Showing 108001 words to 111000 words out of 119225 words
Chapter 37 - TSUTSAR NAMA BOOK 2 By Bilyn Abdul.txt
da tsarinmu yanda ya kamata ana gobe ɗaurin aure kuma sai komai ya canja daga yanda yake. Dan mun tafi amsar kayanmu wajen tela da wanda amarya zata saka da ba'a kai ba akai ram da mu....
💞✨💞✨💞
Shirin kwanciya yayi, lokaci-lokaci yana ɗan jan ƙaramin tsaki dan yunwa yake ji. Da farko chocolates ɗin nashi na fama ya ɗebo, sai kuma ya maidasu yana jan gajeren tsaki. Harga ALLAH abinci kuma yafi buƙata dan rabonsa da cin wani abu matsayin normal abinci 2days kenan. Daga kayan fulawa sai fruits da chocolate yake zubama cikinsa. Saukar idanunsa akan tray ɗin data shigo da shi ɗazun ya sashi nufar wajen. Kwanikan ya buɗe tamkar wanda akaima dole. Dan sai faman yamutse fuska yake da ɓata rai. Fruit salad ɗin daya ɗan sha ɗazun ya zuba ma ido da gasashen naman kaza daketa ƙamshi alamar zai yi daɗi. Harya maida ya rufe kamar bazai ci ba sai kuma dai ya sake buɗewa dan gwara yaci koda kaɗan ne so yake yay barci kada yunwar ta takurasa. Saboda in har yaji damuwa da yunwa tofa da gaske yunwar yake ji. Duk yanda kuma yaso riƙe kansa bashi yiwuwa.
Ya tsakuri kazar zai kai baki akai kiran wayarsa. Yaso sharewa sai dai ganin Abubakar ne babban yaronsa ne shima dake riƙe da harkokinsa a ƙetare ya sashi saka ta hannunsa daya ɗiba a bakin nasa yana ɗaukar wayar. Yaci kusan lauma biyar yana wayar, sai da ya kammala magana da Hayatun ya fahimci ko bissmillah baiyi ba. Kansa ya dafe yana yamutse fuska. Sai kuma yayi bissmillar sannan ya cigaba da ci. Da yake yunwar yake ji sosai yaci ya kuma sha fruit salad ɗin shima sannan ya koma bathroom yay brush ya fito. Kansa tsaye ya nufi gadon zai kwanta sai kuma ya tsaya cak yana kallonta. Gefen lips ɗinsa ya ɗan ciza sai kuma ya ƙarasa ya ɗauki pillow biyu ya koma saman sofa ya kwanta. Bawani yaji daɗin kwanciyar bane ba kasancewar bai saba kwanciyar a hakan ba. Iska ya furzar kaɗan tare da lumshe idanunsa kawai.
Barcin ya ɗan jashi da nisa kaɗan saboda gajiyar da yayi aka fara masa mintsine-mintsine a jiki. Idanunsa ya buɗe kawai batare daya motsa daga kwancen da yake ba. Tun yana ɗaukar al'amarin wasa har dai yaji yau fa dabance, a farko ya ɗauka normal ne kamar kullum, dan ya jima yana fuskantar irin wannan yanayi amma jarumtarsa na tattare komai ta bizne saboda ya riga ya sakama ransa in har ba Ummie ta samu lafiya ya ganta a farin ciki ba baya jin yana da wani spiece a rayuwarsa na kallon wata mace da wannan siffar. To tayaya ma zai yarda hakan ta kasance. Ace mahaifiyarsa na kwance cikin lalura mai ban tashin hankali shi kuma hankalinsa nakan samawa gangar jikinsa abinda take buƙata. Kai impossible. Cikin cizar lips ya sake lumshe idanunsa a yanayin tilastama kansa kamar yanda ya saba. Dan shi bai taɓa shan wani magani domin hana faruwar haka ko samun sassauci ba. Ya dai riƙe azumi tare da takure kansa matuƙa saboda jarumta. Sai idan al'amarin yayi tsamarine yake amfani da lemon tsami bisa shawarar abokinsa Taj.. daga ba hakanba baya shan komai.
Cikin ƙanƙanin lokaci wata irin zufa ta gama jiƙe masa jiki, amma bawon ALLAH ko motsawa baiyi ba yana daga kwancen yana sauraren hukuncin UBANGIJI. Tsanantar al'amarin ya sashi yunƙurawa a karo na farko ya tashi zaune haƙoransa ya datse da lips ɗinsa kamar zai huda shi. Zaman ma gagararsa ya nema farayi, ya miƙe tsaye zuciyarsa na tsananin bugawa. Taku ɗaya biyu ya tsaya cak, saboda ƙullewa da cikin yay sosai ƙafafun ma kansu riƙewa suke. Ga idonsa ya sauka akan wadda ke kwance a saman gadonsa tana barcinta hankali kwance. Duk da ba ganin fiskarta yake da ƙyau ba saboda ƙarancin haske yanda tai luff cikin lallausan blanket ɗinsa ya tabbatar masa da hakan. Kansa ya kauda, sai kuma ya nufi Bathroom da ɗan yanayin sassarfa na tilastama kai jarumta. Babbar shower ɗin mai ƙarfi ya sakarma kansa. A cikin ƙanƙanin lokaci jikinsa ya gama jiƙewa sharkaf, sai dai ta saman kansa yayi amfani da shower cap gudun kada ruwa ya taɓashi yay mura. Dan shi bashi da wahalar yin mura. Sosai ruwan ya dakesa amma baiji komai ya canja ba. Sai ma sake ruruwa da yake jikinsa na sake tabbatar ma da yau ɗin fa yau ce. Cire kayansa yayi ya fito bayan ya ɗaura alwala. Sai dai raka'a biyun farko ma da ƙyar ya iya kaisu saboda yanda al'amarin ke sake ta'azzara. Shiru ya cigaba da zama a saman sallayar, kafin kuma dai ya miƙe da ƙyar. Saman gado ya tafi da nufin hawa sai kuma ya tsaya cak, karan farko ya zubama fuskar Samraah dake shaƙar barcinta a nutse idanunsa da suka juye gaba ɗaya. Ba wani tar-tar yake iya ganinta ba, sai dai yanayin ƙarancin hasken sai ya ƙara ƙawata masa ƙyawunta abinka da wanda ke cikin yanayi. A hankali ya fara takawa tamkar hawainiya mai tsohon ciki. Ya kai hannunsa duka biyu yaja igiyoyi biyu dake ɗaure da net ɗin da aka zagaye gadon tamkar rumfa. Cizar lips ɗinsa ya sakeyi yana mai duƙar da kansa tamkar wanda ke jin abinda zai aikata ba dai-dai bane. Har ya motsa jikinsa da nufin komawa sai kuma ya sake tsayawa cak sakamakon nauyin da ƙafarsa tai masa. Ga zuciyarsa na ƙara tabbatar masa da (Awwab matarka ce fa, ALLAH ya halatta maka miyyasa zaka cutar da kanka kaƙi karɓar ni'imar da yay maka. Kaje tareta, kaje) Da wani irin tashin hankali ya tura yatsunsa cikin sumar kansa ya harmutsata ya furta, “Ya rabbah Ummie! Ummie! Na, ban mata adalci ba. My ALLAH help me! I beg you”.
A dai-dai nan Samraah tayi juyi, bargon daya rufa mata har wuya ta janye ƙasa alamar ya isheta. Tamkar wadda ake juyawa da remote ta juyo sosai ta inda yake tana facing ɗinsa. Saukar idanunsa a saman ƙirjinta ya sashi runtse idanunsa da ƙarfi tare da cije lips ɗinsa har sai da ya fasashi da haƙori. Sai kawai ya zube a saman gadon hannayensa duk biyu dafe da kansa. Tsawon mintina ya ɗauka a hakan kafin zuciyarsa ta gama yanke masa shawarar mafita. Fitilar dake cikin gadon ya kunna tare da haurawa gaba ɗayansa.
Cikin barci na dinga jin saukar numfashi mai ɗumi a saman fuskata. Sosai zuciyata ta yanka na buɗe idanuna. Tar-tar na saukesu akan fuskarsa data gama canjawa zuwa yanayin da ban taɓa ganinsa ba. Sake faɗuwa gabana yayi na waro idanun gaba ɗaya a kan fuskarsa. Idanunsa dake a kaina fes ya lumshe a bala'in slowly sai kuma ya sake buɗesu cikin tsakkiyar nawa. Yanzun kam kasa jurewa nayi, cikin rawar murya data lips na furta, “Na shiga uku Awwab minene haka kake y.....”
“Shiiii!!!!” ya faɗa yana sake matso da fuskarsa daf-daf da tawa tare da ɗaura yatsarsa saman lips ɗina dake rawar tsorata. Cikin wata irin murya mai tsananin sanyi da zama low can ƙasan maƙoshinsa, ta kuma shaƙe ya furta, “Bana son surutu”........✍️
________________
*Aleenah’s Refreshing Scent*
Ta kawo muku ingatattun turaruka na ruwa (perfumes), oil, Humra, Turaren wuta and more. Kunsan kamshi dai rahama ne, ingantaccen kamshi me rike jiki da Kaya me sa nutsuwa da shiga taro cikin kasaita.
Ina hajiyoyi, uwargida, Amare da kuma masu niyyar shiga daga ciki? don’t afford to miss this golden opportunity.
Aleenah’s refreshing scent ta kawo muku kayan kamshi masu kyau, inganci da kuma sauki…….
Akwai Kaya Kala kala na nau’in turaruka Akan farashi me rahusa.
Muna Nationwide delivery 🚚
09034259662
08081693351
Koda kuɗinka sai da rabonka. Ai ƙamshi duniya ne 😘😌😌
__________
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_*
*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_
......Muna akan haka sai kawai ga reply PA ɗin Maash a randa muka aika saƙo na uku. Akan an amince za'a bamu 500m, amma da sharaɗin sai mun bada footage ɗin nan sannan a cika mana. Munta nazari akan hakan da tunanin akwai talala a batun, daga baya aunty tace babu abinda zai faru in sha ALLAH. Wannan ƙwarin gwiwa ya sakamu zuwa muka buɗe sabon account da sunan mai gadina, kai komai ma da nashi akai amfani har account ya samu muka turama Maash. Kuɗi kuwa a ranar suka shigo. Munta murna da ganin madarar kuɗin nan ziryan, sai hakan ya ƙara mana ƙaimi sosai.
Cikin abinda bai fi mintuna talatin ba muka cire kudin zuwa account ɗin aunty, shi kuma wancan muka rufesa gaba ɗayansa. Ga kuɗi sun samu amma video ya gagara samuwa a garemu. Sai ma wani tsautsayi daya so giftawa. Yarinyar ta samu nasarar cirar waya a jikin mai tsaronta tai kiran da aiki ya kusa buɗe mana. ALLAH ya taimakemu dai-dai sanda Mansoor ke kiran Attahiru akan ya kira dcp ya sanar masa Aunty na tare da shi. Shine tai kiran yaron namu akan yayi maza yabar gidan da yarinyar kada kuma ya kuskura yabar wani abu a gidan. Hakan kuwa akayi, sai dai labarin ya canja kansa a dalilin satar data saci sata. Dan kuwa dai an tare yaronmu an ƙwace Samraah, shima kuma anyi ram da shi. Mun shiga tashin hankali da baida misali, musamman ma Aunty, dan kuka ta dinga min a waya kan na rufa mata asiri dan ALLAH kada wanda yaji wannan magana. Niko na tabbatar mata zanyi hakan amma da sharaɗin bayan auren Mansoor da Samraah da sati ɗaya zamu saka ya saketa ya auri Husnah.
Tace ta yaya?.
Na amsa mata da zamu bar Mansoor ya auri Samraah ne dama dan mu amshi video ɗin hannunta. Da zarar mun amsa zamu ƙulla mata sharrin da bama shi kaɗai ba kowa sai yaji ya tsaneta. Ta jinjina al'amarin tare da sanar min ita ba itace abin ji ba Yaya ne da Mansoor. Niko nace mata karta damu komai zamu yisa a tsare ne, yanzu dai mu jira Samraah ta fito dan a lokacin bamu san Maash bane ya amsheta mun zata ƴan sanda ne. Sai daga baya muke jin ba ƴan sandan bane sai kuma hankalinmu ya sake tashi. Muna cikin yanayin ƙullawa da kwancewa sai ga Samraah ta fito. Farin ciki babu irin wanda bamu yi ba, dan mun san plans ɗinmu zasu cigaba da tafiya kenan.
