Header Ads
Showing 90001 words to 93000 words out of 119225 words

Chapter 31 - TSUTSAR NAMA BOOK 2 By Bilyn Abdul.txt

Ads the beginning of article before Image

27 Jun 2024

5250

Ads at the middle of Article

taimakonsa. Ai shi ba yaro bane kuma yana cikin hankalinsa. Miyasa bazai dinga ma kansa addu'a ba. Ko sai neman dukiya kawai ya iya. Su kuma dake zaune Mama ai banga amfanin subar gidan ba yanzu, gara suna a cikinsa ta samu lafiya suma su koma kwasar kashinsu a cikin hannayensu. Ai ni baki sani ba. Aduk lokacin da maƙiyi ke tare dani bana son yay nesa da ni, na fison ya cigaba da rayuwa a jikina dan ya cigaba da kallon cigabana da nasarorina zuciyarsa na zafi. Koba komai shi zai ƙare rayuwarsa da lokacinsa ne wajen ganin ya cimmani. A bayyane shike da asara. Bai ƙaru da komai a duniya ba, ya je lahira ya tadda bai ajiye komai a taskarsa ba. Mi yafi wannan daɗi dan ALLAH”.
Murmushi Mama Balki tayi tana mai kai hannu ta shafa fuskata. Sai kuma tace, “ALLAH yayi miki albarka Samraah. Hakan ma Nagode. Amma dan ALLAH ayi haƙuri dai a haɗa da Alhaji Ƙarami. Yaron na cikin jarabawa mai ban tausayi. Karki damu da murɗaɗɗun halayensa abubuwane sukai masa yawa a cikin kai. Sannan da kike ganinsa nan mutum ne mai ibada da tarin ilimin addini. Kawai dai ana gusar masa da kulawa ne saboda kada yay ma kansa addu'ar. Amma a hakan ma azumin Litinin da Alhamis baya taɓa wucesa. Salla a cikin jam'i komi yake. Hayatu ya rantse min ya maya komai girman kasuwanci da abinda zai samu a cikinsa ko muhimmancinsa idan lokacin salla yayi sai ya barsa. Komai girman mai mulki ko wani muƙami ko dukiya dan Awwab na zaman meeting dasu baya hana da an kira salla ya miƙe ya barsu yaje yayi sallarsa. Sam bai haɗa bautama UBANGIJINSA da komai ba. Sadaka da taimakon marasa ƙarfi bazasu musaltu ba. Yasha yin ƙyautar gidajen zama da motoci batare da ya ko damu ba. Ɗaukar nauyin karatun yara da gyara makarantun addini da masallatai da asibitici ba'a magana. Idan zan ta lissafo miki alkairan Awwab zamu kwana nan, hatta samar da ruwa ga masu ƙarancinsa bai gaza ba, sai dai hakan bazai hana kuma ace yana da wasu halaye marasa ƙyau ba. Dan ɗan adam tara yake a komai na rayuwa bai cika goma ba. Ladanki naga UBANGIJIN talikai idan kinyi hakan”.
Ban iya cemata komai ba face duƙar da kaina kawai ina wasa da yatsun hannuna. Sai kuma a hankali na furta, “Mama kinada hoton mijinki da ya rasu?”.........✍️








_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._




_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*




_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
















*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_








_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_






_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_


....Abinda ya fara dai-daita tsakanin Awwab da Hajiya ƙarama kulawar da take bama Ummie. Wanda dama tun kan ta auri Paah tanayin hakan, shima kuma Awwab ɗin ya sani, shi dai auren ne yake ganin kamar akwai cin amanar mahaifiyarsa sai kuma kishi da yake tayata. Amma daga baya daya fahimci Hajiya ƙaramar bata canja daga duk abinda takema ummien ba sai ya sakko. Wannan dalili na shiryawarsu ya saka Hajiya Ƙarama da Paah dawowa gidan nan. Basufi watanni uku ba Hajiya Nafisa da suke kira (Hajiya Mammah) a yanzu yayar Paah da akai aurenta bayan haihuwar Awwab dan ta jima batai aure ba mijinta suka samu saɓani. A Niger take auren, koda tazo sai Ba prof.. yace bazata zauna masa gida ba, dan a yanda muke jin labari fitinarta ta hanata zama lafiya da mutane kamar yanda ta hanata aure da farko, ba kuma a wannan karon bane ta fara tahowa gida yaji, sai dai na wannan karon yayi tsamari sosai dan harda dukanta mijin yayi. Koda Baba prof.. ya bibiyi al'amarin sai ya gano itace bata da gaskiya, shine ya hanata zaman gidansa. Kakarsu Awwab ɗin ce tace ta dawo nan gidan ta zauna. Itama da farko Awwab yaso borema zamanta, sai dai bamusan yaya akayi ba kuma daga baya yayi shiru. Dawowarta gidan nan komai ya fara canjawa. Ta maidani sashen masu aiki ni da iyayen Hayatu wai matsayin data sammu da shi kenan. Bayan hakan bata sammu a cikin danginsu kona Ummie ba. Ba muji komai ba muka koma. Sai dai muna ji muna gani kulawa da Ummie ya fara gagararmu, an kawo sabbin masu aiki, tare da saka Awwab komawa kan kasuwancinsa. Yaranta biyu ƴammata sun baro Niger sun dawo nan suma. Gasu basu da tarbiyya sam, basa shakkar taka kowa da wulaƙanta kowa. Gasu malalata basu iya komai ba. Dan dalilin zaman nasu yasa Awwab saka a samo masu aiki ganin suna neman ƙazanta gidan. Hajiya Mammah bata wuce wata biyar a gidan ba ALLAH yay ma mahaifiyar Hayatu rasuwa, sosai na shiga kiɗimuwa hakama mahaifinsa da shi kansa Hayatun. Shima Awwab rasuwar ta girgizashi sosai. A dalilin wannan zaman gaisuwa Alhaji Abdullahi ƙanin Paah ya dawo gidan nan da zama shi da iyalinsa, matarsa ɗaya da yara biyu Malika da Muhsin. Dan koda aka gama komai sai suka ƙi komawa nasu gidan suma. Abin nan ya bani mamaki ya kuma ɗauremin kai, sai dai banda tacewa. Ashe basu kaɗai bane, sai ga mahaifiyarsu itama (Kakar su Awwab ɗin matar Baba prof..) wai itama ta dawo nan saboda sun samu saɓani da Baba prof ɗin akan ƙin komawar Hajiya Mammah gidan mijinta. Shikenan duk sun dawo, Baba prof.. da autarta Mashi'a ne kawai babu, dan ita ba'a Nigeria take aure ba. Sai dai duk ƙarshen shekara tana zuwa bikin ƙara shekara na Ummie da Paah ke shiryawa.
Da farko su dukansu kulawa suke bama Ummie. Dan ko sashenta kaje sai ka san ita ɗin ƴar gatan dangi ce. Komai tsaff kamar ba wadda ke'a halin ciwo ba. Idan ba abin ne ya motsa ba ma bazaka taɓa cewa ga lalurar dake damun nata ba. Sosai Awwab ya samu nutsuwa a ɗan tsakanin. Hankalinsa ya kwanta har wata ƙiba yayi ya ƙara haske. Mu kammamu mun samu nutsuwa. Dan a lokacinne akai auren Hayatu da Falak ɗina. Bayan bikin shima Awwab ya bamu shawarar yin aure ni da mahaifin Hayatun. Da farko munso turjewa, amma suka dage shi da Hayatu dole muka amince. Watanni biyu zuwa uku tsakani kakarsu Awwab ta kwanta jiyya. Bata wani jima ba ALLAH yay mata rasuwa a ƙasar Egypt Cairo. Rasuwar ta girgiza kowa na family ɗin, musamman ma Baba prof.. da sai ya baka tausayi. Bayan gama jimami komai ya koma normal. ALLAH ya cigaba da riƙo da hannayen Awwab komai ya taɓa na kasuwanci sai yayi albarka. A cikin abinda bai wuce shekara ɗaya ba ya sake zama wani mahaukacin mai arziƙi da sunansa ke yawo tako ina ama duniya ba ƙasarsa kawai ba. Ba komai ya jawo hakan ba kuma sai ƙarancin shekarunsa da mutane ke gani amma ya tara irin wannan dukiya. Sannan mahaifinsa ba wani shahararren mai arziki bane balle ace ya gada ne. Sanda kakansa da mahaifiyarsa sukai nasu tashen basu ko kama ƙafar nashi arziƙin ba, ansan sunansu ne a iya wani yanki na garin Lagos, shiko duniya ce ke kallonsa a yanzu.
Tun Awwab na ƙarami dama ba mutum bane mai yawan magana sai idan shi yaso. Sai dai akwai tausayi da girmama duk wanda ya girme masa. Bai san wulaƙanta mutane ba koda kuwa ƴan aikine wannan tarbiyyar mahaifiyarsa ce da kakansa Abbie. Babu abinda ya damesa da sabgar kowa tashi kawai yake yi. Tun bayan rasuwar Abbie Baba prof.. ne kawai amininsa. Dan da shi kawai zakaga yana dogon hira. Sai ko mu idan yaso wani lokacin zakiga yazo har nan sashen ya zauna koda ba zaiyi magana ba. Dan alokacin da mahaifiyata ta tarasu zaki ɗauka yanada alaƙar zuminci mai ƙarfine da ita. Sosai ya nuna damuwarsa.
Tunda ayyuka da harkokinsa suka sha masa kai sai abubuwan gidan suka fara canjawa. Kulawar da ake bama Ummie ta fara ja baya. Ciwonta ya sake tsananta. Idan kinga ana kula da al'amarinta ya shigo gari ne, kuma a lokacin zakiga ciwonta ya tsananta. Duk yanda muka so mu kula da ita mu an hanamu, sashenta ma an mana iyaka da shi, duk randa kuma na shiga koda a sace ne al'amarin baya daɗi tsakanina da Hajiya Mammah. Hajiya ƙarama ce kawai ke nata ƙoƙarin bata taɓa fasawa ba dan hargagin Hajiya Mammah baya damunta. Sau biyu ana korarmu ni da Abban Hayatu saboda nacewa akan kulawa da Ummie, Awwab ne ke dawo damu. Dole muka tsaya matsayinmu na masu aiki dan mu zauna lafiya. Amma neman hanyar kuɓutar da Ummie da son gano bakin zaren kullum cikin yi muke. Masu aiki kullum cikin kawowa ake domin kulawa da Ummie, sai dai basa zarta wata ɗaya suke guduwa. Kowa ɗauka yake saboda ciwon Ummien suke guduwa. Ni kuma a raina inajin ba hakan bane ba akwai abinda ke korarsu.
“Wannan shine tarihin wannan gida a taƙaice Kandala. Dan na yanke miki abubuwa da yawa ne a cikinsa saboda wasu dalilai. Sannan ina fata ki fahimci wasu da kanki kuma”.
Hawayen da suka kasa tsaya min tun ɗazun na ƙara sharcewa. Cikin rawar murya data gama dasashewa na ce, “Amma mama miyyasa duk kika faɗa min wannan? Bayan baki sanni ba? Baki san koni muguwa bace, ko nama shigo gidan ne dan wata manufa”.
Ɗan murmushi tayi itama tana share hawayenta. Kafin ta kamo hannuna cikin nata. “Nasan ke ba muguwa bace Kandala. Duk da dai da farko haka kawai naji ƙaunarki a cikin zuciyata. Sai kuma wata fuska da nake gani akan fuskarki da bansan dalilin hakan ba. Da ga baya Hayatu ya sanar mana alaƙar dake tsakaninki da Awwab....”
Wani mugun zaro idanu nayi ina zabura gefe da fincike hannayena dake a cikin nata. Magana nake son yi amma na kasa. Sai lips ɗina dake rawa kawai. Murmushi ta saki tare da sake kamo hannun nawa ta ce, “Kwantar fa hankalinki Samraah. Kar kuma ki fasa aikin ladar da kika fara. Daga Ummie har Awwab da ɗan uwansa abin tausayi ne, suna buƙatar mai tallafama rayuwarsu. Mu kuma da muke da damar yin hakan bamu da wani ƙarfin iko. Dama fatan da muke masa yay aure ya samu mace ta gari da zata juya mulki da tsarin wannan gida ta inda kowa baiyi zato ba. Alhamdullah kuma muna fatan an samu, dan ko yanzu Awwab yaso nunama duniya matsayinki a gurinsa dole kowa ya girgiza, duk da ina tsoron kar su cutar dake dan mutanen nan hatsabiban kansu ne suma, dan ma taurin kan Awwab na rage musu tasiri a wasu lokuta. Sai dai duk abinka baka isa gane wanene na kirkin ba idan kika cire Baba prof.. Dan kowa da tasa illar da manufa da kike gani. Amma ke yarinya ce mai wayo da ilimin addini, dan har na zamani na fahimci kina da shi, ɓoyewa kawai kike kamar yadda kika ɓoye mana ainahin kanki da sunanki. Dan ALLAH ki daure ki taimaki waɗan nan bayin ALLAHn. Awwab mutumin kirki ne, yana iya ƙoƙarin sa wajen tsare mutuncin kansa ta hanyoyi da dama da samarin zamanin nan sukan kasa musamman idan kudaɗe na yawo a hannayensu. Kisa a ranki aikin lada kike yi sakamakon ki naga UBANGIJI. Kisa a ranki ceto zakiyi na Uwa da yaƴanta a cikin gobarar da bata da iyaka. Nasan bake zaki bama Ummie lafiya ba, amma zaki zama wani tsanin taimakawa mukai ga samuwar lafiyar tata. Dan in har kina a tare da ita duk maganin da mu kuma zamu nemo mun san zaki bata. Za ki kuma dinga mata addu'a har shi Awwab ɗin dan bana raba ɗayan biyu akwai sihiri mai ƙarfi shima a jikinsa. Fatanmu shima Fahad ya dawo gida su dai-daita da ɗan uwansa. Sannan waɗan nan mutanen da suka cika gidan nan kowa ya koma inda ya fito..”
Karo na farko na saki murmushi mai ciwo. Sai kuma na girgiza kaina. “Mama zan iya tsayawa dai akan samun lafiyar Ummie in sha ALLAHU da kuma batun dawowar ɗan uwansa gida. Amma shi babu abinda ya shafeni da shi ko halin da yake a ciki. Yaje can ya nemo mai taimakonsa. Ai shi ba yaro bane kuma yana cikin hankalinsa. Miyasa bazai dinga ma kansa addu'a ba. Ko sai neman dukiya kawai ya iya. Su kuma dake zaune Mama ai banga amfanin subar gidan ba yanzu, gara suna a cikinsa ta samu lafiya suma su koma kwasar kashinsu a cikin hannayensu. Ai ni baki sani ba. Aduk lokacin da maƙiyi ke tare dani bana son yay nesa da ni, na fison ya cigaba da rayuwa a jikina dan ya cigaba da kallon cigabana da nasarorina zuciyarsa na zafi. Koba komai shi zai ƙare rayuwarsa da lokacinsa ne wajen ganin ya cimmani. A bayyane shike da asara. Bai ƙaru da komai a duniya ba, ya je lahira ya tadda bai ajiye komai a taskarsa ba. Mi yafi wannan daɗi dan ALLAH”.
Murmushi Mama Balki tayi tana mai kai hannu ta shafa fuskata. Sai kuma tace, “ALLAH yayi miki albarka Samraah. Hakan ma Nagode. Amma dan ALLAH ayi haƙuri dai a haɗa da Alhaji Ƙarami. Yaron na cikin jarabawa mai ban tausayi. Karki damu da murɗaɗɗun halayensa abubuwane sukai masa yawa a cikin kai. Sannan da kike ganinsa nan mutum ne mai ibada da tarin ilimin addini. Kawai dai ana gusar masa da kulawa ne saboda kada yay ma kansa addu'ar. Amma a hakan ma azumin Litinin da Alhamis baya taɓa wucesa. Salla a cikin jam'i komi yake. Hayatu ya rantse min ya maya komai girman kasuwanci da abinda zai samu a cikinsa ko muhimmancinsa idan lokacin salla yayi sai ya barsa. Komai girman mai mulki ko wani muƙami ko dukiya dan Awwab na zaman meeting dasu baya hana da an kira salla ya miƙe ya barsu yaje yayi sallarsa. Sam bai haɗa bautama UBANGIJINSA da komai ba. Sadaka da taimakon marasa ƙarfi bazasu musaltu ba. Yasha yin ƙyautar gidajen zama da motoci batare da ya ko damu ba. Ɗaukar nauyin karatun yara da gyara makarantun addini da masallatai da asibitici ba'a magana. Idan zan ta lissafo miki alkairan Awwab zamu kwana nan, hatta samar da ruwa ga masu ƙarancinsa bai gaza ba, sai dai hakan bazai hana kuma ace yana da wasu halaye marasa ƙyau ba. Dan ɗan adam tara yake a komai na rayuwa bai cika goma ba. Ladanki naga UBANGIJIN talikai idan kinyi hakan”.
Ban iya cemata komai ba face duƙar da kaina kawai ina wasa da yatsun hannuna. Sai kuma a hankali na furta, “Mama kinada hoton mijinki da ya rasu?”.........✍️








