya a ɗakin.
Waya ta ɗauka ta kira mijinta kasancewar ba mazauni ba ne ta faɗa masa abin da ya faru, cikin kuka take faɗin:
"Yaya Fadeelah ta cuce mu, ta kasa riƙe mutuncinta, ciki fa ta yi, ina zamu kai wannan abin kunyan? Ni wallahi na rasa yadda zan yi ma".
Daga ɓangaren shi shiru ya yi sai da ta gama bayani sannan ya ce:
"Ki yi haƙuri ki daina kuka, ƙaddara ce amma kuma duk da ganganci, ki kwantar da hankalin ki insha'Allah gobe ko jibi zan taso sai mu san yadda za a yi, amma kafin nan dan Allah kar ki ce ma ta komai", sai da ya tabbatar da hankalin ta ya kwanta sannan ya ma ta sallama ya ajiye wayar cike da mamakin abin da ƙanwar matar ta shi ta aikata, yana ma ta kallon mai wayo ashe shashasha ce...
Kwanan Fadeelah uku a asibiti a ka sallame ta a ɗan wannan lokacin jikin na ta ya yi kyau sai dai damuwa da ya ramar da ita, tsakanin ta da Anty kuwa sai dai kallo don ko ta ma ta magana ba amsawa ta ke ba, a haka dai suka tattara suka koma gida, kuma har a lokacin mijin Anty bai dawo ba, rayuwa ta ma Fadeelah tsauri, ko kaɗan Anty ba ta raga ma ta...
Ango Adnan kam sai zuba soyayya a ke yi da Amarya Zeenat, ba ta bari ya fita ko nan da can, gaba ɗaya gajiyar da shi take amma ya kasa ce ma ta komai, tsabar tsanar ta ce a kwance a ƙasan ranshi amma bakinsa na mai nauyin furta ma ta, ga shi bai isa ya sa ta abu ta yi ba sai dai ta balbale shi da masifa ta na faɗin ita fa ba 'yar aiki ba ce, ko girki ba ta yi sai dai kullum ya siyo musu, ga ƙazanta kamar me, cikin wata ɗaya da aure Adnan ya rame, sai idanu, kana ganin shi ka ga mai damuwa amma ba zai iya furta wa ba, wani sabon abu ma da Zeenat ta tsira shine fita da ta ke yi kullum ba tare da izinin shi ba, ga shi bai isa ya ma ta magana ba sai ta hau shi da masifa wai yana takura ma ta, tsakanin shi da ita yanzu sai idanu...
Noor na isa asibiti ya kira Abba ya sheda mai abin da ya faru sannan ya ƙarasa ya kira nurses, ba ɓata lokaci aka karɓe su kasancewar asibitin mahaifinsa ne, cikin ƙanƙanin lokaci aka ba su taimakon gaggawa, Besty kam ya jigata sosai kasancewar ya bugu da gefen kujera ga kuma karaya a hannun shi na dama, naɗe wajen aka yi da bandeji bayan an gyara karayar hannun da ƙyar, sannan aka mai allura ya koma baccin wahala, ita kuwa Raudah allura kaɗai aka ma ta kasancewar suma kaɗai ta yi, Noor ya na ƙofar ɗakin da Raudah ta ke a tsaye, haushin ta yake ji sosai, gani yake kamar wani abu ya shiga tsakanin ta da Dee, sam ya ji ba ya ƙaunar ganin ta, ana cikin haka Abba da Mommy suka ƙaraso asibitin a tare, don Noor na gama faɗa wa Abba a lokacin ya na kasuwa shi ma ya kira Mommy hankali tashe, a bakin titi Mommy ta jira shi ya zo ya ɗauke ta suka wuce cike da fargaba, ran Abba ba ƙaramin ɓaci ya yi ba, wato Raudah ba ta jin maganar shi kenan, duk faɗan da ya ma ta a banza ta yi auren ma ba ta rabu da wannan tantirin yaron ba, haka su ka tsaya cirko cirko a asibitin ba wanda yake iya magana, sai bayan isha'i sannan Raudah ta farka, ƙin shiga ɗakin Noor ya yi sai mommy ce ta shiga a lokacin Abba bai dawo daga masallaci ba.
