Header Ads
Showing 105001 words to 108000 words out of 119225 words

Chapter 36 - TSUTSAR NAMA BOOK 2 By Bilyn Abdul.txt

Ads the beginning of article before Image

27 Jun 2024

5258

Ads at the middle of Article

samun amsa sai tsine mar yake a zuciya a daƙilen nan ya furta, “10:30 ne ƙa'idar zuwana nan dama”.
Yawu mai nauyi Minister ya haɗiye yana jinjina kai da washe baki, “Hakane kuma gaskiya. Hakan ma na gode.”
Maash ɗin baice komai ba, sai ajiye wayar yay gefensa ya ɗan ɗago ya zubama Minister cat eyes ɗinsa masu kaifi da ƙarfin gani. “Zamu iya fara abinda ya zaunar damu dan banda lokaci”. Ya furta ƙasa-ƙasa batare daya janye idanun ba kuma. Ji Minister yay duk kamar ya daburce. Cikin sarƙewar harshe da in inar da bai san daga ina tazo masa ba ya fara magana yana kaɗa kai kamar tsohon jandala gwaja na ƙadangare.
“Yes! Yes mizai hana. Bussines ne dama nake son mu ƙulla ranka ya daɗe, na turoma PA ɗinka kuma dukkan bayanai na. Motoci nake son a shigo min dasu kamar guda dubu biyu, idan babu damuwa bana son su wuce wata biyar. Dan nayima yarona alƙawari bana son na saɓa. Sai dai za'amin alfarmar biyan kaso ɗaya bisa biyun kuɗin daga nan zuwa ƙarshen shekara zan sake bada kaso ɗaya kasan al'amarin namu harkar gwamnati tasa fidda kuɗi kai tsaye zai iya jawo mana matsala, next shekara a wata biyar ɗin farko sai na ƙarasa biya harma da ƙarin wasu kuɗaɗe a sama. Amin alfarmar nan dan ALLAH badan ni ba badan na isa ba. Idan kuma kana buƙatar kaya sai muyi gishiri na baka manda a shirye nake”
Shiru babu alamar Maash zai amsa saima cigaba da kallonsa yake wani ƙasa-ƙasa batare da yasan kallon na hargitsa jinin minister ɗin bane. Hayatu daya fahimci Maash bazaice komai bane ya fuskanci ministar a karo na farko. Kansa tsaye ya furta, “Sir amma na gaya maka akwai ƙa'idoji sosai, sannan mu bama bada bashi kai tsaye sai kabi dukan ƙa'ijin mu. Bazai kuma yiwu ka bamu kuɗi ɗaya bisa biyu ba mu kawo maka kaya. Ƙa'idarmu zaka bada biyu bisa uku ne, tare da takardun kadarorinka na adadin sauran kuɗinmu dake kanka, lauyanka da namu su saka hannu muma mu saka. Mune kuma zamu baka lokacin biya, sannan bama buƙatar kuɗin ruwanka, zamu sakama kayanmu iya ribar da muke buƙata ta cinikayya kawai wannan kuma sirrinmu ne. A sunayen motocin daka bada kuma akwai waɗanda dokar ƙasa ta hana shigo da su kwata-kwata. Mu kuma bama ƙimma doka biyayya saboda duk wanda zai mu'amalance mu dolene muma yabi tamu dokar, idan ya kauce kuma ya rage nasa. Da farko dai fara karanta wannan sune dokokinmu da sharɗin ƙulla kasuwanci damu first. Ƙa'idarmu kuma gani ɗaya ake mana, dan daga wannan zaman boss bazai sake zama da kai ba face to face. Idan ka shirya daga nan har zuwa 3 lokcinka ne”.
Tuni fuskar ministar na ƙoƙarin canja yanayi, amma dai yana ƙoƙarin hana bayyanar hakan. Takardar da Hayatun ya taso ya ajiye masa a saman table ɗin gabansa ya ɗauka. Da sauri ya ɗago ya kalla Maash ɗin da yay biris da su, dan idanunsa ma a lumshe suke kamar namai barci. Sai dai makirin tsaff yake kallon Minister da su har yanzu. “Amma ranka ya daɗe yaya haka? Sannan nace inada kaya a hannu ko yanzu zan iya baku su muyi ciniki nima”.
“Tsarin kenan?”. Ya faɗa a yanda yake alamar kunnesa dai na'a kansu.......✍️




_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._




_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*




_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
















*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_








_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_






_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_




.....Baki Minister ya buɗe zai sake magana Hayatu ya taresa da faɗin, “Ranka ya daɗe bama canjawa a yanda muke. Zaɓi biyune kawai yarda matsayin amincewa, ko haƙura ka nema wasu kuyi business ɗin kawai mu bamu da damuwa, sannan bama buƙatar wasu kayanka mu nan dan duk abinda muke nema mun san inda muke samunsa”.
Wani mugun yawu minister ya sake haɗiyewa. Ji yake kamar ya zaro bindigar jikinsa ya fasa kan Maash ɗin da shegen PA ɗin nasa ma kowa ya huta. Sai dai hakan bashi yiwuwa, dan Maash na zama ya zaro tasa bindigar ya ajiye ta yanda kowa yake ganinta ƙuru-ƙuru, idan girma ne da cika aiki kuma tafi tashi a komai. Ashe girman kai da wulaƙancin yaron nan da ake faɗa masa ma ya wuce duk hakan. Yaro ƙarami da bai wuce sa'an ƴaƴan cikinsu ba sai gara rayukansu yake akan tituna saboda ya tara dukiyar da ba'asan tayaya tai tashin hauhawar gwauron zabi cikin ƙanƙanin lokaci haka ba. Gashi ya mamaye komai sai da shi a manyan Business ɗin ƙasar da ada sune masu juyasu a yanda suka so. Dolene ma suyi maganin terror ɗin yaron nan da sam babu tsoro ko shakkar kowa a cikin idanunsa shege mai ido a tsakar kai. Wata fitinar zasu ƙullo masa ta yanda ko allura bai isa sake sarrafawa ya siyar a ƙasar ba cikin daɗin rai. Dan tsalle target ɗin su na farko akan ƙin ko ganin Bussines ɗin daya zo masa da shi bashi ke nuna zasu barsa bane, akwai plan A har zuwa Z da suka tsara a kansa....
Kallon agogo da Maash yayi ya saka Hayatu daya san abinda yake nufi faɗin, “Sir kowane irin lokaci boss zai iya barin wajen nan mi ka yanke?”.
Firgigit Minister ya dawo hayyacinsa. Murmushi danne ɓacin rai ya saki da faɗin, “Shike nan na amince ɗin”.
“Okay zamu iya fara ciniki, lawyer ɗin mu na hanyar zuwa nan ɗin. Muna fatan tare kake da naka kai ma?”.
“Eh muna tare, yana can waje inda securitys suka ce su tsaya.”
Kai hayatu ya jinjina kawai yana rubuce-rubuce a file ɗin hannunsa. Kafin ya ɗauki ɗaya daga cikin wayoyi huɗu daya zube a gefensa, danne-danne yayi tare da miƙewa cikin girmamawa zuwa gaban Maash. Amsa Maash ɗin yayi batare da yace komai ba. Sai da ya kai wayar kunnensa cikin bada umarni ya furta “Lawyer ɗinsa ya ƙaraso”. Daga haka ya miƙama Hayatu wayar. Amsa Hayatu yayi shi kuma ya ajiye masa file ɗin hannunsa a stool ɗin gefensa....


Ƙarfe kusan uku suka dawo gidan, a matuƙar gajiye ya shigo, ga kansa na masa ciwo sosai na hargagin da surutun da Minister ya sashi yi. Dama sun sauke Hayatu gida, shi da TJ ne kawai da guards ɗinsa suka ƙaraso nan. Kai tsaye ya wuce bedroom, ya bar Tj na ƙoƙarin kashe sauran abubuwan dake kunne a falon. Kamar yanda ya saba kansa tsaye ya buɗe ƙofar ɗakin nasa ya shiga da sallama ciki-ciki yana ƙoƙarin zame jacket ɗinsa. A kan Laalah idonsa ya fara sauka. Har zai fara fusata tunda ba barinsa yake ya shigo masa nan ya kwanta ba sai kuma idonsa ya sauka a kanta. (Ya ALLAH) ya faɗa acan ƙasan ransa. Dan wlhy shaf yama manta ya barta anan ɗin. Sosai ta wani lafe can jikin fuskar gadon alamar a tsorace tai barcin saboda Laalah. Saletaf da handcuffs daya saka mata kuma na nan duka. Wani irin murza goshin yayi. Sai kuma yaja sirrin tsaki a ɗan kausashe da nuna harzuƙa ya furta, “Laalah get up!”. Zumbur kuwa karen ya miƙe shege da kunnen maciji dan barci yake fa. Amma tun motsa ƙofar ya wani tada kunnuwa sama alamar saurare, da alama kuma tunda bai miƙe ba tun farko ya gane ubangidan nasa ne ya dawo. Ƙofar ya buɗe masa kawai ya ce, “Go and sleep, goodnight thanks”. Bindi karen ya kaɗa masa ya fita abinsa shi kuma ya maida ƙofar ya rufe tare da ƙarasa cillar da jacket ɗin daya cire ɗin saman sofa. Gaban gadon ya ƙarasa tare da lalubar aljihunsa ya ciro keys ɗin Handcuffs ɗin ya cire mata daga hannayenta, dama bai wani matse ba, sai dai hannunta bazai iya fita ba. Kamar wadda ke a ido biyu kuwa ta wani sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi sosai da ya saka shi ɗan kallonta. Idanun ya zuba mata kusan sakan goma kafin ya kai hannun a hankali ya shiga ɗaye saletaf ɗin a hankali, da yaga zata motsa sai ya dakata. Sai ta sauke ajiyar zuciya ta koma sai ya cigaba. A haka ya gama cirewa duka. Aiko ta wani turo lips dinta gaba da suka sake zama jazur suka tsuke sosai kamar an gyara mata su ne da gayya. Sai lokacin yaga sawun hawaye da suka bushe alamar an dai ci kuka.
(Trouble Maker ). Ya faɗa a ransa yana kauda kansa da barin wajen. Ta riga ta juya kwanciyar tata zuwa jikin fuskar gado, dole ya koma ta can side ɗin hannunsa ɗauke da blanket ɗin dake a gadon ya lulluɓa mata dan yanda ta takure waje ɗaya yasan sanyin acn nan ne ya takurata. Shi kuma harga ALLAH bama zai iya zubar da kansa ya tashe ta ta koma side ɗinsu ba. Tunda zuwa yanzu ya gane a side ɗin Ummien sa take kwana. Dan baya ma jin ta cika sati a biyu tabar kwana a side ɗin masu aiki......


💞✨💞


Duk yanda Mom taso amfani da maganin nan hakan ya gagara, dan Halime ta kafa ta tsare kamar ta fahimci mi take shiryawa. Gashi koda ta kira Abba akan itafa sai dai a raba abinci Halime tayi nata ita tayi nasu ita da yara kai tsaye yace bai amince ba. Daga ƙarshe ma sai gashi ya dawo gidan. A gabansa Halime ta gama girki ta ɗibar musu ita da shi ta samo kula mai ƙyau kuma a kayanta ta zuba wani. Koda Abba ya tambayeta na waye, kai tsaye ta sanar masa na “Yaya Musaddiq ne. Yana babba a gida amma aita bashi abinci a wulaƙantaccen kwano bayan shike cefanen. Ni ba haka naga su Gwaggo nama su Yaya Buhari ba a gidanmu”.
Shiru Abba yay yana kallonta dan ya gagara yin magana. Sai ma wani nauyi ne yaji kansa ya masa tamkar Musaddiq ɗin na gabansa. Wannan abu ya ƙonama Mom zuciya. Tako shiga surfama Halime zagi, amma ko tari ƙinyi tai, sai da taga zagin na neman zama na fitar hankali ta fashe da kuka. Hankali tashe Abba yay kanta yana tambayar ta lafiya. Kukan ta sake fashewa da shi sosai. “Innata na tuna, tana cikin kabari amma ana zaginta. Kaicon wannan rayuwa, ban ja mata addu'a ba sai zagi, gaskiya bazan iya zaman gidan nan ana zagarmin mahaifiya ba”.
Rikicewa Abba ya sake yi, tuni ya manta da wata Mom a wajen ya kama Halime ya rungume. “Haba Halimatussa'adiyya na, ke da barin gidan nan ai sai dai in mutuwa. Kiyi haƙuri ai duk wanda ya zagi wani iyayensa ya zaga. Karki sake faɗar haka kinji, ALLAH yay miki albarka”.
“Amin nagode _my Rabon alkairi_. Na kuma yarda da kai bazan sake damuwa ba. Ai lobiyu irin kamar kainuwar tafkin bayan gidanmu ɗin nan”. Ta ƙare maganar da fakar idon Abba tai ma Mom da tai mutuwar tsaye sagale tana kallonsu. Sai kuma ta wani sake narkewa jikin Abban tana shashashar kukan ƙarya. Ai tuni Abba ya sake rikicewa, hannunta ya kama tare da ɗaukar kular abincin Musaddiq data zuba ɗin suka shige ɗaki yana sanarma Mom ga nasu nan a tukunya ta ɗauke su sun shige. Rasa ma abinyi Mom tayi, sai kawai taji hawaye na rige-rigen sakko mata. Shiru tai tsaye a wajen hawayen na tarara, tana ɗagowa suka haɗa ido da Halime na leƙenta ta window tana dariya. Gwalo tai mata dayin fari da ido ta saki labulen.
Yuuu Mom taji jiri na neman ɗibarta, har sai da ta kaita da dafe bango zuciyarta na mata zafi kamar zata buga. Wai ita Jalilah dake juya gidanta yanda take so, idan ta bama Imam umarni har rawa jikinsa yake don ganin ya cika mata akan lokaci. Amma yau a gabanta yake rawar jiki akan yarinya ƙarama sa'ar ƴarta har yana faɗa mata magana a kaikaice wai wanda yay zagi iyayensa ya zaga. Kai wane irin juya baya duniya ke son yimata ita kuwa a rayuwar nan....


To bari na tayaki tambaya momcy🤣🥱

💞⭐💞⭐💞


A ranar ni na samar da Number, na kuma tura saƙo ga Maash ta hanyar yaron mijina, amma ita har tsawon sati tana fakon wayar Mansoor, randa ta samu kuma tace bataga video awayar Mansoor ɗin ba iya bincikenta. Hankalinta duk ya tashi, amma sai na kwantar mata da shi ta hanyar tunatar da ita ai in shi babu a wayar tasa ya goge ko ya kwashe yarinyar nada shi. Bai kuma zama lallai ace an rasashi ta wajenta ba. Ta gamsu da zancena, dan haka tace nabar komai a hannunta zata samo video ɗin. Amma ya kamata a fara turama Maash saƙo fa kafin samuwar video dan guri nata ƙurewa kada wani ya rigamu. Ta bani dariya sosai, dan son kuɗin Aunty mai lasisi ne. Na yarda da shawarartata duk da ban gaya mata na fara turawa ba, dan haka a ranar muka fara turama PA ɗin Maash saƙo. Munyi hakane saboda saƙon zaifi isa garesa fiye da mu tura a wayarsa. Koda muka tura dai shiru babu wani reply har tsawon kwanaki, dan haka muka sake turawa. Anan ma babu amsa ga video ya gagara samuwa a hannun budurwar Mansoor. Sai kawai wani tunani yazo min. Munfa riga mun danganta video da ita yarinyar, Maash kuma ba sakarai bane zai iya bibiyarta. Gashi mu kuma babu video ma a hannunmu. Sai kawai muka yanke shawarar kidnapping ɗinta. Komai kuwa yazo mana cikin sauƙi da taimakon maigadi na dana bama dubu ɗari. Sai dai abin takaici babu video a wayar Samraah. Munyi-munyi kuma ta bada shi amma taurin kan yarinyar taƙi badawa........✍️






_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._




_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*




_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
















*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_








_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_






_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_




......Muna akan haka sai kawai ga reply PA ɗin Maash a randa muka aika saƙo na uku. Akan an amince za'a bamu 500m, amma da sharaɗin sai mun bada footage ɗin nan sannan a cika mana. Munta nazari akan hakan da tunanin akwai talala a batun, daga baya aunty tace babu abinda zai faru in sha ALLAH. Wannan ƙwarin gwiwa ya sakamu zuwa muka buɗe sabon account da sunan mai gadina, kai komai ma da nashi akai amfani har account ya samu muka turama Maash. Kuɗi kuwa a ranar suka shigo. Munta murna da ganin madarar kuɗin nan ziryan, sai hakan ya ƙara mana ƙaimi sosai.
Cikin abinda bai fi mintuna talatin ba muka cire kudin zuwa account ɗin aunty, shi kuma wancan muka rufesa gaba ɗayansa. Ga kuɗi sun samu amma video ya gagara samuwa a garemu. Sai ma wani tsautsayi daya so giftawa. Yarinyar ta samu nasarar cirar waya a jikin mai tsaronta tai kiran da aiki ya kusa buɗe mana. ALLAH ya taimakemu dai-dai sanda Mansoor ke kiran Attahiru akan ya kira dcp ya sanar masa Aunty na tare da shi. Shine tai kiran yaron namu akan yayi maza yabar gidan da yarinyar kada kuma ya kuskura yabar wani abu a gidan. Hakan kuwa akayi, sai dai labarin ya canja kansa a dalilin satar data saci sata. Dan kuwa dai an tare yaronmu an ƙwace Samraah, shima kuma anyi ram da shi. Mun shiga tashin hankali da baida misali, musamman ma Aunty, dan kuka ta dinga min a waya kan na rufa mata asiri dan ALLAH kada wanda yaji wannan magana. Niko na tabbatar mata zanyi hakan amma da sharaɗin bayan auren Mansoor da Samraah da sati ɗaya zamu saka ya saketa ya auri Husnah.
Tace ta yaya?.
Na amsa mata da zamu bar Mansoor ya auri Samraah ne dama dan mu amshi video ɗin hannunta. Da zarar mun amsa zamu ƙulla mata sharrin da bama shi kaɗai ba kowa sai yaji ya tsaneta. Ta jinjina al'amarin tare da sanar min ita ba itace abin ji ba Yaya ne da Mansoor. Niko nace mata karta damu komai zamu yisa a tsare ne, yanzu dai mu jira Samraah ta fito dan a lokacin bamu san Maash bane ya amsheta mun zata ƴan sanda ne. Sai daga baya muke jin ba ƴan sandan bane sai kuma hankalinmu ya sake tashi. Muna cikin yanayin ƙullawa da kwancewa sai ga Samraah ta fito. Farin ciki babu irin wanda bamu yi ba, dan mun san plans ɗinmu zasu cigaba da tafiya kenan.
Mun cigaba

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads