Showing 39001 words to 42000 words out of 119225 words
Chapter 14 - TSUTSAR NAMA BOOK 2 By Bilyn Abdul.txt
halin nashi ba. Lallai sai a jinjina masa. Ganin yanda duk suka maida hankalinsu a kansa nasa ƙafa na taɗe Azizat dake ta leƙensa kamar mai son binsa. Razananniyar ƙarar data fasa ya saka kowa zabura sukayo kanta.
Da wannan damar Mama Balki taja hannuna da sauri hankalinta tashe muka sulale muka fice. Ashe ita taga abinda nayi, suko sai suke tambayar miya faru? Yaya akai ta faɗi. Oho mudai tuni mun ware bamu san yanda suka ƙare ba kuma....
🤣🤣ALLAH ya shiryeki Sam-G.
❤️★❤️★❤️
“Gwaggo maganar auren nan dama nake son mu tattauna kafin ki wuce. Dan ina son ayi komai a gaggauce cikin watan nan”.
Cike da ɗunbin farin ciki Gwaggo Gudidi ke kallon Abba dake maganar, ta saki dariya tare da yin guɗa. “Kai kai da ace na iya ghuɗa babu abinda zai hanani tsallarata sama har sai duk ƴan anguwa sunji Imamu. Ka daɗe baka sakani a farin ciki irin yau ba. ALLAH yay maka albarka. Amma ince dai ƴar mutunci ka sama mana ba irin wannan matar taka ba dan bana son a sake yin jifar gaffiyar ɓaidu”.
Kai Abba ya girgiza yana ɗan murmushi, “A'a Gwaggo in sha ALLAHU sam ba halinsu ɗaya ba. Yarinyar da suka doka ɗin ce dama.”
“Kai kai to Masha ALLAH. Aiko kayi ƙyan kai, dan hakan da zakayi shine babban murtani da zaka maidawa matarka tasan ka haifu cikin uwa da uba. Amma kuma ai naji yaran na faɗin ta gudu tun a ranar da abin ya faru? Ko kasan inda take ne?”.
“A'a Gwaggo ban sani ba. Amma dai ta sanar min da garinsu. Nasan kuma insha ALLAHU can ɗin zata nufa tunda Alhaji Sadisu ya bincika daga inda Jalilahn ta ɗakkota ance bata koma can ba. Dan haka nake son muyi azamar bin bayanta tun kafin abin yayi nisa”.
“Eh to hakan ma dabara ce ai. ALLAH ya bada sa'a da nasara. Yaushe zaku je ɗin?”.
“Da dai gobe idan ALLAH ya kaimu ne. Sai shi Musaddiq ya jamu dan ni bazan iya tuƙi ba. Alhaji Sadisu ko baida jimirin yin tuƙi a doguwar tafiya sam”.
Ɗan jimm Gwaggo tayi alamar tunani, dan in bata manta ba Musaddiq ya sanar mata gobe ne zai je gwaji da akace za'a musu a inda aka ɗaukesa aiki. Da ɗan sauri ta girgiza kanta. “A'a inaga shi Jafaru sai ya jaku kawai dan yasan ƴan tumaki sosai tunda shima matarsa ƴar wajen garin ce. Kaga ko ai faɗuwa tazo dai-dai da zama ba sai anta faɗi tashin tambaya ba”.
Cikin nuna farin ciki da gamsuwa Abba ya shiga tabbatar mata da hakan yayi, ya ɗora da godiya. A take kuma babu ɓata lokaci yay kiran Jafaru ɗin. (Jafaru shine ɗa na biyu a wajen Gwaggo Gudidi. Kusan sa'anni suke ma da Abba dan komai na rayuwarsu tare sukayi. A dalilin Mom tarayyar tasu ta samu rauni. Dan yanda take nuna bata ƙaunar ƴan uwansa su raɓesa duk wanda yazo sai ya tafi da tabon rashin mutuncinta yasa Jafaru janyewa daga jikin Abba. Saboda akwai wani zuwa da yayi Mom ta cimasa mutunci harda ƙwallarsa. Daga lokacin ya tattara Abba ya ajiye gefe sai dai su gaisa sama-sama ta waya ko idan wata sabgar ta haɗasu ta dangi ko in sun haɗu a gidan Gwaggon. Abin na damun Gwaggo amma ta gagara sasantasu, sau yanzu ga dama ta samu kuma)....
✨💫✨💫✨💫
Ko kaɗan Mama Balki batai min faɗa game da abinda naima Azizat ba. Sai ma Sosai yanda ta nuna tashin hankalinta ita da su Bahijja game da batun komawata aiki sashen Hajiya Mammah ya bani mamaki. Dan na sake fahimtar al'amarin babba ne. Duk da kuwa Bahijja ta ɗan bani labarinta a ƙaice ni banga wani abun tsoro tattare da ita ba, idan masifa ce na saba data Mom da ƴaƴanta ai. Sambatu suke sosai da nuna jimantawa har Mama Balki na faɗin na gudu kawai tun ma kafin komai ya faru. Zata saka mijinta ya taimaka min na fita a daren yau.
Murmushi na saki a hankali duk da kuwa nima ina jin shakkun al'amarin a zuciyata. Sai dai wani sashe na ƙarfafani dan koba komai zan samo labarai. Haka kawai kuma ina son sanin gaskiyar labarin tushen komai. Atake naga fuskokin masu dariya da nuna farin ciki a kaikaice a cikinsu na sauyawa a dalilin murmushin nawa. Nima sai kawai na basar da canja yanayina. Ƙwallar ƙarya nayi ƙoƙarin tarama idanuna. Tare da nuna tashin hankali ina mai roƙon Mama Balki data taimaka min na gudu ɗin... A bazata mukaji an saki tsaƙi, kusan mu dukanmu muka kalli mai tsakin. Ba kowa bace face aunty Kubra. Yanayin shock na gani a fuskar Mama Balki, da alama dai ta fahimci tayi ɓaranɓaramar sakin zancen gaban kowa. Sai dai bata iya cewa komai ba
Cike da taɓe baki Aunty Kubra ta cigaba da faɗin, “Mama ina baki shawarar ki rufama kanki asiri. Ke dai kinfi kowa sanin halin Hajiya Mammah a gidan nan. Sannan ita ɗin ba ita ta jama kanta ba. Banda kauɗi da rawar kai uwarwa ya kaita marin ƴar masu gida. Jarumta tafi wani a cikinmu da muke haƙurin shekara da shekaru da su ko mi? Kinga yanzu ai ya rage nata ta ajiye kauɗinta da iyayi gefe ta nemawa tsoffinta kuɗin cin tuwo cikin sallama. Idan ba hakaba wataran ba sashen Hajiya Mammah ba Sashen Hajiya Babba zasu kaifafa ko kuma da karnukan gidan nan wlhy zasu haɗata”. Daga haka ta miƙe tai ficewarta tana wani rausaya da girgiza jiki.
Shiru kowa ya gagara cewa komai, sai shashshekar kukana kawai kake ji. Kusan mintuna biyar Mama Balki tayi ƙarfin halin bama Bahijja umarnin tafiya dani ɗaki na kwanta. Babu musu Bahijja ta miƙe ta kama hannuna. Sai naga itama A'i ta miƙe fuskarta cike da tsantsar damuwa itama ya kama ɗayan hannuna....
Duk yanda naso rintsawa barci a wannan daren kasawa nayi. Dan komai ya tsaya min arai ne. Duk yanda nake jin rashin damuwa game da yin aiki a sashen Hajiya Mammah ɗin wani sashi na zuciyata na tsoratar dani da nuna min illar hakan, dan na fahimci matar bata da mutunci sosai. Dan duk mai hankali ya auna yanda kowa ke nuna damuwarsa akan batun zai sake tabbatar da bada wasan yara bane al'amarin. Ganin yanda zancen yaƙi barin raina sai kawai na tashi na ɗauro alwala na fara nafilfili. Har asuba ban runtsa ba sai da nayi salla..........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_
.......Ina idarwa na ɓingire a wajen sai barci. Ban tashi farkawa ba sai da A'i ta tasheni wai Hajiya Mammah na kira na. Yanda take maganar cikin nuna tsoro da damuwa ya sakani tsira mata ido. Sai dai bata bani damar mata tambaya ba ta juya sukuku ta fice tana faɗin, “Kiyi sauri ki shirya muje kar mu sake wani laifin kuma. Dan ga Mama Balki can tasha maruka akan guduwar da kukayi jiya da dare duk da ƙaryar kareki da tayi kan baki da lafiya ne shiyyasa”.
Sosai naji wani irin masifaffen ɓacin rai. A take ta bududdugin ta motsa (zuciya) na shiga taunar lips da ƙarfi-ƙarfi tamkar zan hudashi. Gaba ɗaya wata irin tsanar matar mai tsananin gaske ta shiga zuciyata. Yanzu dan ALLAH babbar mace kamar Mama Balki ce za'a mara wai. Kai wannan wane irin gidane haka na marasa tarbiyya da girmama mutane. Dan kawai mutum nada dukiya sai akace zai iya taka kowa a yanda yake. Kaicon wannan rayuwa mara fasali da rashin sanin daraja da kimar ɗan Adam.
A gurguje nayi wanka na shirya cikin Uniform ɗin da A'i ta ajiye min. Koda na fito a falo na sameta tsaye tana jirana. Kallon juna mukayi. Ta ɗan kafeni da kallo sai dai batace komai ba tayi gaba na bita a baya...
💞👉💞👉💞
“Alhamdullah su Abba sun isa ƴan tumaki lafiya. Tafiyar da Mom bata da masaniya a kanta, dan har yanzu Abba baya shiga harkarta. Ita kuma ta tada hankalinta sunata bibiyar teachers domin sabunta ayyuka akan Abban dan ta lura komai fa na neman canjawa. Kullum cikin ƙaryar fita take duk da kuwa yana gida yana jinya. Bai taɓa hanata ba, kamar yanda Gwaggo Gudidi bata taɓa tanka musu ba. Da tambaya da kwatance suka gano gidan su Halime da ƙyar kasancewar sun sami cikakken address wajen mai kawosu aikatau daga ƙauyen. Wadda da ƙyar suka samu ƙawar Mom ta sanar musu bayan sun danƙa mata kuɗaɗe. Tako kai su amma ta roƙi Abban da kar ya sanarma Mom ita ta faɗa, duk da kuwa ita bata san manufar Abban ba. Ya sanar mata ne kawai zasu bincika idan Halime taje gida kar a samu kuskure tayi wani wajen daban. Ta gamsu ɗari bisa ɗari dan tanama Abban kallon girmamawa duk da tasan aminiyarta ta daɗe da gamawa da shi. Koda yake itama ɗin ta gama da nata mijin ai duk da basu taɓa tarayya da Mom wajen zuwa gidan teachers ba. Kowa nayin al'amarinsa ne a bayan fage..
Sun ɗauki kusan mintuna talatin a gidan mai anguwa da sukai dabarar fara zuwa kafin Baba da aka aika kira ya ƙaraso. Tun shigowarsa Abba keta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, dan ko makaho ya laluba yasan shine mahaifin Halime saboda kama da sukeyi matuƙa tamkar yayi kaki ya ajiyeta. Sake gyara nutsuwa Abba yayi, hakan har ya saka Alhaji Sadisu sakin murmushi. Bayan Baba ya gaisa da mai anguwa ya juyi gasu ba. Kafin ma ya gaishesu su sun shiga gaida shi. Dan ko babu batun abinda ya kawosu zai girmesu gaskiya. Bayan an kammala gaggaisawar mai anguwa ya nunama baba su Abba.