Ko da Mommy ta shiga ta tarar da Raudah a kwance idanunta biyu amma hawaye na tsiyaya a fuskarta, ko a mafarki ba ta taɓa zaton Noor zai iya dukan ta ba, lallai ta san ta kai shi maƙura, tsinkar muryar Mommy ta yi ta na cewa:
"Ai ba ki ma yi kuka ba, bari Abbanku ya shigo za ki faɗa mana uban me wannan yaron ya je yi gidanki na aure",
Ƙara sautin kukan Raudah ta yi don ta tabbatar yau kashinta ya bushe, babu abin da zai hana Abba dukan ta, ita babbar damuwar ta ma Noor ganin ba ta gan shi a ɗakin ba, tunowa ta yi da abin da ya faru sai ta ji duk duniya ba wanda ta tsana kamar Dee don ko sunan shi sai ta ji ya ma ta ɗaci, yau a kan shi mijinta da take matuƙar so kuma yake son ta, mai haƙuri da kawaici ya sa hannu ya dake ta? Ko da ya ke ba ta laifinsa ba ne, don ko ita ce abin da za ta yi kenan ko zuciyarta za ta ji sanyi, babbar damuwarta ma shi ne kallon da Noor zai ma ta, ba ta da wata mafita, kuma duk abin da za ta faɗa ba lallai su yarda da ita ba, ita yanzu babbar matsalar ta ma bai wuce Noor ba ta ga har yanzu bai shigo ba, numfashi mai ƙarfi ta ƙara ja tana mai kallon Mommy, ganin Mommy ta ƙi kallon ta ne ya sa ta rufe ido tamkar mai bacci.
Ko da Besty ya farka ba wanda ya zo ya duba shi sai nurses da ke sintiri, kanshi har yanzu bai daina sara mai ba, ya yi nadamar kasancewar shi Besty, a ranshi yake faɗin "me ma ya kai ni gidanki Raudah? Ga shi nan na ja ma kaina" ganin ya kasa ɗaga hannun shi ne ya duba ya ga hannu a nannaɗe hakan ya tabbatar mai da har karya shi Noor ya yi, nurse ce ta shigo ta ƙara duba shi sannan ta ƙara mai allura, roƙon ta ya yi ta kira mai mahaifiyar shi, bayan ta kira ne ya shaida ma ta yana asibiti, ba shiri ta tashi ta yafa gyale ta taho wajen Dee kasancewar shi ne yaron su ɗaya tal da Allah ya ba su, ko da ta iso ta ga yadda jikin nashi ya yi bayan ya labarta ma ta abin da ya faru faɗa ta hau shi da shi tana faɗin:
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun!! Kamaludeeni yaushe ka zama kwarto?" Ta tambaya cike da mamaki, da ƙyar Dee ya iya ɗago idanunsa da suka kumbura saboda yadda kan shi ya ke mai ciwo ya ce:
"Haba Mama kwarto kuma? Kawai ƙawata ce fa shi ne na je na gan ta" ya faɗa yana juyar da kan shi gefe domin ba ma ya son ƙara tunawa, faɗa sosai Mama ta dinga mai kamar ta aro baki sannan ta fita waje ta kira mahaifinsa ta sanar da shi, shima ba shiri ya bar aikin ginin da ya ke yi ya taho asibitin, ko da mahaifiyar Dee ta labarta mai abin da ya faru tashi ya yi ya fice daga ɗakin yana cewa "Allah shi ƙara" tun da shi ya ja wa kan shi.
A haka suka kwashe tsahon kwana uku a asibitin kuma har yau Noor bai shiga ya ga jikin Raudah ba, Abba dai ya duba ta sau biyu amma har yanzu bai ce komai ba, babu wanda ya san tana asibiti a cikin familynsu saboda Abba ya ce wanann labarin ba abin sanarwa ba ne, Mommy na kula da rashin shigan Noor duba Raudah amma ba ta ce mai komai ba, kullum a asibitin yake wuni kuma duk abin da ake buƙata shi yake yi, shima a ɓangaren 'yan gidansu bai sanar da kowa ba, kullum Raudah sai ta yi kuka tana ce ma Mommy dan Allah ta kira ma ta Noor amma ko kallo ba ta ishi Mommy ba sai dai ta bata amsa da cewa "ai ke kika ja ma kanki ba wani ba" .
A zaman da suka yi a asibitin ne mahaifin Raudah suka haɗu da mahaifin Dee har suka tattauna sosai, ɗan zaman da suka yi har sun saba tare da samar wa da kan su mafita, mahaifiyar Dee ce ma ta lura da shige da ficen su Abba a asibitin shi ne ta tambayi wata nurse, yadda nurse din ta ma ta kwatance cewa tare wani ya kawo su da wata mace hakan ya tabbatar ma ta da ita ce matar da Dee ya je gidanta, shi ya sa ta faɗa wa mahaifinsa shi ne ya nemi Abba suka yi magana kuma alhamdulillah domin kuwa sun fahimci juna yadda ya kamata, mahaifin Dee ya so su haɗu da, shine Abba ya sanar wa da Noor din amma da ke har yanzu bai huce ba, ya na ganin mahaifin Dee sai ya canza waje .
Ko da aka sallami su Raudah gidansu Abba ya mayar da ita da kan shi, ta ji sauƙi ba laifi, a ranar shi ma Dee mahaifinsa ya ce a sallame su saboda sun gaji da zaman asibitin shi dama karayar da ya yi ne da buguwar da ya yi a kai ba su warke ba wannan kuma sai a hankali, Abba ne ya biya ma Dee kuɗin asibiti saboda Noor ƙin biya ya yi na matarsa kaɗai ya biya ya juya ya bar asibitin, shi kaɗai ya san yadda yake ji a zuciyarsa. Yana son ganin Raudah amma fushin da yake yi da ita ba zai bar shi ya iya ganin ta ba...
Bayan kwana biyu da dawowar su iyayen Dee suka zo tare da Dee gidan domin yin zama na musamman a tsakanin su, da ƙyar Noor ya yarda ya zo don ma yana jin kunyar Abba ne, a babban falon Abba suka zauna, bayan zaman su da kamar minti goma sai ga Raudah ta shigo sanye da farin hijabi har ƙasa, suna haɗa ido da Noor gabanta ya faɗi ganin yadda ya rame sosai kamar ba shi ba, sauke idanunwan ta tayi ƙasa tana tafiya a hankali har ta kai gefen da Noor ya ke ta zauna a ɗan gaba da shi, juyawa ta yi ta hango Dee a ƙasa a gefen ƙafar mahaifin shi dama ta san iyayen shi domin yana saka su a status, kallo ɗaya Noor ya ma ta ya ɗauke kai kamar bai ganta ba, haka kawai sai ya dinga jin haushin ta, Uncle Babangida ne ya buɗe taro da addu'a sannan ya fara da musu nasiha tare da nunar musu yadda addini ya tsara macen da ya kamata ka yi mu'amala da ita da kuma namijin da ya kamata ka yi mu'amala, da haramcin kula wadda ba muharramarka ba da kuma wanda ba muharraminki ba, kuka kawai Raudah take yi saboda jin yadda Allah ya tanadar ma da masu irin halayen ta azaba amma ta biye wa son zuciya, jikin Dee ya mutu murus kuma tun ba yau ba ya yi nadamar abin da ya yi, Abba ne ya katse Uncle Babangida da faɗin:
" Raudah kin ba ni kunya, tun da ki ka taso a gidan nan har kika mallaki hankalin kan ki kin taɓa ganin wani wanda ba ki sani ba ya zo da sunan shi abokin mahaifiyarki ne?"
Girgiza kai Raudah ta yi ba halin magana Abba ya ci-gaba da cewa:
"Ko kin taɓa gani na da wata da sunan ita ɗin ƙawata ce?" Nan ma dai girgiza kai ta yi sannan ya ce:
"Oh to sai ke tsabar shashasha ce ke, ba ki san inda yake miki ciwo ba shi ne za ki biyewa son zuciya da wata shegantaka da sunan wayewa wai Besty ko? To ai gashi nan kina nema ki ɓalle auren ki da hannunki, kuma wallahi wallahi wallahi kin ji rantsuwar musulmi in dai Nuruddeen ya rabu da ke to sai dai wani gidan ba nawa ba". Yana gama faɗar haka ya ja bakinsa ya yi shiru ai Raudah na jin kalmar rabuwa ta ƙara fashewa da kuka ba wanda ya ce mata komai sai da tayi mai isar ta sannan ta yi shiru, mahaifin Dee ya ɗora da faɗin:
" Ni na rasa me zan ce ma wallahi, Alhaji, Hajiya dan Allah kuyi haƙuri dama shi ya sa na ce gwara mu taru mu yi magana ta fahimta, waɗannan yara sam ba su kyauta ba sun yi rashin hankali kuma wannan ba tarbiyyar musulmi ba ne kuma ni wallahi abin da mijin yarinyar nan ya yi ya min daidai domin kuwa ko ni ne zan yi fiye da haka ma" sai ya juya wajen da Dee ya ke ya ce " kai kuma na dawo gare ka mutumin banza mutumin wofi, wallahi wallahi idan baka fita a harkar 'yar mutane ba sai ranka ya ɓaci kai kasan karon mu da kai ai, ba kai ba ita na faɗa maka, ko da wasa na sake jin makamanciyar hakan kai ko ba a kan ta ba ko a kan wata ce na haramta maka zama Besty idan ka ƙi kuwa za ka gane ba ka da wayo".
Share hawaye Dee ya yi sannan ya ce " don Allah don Annabi ku yafe min insha'Allah ba zan sake ba tun daga ranar da abin ya faru na yi nadama kuma insha'Allah ko a kan wata ma ba zan ƙara zama Besty ba domin a "SANADIN BESTY" aka karya min hannuna, hannun da har yanzu ya ki ɗauruwa", ya ƙarasa zancen hawaye na ƙara zubo mishi, rarrafawa ya yi ya je wajen Noor ya roƙe shi gafara a taƙaice, ya amsa mai sannan ya nemi yafiyar Raudah da iyayenta, shi da zama Besty har abada, haka aka musu katangar ƙarfe mai ƙarfi tare da gindaya musu sharuɗa na musamman, sannan ita ma Raudah ta nemi yafiyar iyayen ta da mijinta saboda ta san ta kai su bango tun da har suka iya jure yin fushi da ita, tana hango fushin da Noor ya ke yi a cikin ƙwayar idanunsa amma ya ta iya? Ba ta ankara ba ta ga ba kowa a ɗakin daga ita sai Noor ashe duk sun watse, gefen Noor ta je ta kamo hannunsa tana kuka a lokaci guda ta na cewa:
"Ka yi haƙuri mijina sharrin shaiɗan ne ba zan sake ba, Please forgive me" kallon ta ya yi da rinannnun idanunsa ya ce:
"Why Raudah? Why? Me na miki haka da za ki saka min da wannan? Na dawo gida na na ganku da wani, wani fa Raudah?" Fashewa Raudah ta yi da matsanancin kuka ganin ba zai iya jure saurarar kukan nata ba ya sa shi ficewa daga parlour'n ya bar ta a wajen...
Bayan dawowar mijin Anty da kwana biyu suka tusa Fadeelah a gaba zuwa gidansu Adnan da ke ya taɓa kai ta gidan ta jira shi ya ɗauko abu ya fito, korar kare iyayensa suka musu