Mun cigaba da tsarinmu yanda ya kamata ana gobe ɗaurin aure kuma sai komai ya canja daga yanda yake. Dan mun tafi amsar kayanmu wajen tela da wanda amarya zata saka da ba'a kai ba akai ram da mu....
💞✨💞✨💞
Shirin kwanciya yayi, lokaci-lokaci yana ɗan jan ƙaramin tsaki dan yunwa yake ji. Da farko chocolates ɗin nashi na fama ya ɗebo, sai kuma ya maidasu yana jan gajeren tsaki. Harga ALLAH abinci kuma yafi buƙata dan rabonsa da cin wani abu matsayin normal abinci 2days kenan. Daga kayan fulawa sai fruits da chocolate yake zubama cikinsa. Saukar idanunsa akan tray ɗin data shigo da shi ɗazun ya sashi nufar wajen. Kwanikan ya buɗe tamkar wanda akaima dole. Dan sai faman yamutse fuska yake da ɓata rai. Fruit salad ɗin daya ɗan sha ɗazun ya zuba ma ido da gasashen naman kaza daketa ƙamshi alamar zai yi daɗi. Harya maida ya rufe kamar bazai ci ba sai kuma dai ya sake buɗewa dan gwara yaci koda kaɗan ne so yake yay barci kada yunwar ta takurasa. Saboda in har yaji damuwa da yunwa tofa da gaske yunwar yake ji. Duk yanda kuma yaso riƙe kansa bashi yiwuwa.
Ya tsakuri kazar zai kai baki akai kiran wayarsa. Yaso sharewa sai dai ganin Abubakar ne babban yaronsa ne shima dake riƙe da harkokinsa a ƙetare ya sashi saka ta hannunsa daya ɗiba a bakin nasa yana ɗaukar wayar. Yaci kusan lauma biyar yana wayar, sai da ya kammala magana da Hayatun ya fahimci ko bissmillah baiyi ba. Kansa ya dafe yana yamutse fuska. Sai kuma yayi bissmillar sannan ya cigaba da ci. Da yake yunwar yake ji sosai yaci ya kuma sha fruit salad ɗin shima sannan ya koma bathroom yay brush ya fito. Kansa tsaye ya nufi gadon zai kwanta sai kuma ya tsaya cak yana kallonta. Gefen lips ɗinsa ya ɗan ciza sai kuma ya ƙarasa ya ɗauki pillow biyu ya koma saman sofa ya kwanta. Bawani yaji daɗin kwanciyar bane ba kasancewar bai saba kwanciyar a hakan ba. Iska ya furzar kaɗan tare da lumshe idanunsa kawai.
Barcin ya ɗan jashi da nisa kaɗan saboda gajiyar da yayi aka fara masa mintsine-mintsine a jiki. Idanunsa ya buɗe kawai batare daya motsa daga kwancen da yake ba. Tun yana ɗaukar al'amarin wasa har dai yaji yau fa dabance, a farko ya ɗauka normal ne kamar kullum, dan ya jima yana fuskantar irin wannan yanayi amma jarumtarsa na tattare komai ta bizne saboda ya riga ya sakama ransa in har ba Ummie ta samu lafiya ya ganta a farin ciki ba baya jin yana da wani spiece a rayuwarsa na kallon wata mace da wannan siffar. To tayaya ma zai yarda hakan ta kasance. Ace mahaifiyarsa na kwance cikin lalura mai ban tashin hankali shi kuma hankalinsa nakan samawa gangar jikinsa abinda take buƙata. Kai impossible. Cikin cizar lips ya sake lumshe idanunsa a yanayin tilastama kansa kamar yanda ya saba. Dan shi bai taɓa shan wani magani domin hana faruwar haka ko samun sassauci ba. Ya dai riƙe azumi tare da takure kansa matuƙa saboda jarumta. Sai idan al'amarin yayi tsamarine yake amfani da lemon tsami bisa shawarar abokinsa Taj.. daga ba hakanba baya shan komai.
Cikin ƙanƙanin lokaci wata irin zufa ta gama jiƙe masa jiki, amma bawon ALLAH ko motsawa baiyi ba yana daga kwancen yana sauraren hukuncin UBANGIJI. Tsanantar al'amarin ya sashi yunƙurawa a karo na farko ya tashi zaune haƙoransa ya datse da lips ɗinsa kamar zai huda shi. Zaman ma gagararsa ya nema farayi, ya miƙe tsaye zuciyarsa na tsananin bugawa. Taku ɗaya biyu ya tsaya cak, saboda ƙullewa da cikin yay sosai ƙafafun ma kansu riƙewa suke. Ga idonsa ya sauka akan wadda ke kwance a saman gadonsa tana barcinta hankali kwance. Duk da ba ganin fiskarta yake da ƙyau ba saboda ƙarancin haske yanda tai luff cikin lallausan blanket ɗinsa ya tabbatar masa da hakan. Kansa ya kauda, sai kuma ya nufi Bathroom da ɗan yanayin sassarfa na tilastama kai jarumta. Babbar shower ɗin mai ƙarfi ya sakarma kansa. A cikin ƙanƙanin lokaci jikinsa ya gama jiƙewa sharkaf, sai dai ta saman kansa yayi amfani da shower cap gudun kada ruwa ya taɓashi yay mura. Dan shi bashi da wahalar yin mura. Sosai ruwan ya dakesa amma baiji komai ya canja ba. Sai ma sake ruruwa da yake jikinsa na sake tabbatar ma da yau ɗin fa yau ce. Cire kayansa yayi ya fito bayan ya ɗaura alwala. Sai dai raka'a biyun farko ma da ƙyar ya iya kaisu saboda yanda al'amarin ke sake ta'azzara. Shiru ya cigaba da zama a saman sallayar, kafin kuma dai ya miƙe da ƙyar. Saman gado ya tafi da nufin hawa sai kuma ya tsaya cak, karan farko ya zubama fuskar Samraah dake shaƙar barcinta a nutse idanunsa da suka juye gaba ɗaya. Ba wani tar-tar yake iya ganinta ba, sai dai yanayin ƙarancin hasken sai ya ƙara ƙawata masa ƙyawunta abinka da wanda ke cikin yanayi. A hankali ya fara takawa tamkar hawainiya mai tsohon ciki. Ya kai hannunsa duka biyu yaja igiyoyi biyu dake ɗaure da net ɗin da aka zagaye gadon tamkar rumfa. Cizar lips ɗinsa ya sakeyi yana mai duƙar da kansa tamkar wanda ke jin abinda zai aikata ba dai-dai bane. Har ya motsa jikinsa da nufin komawa sai kuma ya sake tsayawa cak sakamakon nauyin da ƙafarsa tai masa. Ga zuciyarsa na ƙara tabbatar masa da (Awwab matarka ce fa, ALLAH ya halatta maka miyyasa zaka cutar da kanka kaƙi karɓar ni'imar da yay maka. Kaje tareta, kaje) Da wani irin tashin hankali ya tura yatsunsa cikin sumar kansa ya harmutsata ya furta, “Ya rabbah Ummie! Ummie! Na, ban mata adalci ba. My ALLAH help me! I beg you”.
A dai-dai nan Samraah tayi juyi, bargon daya rufa mata har wuya ta janye ƙasa alamar ya isheta. Tamkar wadda ake juyawa da remote ta juyo sosai ta inda yake tana facing ɗinsa. Saukar idanunsa a saman ƙirjinta ya sashi runtse idanunsa da ƙarfi tare da cije lips ɗinsa har sai da ya fasashi da haƙori. Sai kawai ya zube a saman gadon hannayensa duk biyu dafe da kansa. Tsawon mintina ya ɗauka a hakan kafin zuciyarsa ta gama yanke masa shawarar mafita. Fitilar dake cikin gadon ya kunna tare da haurawa gaba ɗayansa.