“Malam Yusufa baƙine dama suke neman gidanka. Naso saka yaro ya rakasu sai suka buƙaci haɗuwa da kai anan shiyyasa na aika akayi kiranka”.
Da ɗan nuna alamun mamaki Baba ke kallon su Abba. Ganin yanda Abba ya duƙar da kansa Alhaji Jafaru ya fara magana a nutsensa. “Ni sunana Jafaru, wannan sai ƴan uwana Alhaji Sadisu da Alhaji Imam. Baba baka Sammu ba gaskiya. Wannan ɗan uwan nawa Alhaji Imam shine mai gidan da ƴarka Halimatu take zaune acan birni.....”
Sosai Baba ya waro idanu, tare da sakin salati ya ce, “Kai kai Masha ALLAH. Bawan ALLAH ashe baka rasuba Sa'adiyya duk ta kasa zaune ta kasa tsaye. Tunda ta iso garin nan kwana biyar kenan kullum bata da aikin daya wuce kuka. ALLAH mun gode maka”.
Murmushi Abba yayi cike da jin sanyi a ransa Halimensa ta damu da shi. Murya a sanyaye ya ce, “ALLAH kam shine abin godiya Baba. Nima kuma ina ƙara gode masa da ya zamto gida tayo ba wani wajen ba. Dan muna can hankalinmu duk a tashe da ƙyar aka samo wadda ta ɗauketa daga nan ta bamu address.”
Sosai Baba ya nuna jin daɗinsa da wannan kulawa. Fuskarsa washe da murmushi shima ya ce, “Ai dama duk tsanani Sa'adiyya bazata nufi ko ina ba sai gida. Nima Nagode sosai da wannan kulawa taku, lallai na yarda da gaske yarinyata tana a hannun mutanen kirki. ALLAH ya kiyaye gaba ya ƙara lafiya”.
A tare duk suka amsa da Amin. Kafin Alhaji Sadisu ya ɗora da bayani bayan sun ɗan yi jimm na wani lokaci. “Baba dan ALLAH idan bazaka damu ba muna neman wata alfarma ne”.
“Ku faɗi komi kuke buƙata a gareni kai tsaye in dai baifi ƙarfina ba zan muku shi in sha ALLAHU”.
Cike da jin daɗin furucin nasa Alhaji Sadisu ya cigaba da faɗin, “Muna neman alfarmar ka bamu auren Halimatu”.
Ba baba kawai ba hatta da mai anguwa sai da ya waro idanu sosai cikin nuna ƴar tsorata......
🌛🌟🌜
Kallo ɗaya nayima Mama Balki dake gurfane gaban Hajiya na ɗauke idanuna zuciyata na suya. Da ƙyar na iya control ɗin kaina nima na kai durƙushe. Latse-latsenta take a laptop tamkar batama san da zuwan namu ba. Gefenta Azizat ce kwance itama tana latsa wayar fuskarta mamaye da fara'a. Sai da ta mula dan kanta sannan ta ɗago bayan ta rufe laptop ɗin. Fuska a yatsine kamar taga kashi ta daka min tsawa. Dakewa nayi batare da nuna razana ba. Sai cemata da nayi “Ina kwana”.
“Daban kwana ba ƙya ganni firiritacciya. Ke mai ido a tsakar kai kinzo cin arziƙi gidan mutane har da marin ƴar masu gida ko?”.
“Ko kuma ƴar cin arziƙin itama ba”. Na faɗa ƙasa-ƙasa.
“What! Mi kikace?”.
Ta faɗa a matuƙar tsawace. Idanuna na ɗago na kalleta fuska a shagwaɓe. “Nifa bance komai ba Mamma. Please ki daina faɗan firgitani kike sake yi”.
Ba ita ba hatta Azizat ɗin Tata sai da ta juyo tana kallona da mamaki ƙarara a fuskarta. Balle su Bahijja da suka waro idanu da wangale bakuna. Niko yi nai tamkar ban gansu ba na sake shagwaɓe fuskata da taɓeta. Sai kuma na ɗauka ruwan dake a cikin kofi a gabanta na miƙa mata. “Kisha ruwan sanyi Mamma zuciyarki zatayi sanyi. Ba'a son masu shekaru irin naku da yawan faɗa za'a iya samun matsalar hawan jini daga nan ta zama ta zuniya”.
Galala ta sake yi tana kallona. Niko na tsatstsareta da idanu ina sake tura baki da marairaice face. Da wani irin masifar ƙarfi ta cije lips ɗinta tamkar zata hudasu. Sai kuma tasa hannu ta kaɓar da kofin hannun nawa. A take ruwan ya tarwatse mana a jiki har ita. Cikin masifar ƙaraji da wutar bala'i ta ce, “Balki!!!”. A razane Mama Balki ta amsa tana miƙewa daga durƙuson da tayi zaram. “Na.. na... Na'am Hajiya”.
“Ɗauki yarinyar nan ku ɓace min anan kafin na haukata jikunan ku da duka ku duka. Na kuma fasa aikin nata a sashena ki kaita sashen Hajiya Babba ta gyaro shi kafin nan kafin azhar”.
Wani irin waro idanu na masifa Mama Balki tayi, cike da tashin hankali da suɓutar baki ta furta, “Sashen Hajiya Babba kuma Hajiya?”.
“Ko bazaki kaitan ba ne?!!”.
Cikin rawar jiki mama Balki ta shiga girgiza kanta da faɗin, “To to to Hajiya ALLAH ya huci zuciyarki, za..zan kaita mana.” mama Balki ta faɗa tana kama hannuna jikinta na rawa sosai. Da ƙyar na iya danne dariyar dake cina har muka baro wajen, dan tana ambaton Hajiya babban naji tamkar na dirga tsalle dan daɗi. Muna kammala hawa upstairs ɗin a stairs ɗin ƙarshe na ɗan kallo ƙasan, sai da na haɗiye dariyar dake cina sannan na kwaɓe fuska kamar zan fasa kuka. “Mammah dan ALLAH ni dai ina neman alfarma. In dai akwai matsala da zarar kunji na banka ihu a kawo min ɗauki koda sassaƙa-sassaƙan garadan nan na bakin ƙofar gida ne a turamin idan ma ku bazaku iya ba”.
A matuƙar fusace ta watso min muguwar harara da gwala-gwalan idanunta “Sai dai a turo miki Ubanki. Ƴar iskar yarinya sheɗaniya. Da alama kema dai mahaukaciyar ce get out of my side kafin na canja miki kamanni”.
Baki na tura mata cikin sake narke fuska da yamutseta na ce, “Ai dai ubana yana aljanna in sha ALLAHU badai shi b....”
Kafin ma na kai ƙarshe Mama Balki ta fisga hannuna jikinta na rawa. Duk yanda naso ta sakan taƙi yin hakan har sai da muka ɓacema ganinsu. Kamar zata saki kuka ta ce, “Kandala baki da hankali ko? Yanzu wannan hukuncin da suka zartar a kanki bai isheki ishara ba ki koya kimtsa bakinki? Dan ALLAH ƴar nan kada ki sakamu a masifa mutanen gidan nan sun wuce fiye da yanda kike tsammani a fitina wlhy. Kiyi fatan Alhaji ƙarami bai bar gidan nan ba yazo ya fiddaki a wajen nan da wuri, zanje na samesa yanzun nan”.
Da sauri na ce, “A'a mama dan ALLAH kada ki kirashi. Miye dan tace nazo nayi aikin anan?”.
“Yarinyar nan baki da hankali, wautarki tayi yawa wlhy. Kandala wannan sashen da kike gani baida maraba da rami mai kwazazzabo da in ka faɗa a cikinsa sai abinda ALLAH yayi. Gara kiyi aiki a sashen Hajiya Mammah ɗin dan ita masifa ce kawai da takura, amma