_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._




_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_


_BANK NAME:KEYSTONE_


_BANK ACC NO:6019473875_


_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_


_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_


__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_


*09033181070*


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*




_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_








*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
















*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_








_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_






_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_




......Ɗan jimm Mama Balki tayi alamar tunani, kafin ta jinjina kanta. “Za'a samu hotonsa, amma sai dai a wajen Alhaji ƙarami. Dan lokacin da muka dawo rai a ɓace daga garinsu abinda danginsa sukai mana ya sakani a damuwa sosai harna kwanta ciwo. Bani da aiki sai kallon hotonsa ina kuka. Ga kuma halin da Ummie take ciki itama duk na haɗu na ƙara hargitsewa. Shine Ummie ta saka Alhaji Ƙarami ya tattare hotunan duka daga wajena, ni kuma ban sake amsa ba bayan komai ya lafa na samu nutsuwa. Amma ina ganin zan tambayesa yanzu, ko kuma na saka Hayatu ya amso”.
Kai na jinjina mata cikin gamsuwa.


✨❤️✨


Yau kwanaki biyu kenan Mom bata saka Abba a idanunta ba. Dan tun jifar da tai masa a washe garin angwancinsa bai sake shiga inda take ba. Hakama amaryar tasa taƙi fitowa. A tunaninta dana yaƴanta harma da Ummanta ai tsoro ya hana amarya fitowa. Dan haka suka fara jin alfahari a ransu musamman ma Mom. Haka zata fito tsakar gida tana habaici da yada magana. Daga Gwaggo Gudidi har Halime da Gwaggon ce ta kwaɓeta babu mai kulata. Hakama Abba yayi watsin ruwan tsarki da ita shan shagalinsa kawai yake da amaryarsa. Gaba ɗaya ya ajiye shekarun girmansa gefe yana koyama Halime salo-salo da tabbatar mata ita ɗin ma fa mace ce. Itako banda raki da taɓara babu abinda take ɓarar masa. Gaba ɗaya ta susuce bawan ALLAH baya ganin komai da tuna kowa a gabansa sai ita. Hatta kasuwa a kwani biyun nan babu inda yake zuwa a gidan yake yini salla kawai ke fidda shi. Dole kuma akayi abinci Gwaggo Gudidi taje ta ɗiba musu tasa Bibaa na kumbure-kumbure takai musu har falo.
Yau dai zaman ɗaki ya ishi Halime. Tana ganin Abba ya fita sallar la'asar ta fito. Tsaff take cikin kwalliya, duk kwalliyar ba'a yi ta yanda ya kamata ba kaya data saka sun fiddo jikinta tsaff da yi

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads