Header Ads
Showing 27001 words to 30000 words out of 49729 words

Chapter 10 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

711

Ads at the middle of Article

ji fad'an Maminta. Ta gama had'ewa cikin gown lace ne mai adon golden da fari. Ta d'ora golden head sai 'yar jaka had'e da takalminsa da na mayafi.
Su Aisha da sauran abokan karatunsu na sakandire da jami'a sai 'yan uwa sun yi ankonsu suma sun fito d'as cikin golden lace, yayinda mazan sukayi ankon farin boyel.
Mami ta shigo ta d'ago ha6ar Bintu tana dubanta. Murmushi ta saki.
"Masha Allah, Allah Ya kauda idanun mak'iya akanki my daughter. Kinyi kyau, sai ki k'ara kame kanki banason rawa kinji ko?"
Bintu ta amsa kawai da to. Ina ta ga wani dama ta yin rawa a auren da ba wani so da d'aukinsa take ba?
Aisha ce tayi mata rakiya har motar angon. Ta saci kallon motar. Baka ganin wanda ke ciki, hakan yasa ta maida kanta k'asa. Kafin su k'arasa Bintu ta ja tsaki.
"Wallahi taraku nakeyi daga ke har su Anti Hajaran, zan rama d'aya bayan d'aya."
Jin abinda ta furta yasa Aisha darawa.
"Ashe fa d'an iska d'an iska ne ko? Oho dai, kafin kiyi mana ke muka soma yiwa."
Bintu ta yi kwafa.
"Lokaci."
Daga haka bata k'ara cewa uffan ba tana jin dariyar Aisha.
Aisha ta bud'e mata k'ofar ta shiga, wani sanyi ya ratsata had'e da k'amshi. Ta dubi gefenta, ajiyar zuciya ta saki ta kauda fuskarta. Ai 6ata lokaci ne ma idan tace yayi kyau, daman kyakkyawan ne. Saidai a yau kowa ya ganshi zai k'ara son ya k'ara kalla banda ita Bintun. Acewar zuciyarta kenan.
Muryar Hashim dake zaune wajen direba ya katse tunaninta.
"Ina gaisuwa amarsu."
Ta daure ta gaisheshi cikin sassanyar muryar da ya ba shi mamaki, ya saba jin Bintu da karad'i, bata da wani sanyi. Ya dai basar ta hanyar dariya kafin ya amsa ya had'a da fatan alheri. Bata amsa ba, alokacin kuma ya ja motar.
Shiru ya biyo baya. Can kuma ta ji wayarta ta d'auki k'ara. Ta ciro ta duba. Text message ne daga unknown number. Ta bud'o ta karanta.
"Kin ci nasarar zama matata, ina tayaki murna, fatan baki mance dukkan maganganun da na yi miki a baya ba?"
Ta dubeshi kad'an bayan ta kammala, wani shu'umin murmushi ya sakarmata mai k'ara sanya yanmata matowa a kansa. Ta kauda kanta, abin da ya ba shi mamaki ganin batayi niyyar ba shi amsa ba, k'arshe ma ta kashe wayar gaba d'aya ta jefa jaka.
Hashim ya danna rediyo nan kuma kid'a ya soma tashi jin da yayi shirun na motar ya isa. Haka har suka isa babu wanda ya k'ara cewa wani uffan sai shi da Hashim da ke d'an ta6a hira.






[7/19, 9:07 PM] ‪+249 99 715 2061‬: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<29>>


Sun isa har dab da k'ofar shiga hall d'in sannan Hashim ya faka.
"Ku jira kar ku fito, ina zuwa."
Ya fita daga motar. Ma'aruf ya dubeta, ba laifi kam ta yi kyau kamar ba wacce ya sani ba, duk kuwa da cewar ya ga wadanda suka fita a kyawun. Ya maida kansa ga kallon wajen. Yayi daidai itama ta juyo tana dubansa. Ji fa, namiji har namiji, amma zuciyarsa banda mugunta babu komai ciki.
"Jikina ya bani ana kallona."
Ta kauda kanta, a karo na farko tayi niyyar maida mishi martani.
"Ni me zan kalla a fuskarsa wanda babu shi a wajen..."
Bata kai ga k'arasawa ba sakamakon fisgo kafad'arta da yayi, wannan ya sanya fuskokinsu suka kusanci juna har suna jin hucin numfashinsu. Cikin kakkausar murya kuma mai k'aramin sauti ya soma magana.
"Ki bar gangancin gayamin dukkan wasu kalmomi da suka fito daga bakinki, idan kuwa bazaki kula ba zan ladabtar da bakinki wallahi."
Ya saki kafad'arta, ta matsa da sauri tuni ta soma k'ok'arin zubda hawaye. Ganin haka ya k'ara magana.
"Lallai kukanki na nufin na ci galaba akanki tun kafin a je ko'ina."
Jin abinda yace ya sanyata azamar share fuskarta.
"Ai ba kuka nakeyi ba. Kuma ma.."
Ta had'iye abinda tayi niyyar cewa tunano da abinda ya fad'amata a yanzun. Gane hakan da yayi ne, ya sanyashi murmusawa kawai baice uffan ba. A haka kuma sai ga Aisha tace su fito. Ashe kan 'yan matan da zasu shigar da su aka had'o. Can na hango dangin Rof na whatsapp a sun jeru suma babu wacce batayi anko ba, wannan ne dalilin da yasa dole aka barsu suka shiga jerin masu shigar da amarya.
Bintu ta fito, har aka zagayo da ita angon bai da niyyar fitowa. Shi kam hawayensa ya tsaya d'aukewa. Babu wacce ya tuno sai matarsa Ma'u. Masoyiya agareshi, bayajin har abada zai manceta. Allah Sarki rayuwa.
Hashim na shirin kwankwasa masa sai ya bud'|e ya zuro k'afafunsa ya fito. Bintu takaici ya hanata ma dubansa, idan yana wani yangar sai kace mace. Ita fa ta lura ajinsa har yayi yawa. Tayi kwafa a hankali kawai.
Ba tayi aune ba, sai jin tattausan hannunsa tayi a cikin nata, bai tsaya a rik'on ba har saida ya sark'esu wuri guda. Ta d'aga kai ta dubeshi, sai hasken flasher suka gani, tuni ya soma tafiya ta bishi cikin wani irin yanayi na sanyin jiki da rik'on ya janyomusu duka. A haka suke taku. Da ka gansu sai kayi zaton wasu taurari masu haske fiye da sauran.
Shi Ma'aruf yana takunsa cike da jin isa da k'asaitar shi d'in kyakkyawa ne kuma mai aji kwarai da kowace mace zataso ya kasance abokin rayuwarta. Ga Bintu kuwa, yangar daman ta zamto jiki agareta, haka tafiyarta take saidai ta yau ta bambanta da sauran. Sai wani shan k'amshi takeyi bata ko kallon mutane sosai ballantana ta damu da masu d'aukarsu hotuna. A haka har suka k'arasa mazauninsu.
Sai lokacin ta soma k'ok'arin zame hannunta ganin ba shi da niyyar sakinta. Shaf shima ya mance da wai hannun Bintu ya ke rik'e da, ya saki hannun bayan ya kalleta kad'an kawai.
Nan aka soma gudanar da shagalin biki, can na hango 'yan matan Zauren Karatu da DM har ma da Classic Ladies suna faman cashewa abinsu, kana ganinsu kasan basu da wata matsala asalima murna kwarai sukeyi game da wannan aure na Ma'aruf da Bintu. Bintu ta ja tsaki, wanda ya dira a kunnen Ma'aruf. Ya matso saitin kunnenta yanda zata ji abinda zai ce.
"Kika k'ara tsakin nan tsaka zaki zama."
Ta matsa gami da dubansa, ya d'aga mata gira kad'an da murmushin k'ularwa. Ta kauda kanta kawai tana mai tsuke bakin.
Can kuma aka tsaida kid'an, akayi addu'ar bud'e taro, kafin kuma a soma hada-hadar cin abinci.
Har aka kammala babu abinda Bintu ta sanya a bakinta sai lemo. Shi kuwa gogan babu laifi ya d'an ci abincinsa.
A k'arshe aka umarci Ango da amarya su fito domin yanka (cake), ya soma mik'ewa, abin mamaki ya k'ara mik'o mata hannunsa wanda ba k'aramin burge mutanen wajen sukayi. Ga iyalan Mami kuwa, su Rufa'i da Aisha abin ya basu mamaki matuk'a, haka suma su Atine su d'an dolo da suka san rashin d'asawar Bintu da yayanta.
Ta dubeshi, kallon idanunsa ne bataso, sanyaya jikinta yakeyi.
"Haba Amarya kina yanga, daure ki mik'awa angonki hannu." Cewar mai gabatarwar wanda ya bawa sauran jama'a dariya. Hum! Wai sai ga Bintu ta ji kunya. Ta d'aga hannunta ta d'ora a saman nasa ranta babu dad'i saidai jikin yayi sanyi. Ta mik'e suka soma saukowa. Mami ranta yayi sanyi matuk'a, addu'arta bai wuce yanda ma'auratan nan suka had'u ba, Allah Yasa aurensu yayi albarka.
Adda Ummi ce mai mik'a wuk'ar yanka cake, Ma'aruf ya kar6a. Bayan ya yanko ya sanyamata a baki, aka d'au sowa. Itama dakyar ta iya sanyamishi a baki bayan ta daurewa zuciyarta, abinda ya bak'anta mata bai wuce yanda har ya k'ara wani rik'o hannunnata ba.
Bayan sun kammala aka tsayar dasu, cikin fili, nan aka soma zuba musu ruwan kud'i. Can na hango matasan DM mazansu da matansu suna 6arin ruwan kud'i.
A haka aka tashi amarya ta dage Maminta zata bi. Ba takura kuwa, Mami ta ja ta zuwa motarta suka tafi tare da wasu k'annen Mamin.
Washegari aka gabatat da lakca, inda matan DDM da Khairin Nisa'i suka jagoranta. Da yamma aka shirya amarya za'a kai ta gidan mijinta...!
[7/19, 10:24 PM] ‪+249 99 950 1031‬: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<30>>
Zo kaga kuka da turjiya wajen Bintu. Ta rik'e Mami da Aisha gam! Har ta kusa sanya Mami kuka, Aisha kuwa ai ba'a magana. Abokiyar hirarta zata tafi ta barta. Dakyar Mami ta ja ta ta sanyata a mota bayan ta k'ara mata da nasiharta akan ta Abba da mahaifinta.
Har aka isa gidan kuka kawai takeyi. Haka Bintu tana ji tana gani kowa ya watse ya barta, ko k'awayen amaryar wadanda rabinsu 'yan uwana babu wanda aka bari bisa fad'in Mami.
Jin shiru yasa ta bud'e idanunta. D'akin Asma'u a baya kenan wanda ya yau yake mallakinta. Anyi fenti mai kyau, kayanta masu tsada. Ta numfasa, jin tsayuwar mota yasa ta mik'ewa da azama ta rufe k'ofar da muk'ulli. A fili ta furta.
"Naga abokan da zaka tattaro min su cikamin kunne da hayaniya."
To shima Ma'aruf d'in babu wanda ya janyo rakiya sai Hashim wanda shi ya tilasta masa suka biya siyo KAZAR AMARCI da sauran kayan sha.
Da sallama suka sanyo kai falon. Daman basu tsammaci ganin kowa ba a falon, don haka Hashim ya nemi wuri ya zauna. Ma'aruf ya harareshi ganin hakan.
"To me kuma kake nema?" Hashim ya sanya dariya.
"Ikon Allah, ka manta bisa al'ada abokan ango ke rakiya suma su tofa nasu addu'ar?"
Ma'aruf wanda shima ya nemi wajen zama, ya cire hularsa ya yamutse fuska.
"Look, ka tilastamin mun siyomata tarkace, ba kuma zan d'auki wani sabon abu ba bayan wannan kaji ko? Baruwana da wata al'ada. Malam ka tashi ka je Sally tana jiranka."
Hashim tun yana d'aukar abin wasa don kuwa a auren Ma'aruf na farko, har Ma'un ya kawo falon idanunta a rufe ya yi musu 'yar nasiha. Ganin haka ya watsar, ya bishi da nasiha daga nan kuma ya mik'e.
"To ai shikenan, mai yiwuwa kishi ke damunka. Bari na tafi, Allah Ya sanya alheri. A kuma ji tsoron Allah dai. Atoh."
Wani kallo kawai ya bishi da shi baice uffan ba. Ya mik'e yayi mishi rakiya har wajen motarsa.
Bintu tana jin dukkan abinda suke fad'a, ta ta6e baki, wai ma? Shi kansa bai isheta kallo ba yanzun balle kuma abokinsa.
Ta cire laffayarta ta wurga saman gadon. Wani riga da siket na farin leshi d'inkin ya kamata kwarai hakan ya k'ara fiddo zahirin zubin halittarta.
Ta fisge d'ankwalin, tana k'ok'arin zuge zip din rigar ne ta ji an murd'a k'ofar. Jin ta a k'ulle ya sanyashi soma bugawa a sannu.
Ta harari k'ofar ta cigaba da abinda ta soma. Shima daga bugu uku bai k'ara ba ya bar wajen, daman ledar zai mik'a mata, haka ya sanyata a firij ya fice zuwa d'akinsa bayan ya kashe fitilu.
Ita kuwa Bintu ta chanja kayanta zuwa riga da dogon wando ta nemi makwanci. A gajiye take sosai, hakan yasa ko mintuna uku bata ci ba bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Asuba nayi kuwa ta farka, wannan kuma sabon su ne, Mami ta sabar musu da tashi sallar asuba. Tana idarwa kuma ta lafke anan saman dardumar sai bacci, abinda ta kasa horuwa da shi kenan, hak'uri har fitowar rana.
Cikin baccin ne ta ji ana bugun k'ofarta tamkar za'a 6alla. Bintu ba dai nauyin bacci ba. Ta mik'e a firgice. Ga rana har ta fito kyal. Ba shiri ta bud'e k'ofar.
Ma'aruf ta gani sanye cikin farar jallabiya sai faman huci yakeyi.
"Wane irin wulak'anci ne haka ina bugun k'ofa bazaki bud'e ba, banda wannan ma, wanene ya baki damar rufe k'ofa?"
Ta turo baki.
"Gani nayi d'akina ne."
Ya watsa mata mugun kallo.
"D'akinki, ni kuma gidana ne. Ki ka k'ara gangancin rufe k'ofa sai na hukuntaki. Ba ki da abinda zan nema."
Ta dubeshi kawai cike da tsananin 6acin rai dangane da furucinsa. Ta kauda kanta tana mai tunanin abinda ya kamata tayi domin ramuwa. Ya katsemata tunani.
"Ki kunna wayarki, Mami na son magana da ke. Ki kuma yi sallah, don banga alamun kinyi ba."
Ya juya ya fice ya barta tsaye kamar an dasa ta. Ta ci alwashin Yaya Ma'aruf sai yayi dana sanin munanan kalamansa gareta. Tayi murmushi mai fassarori.
"Bintu ce fa." Cewar wani sashe na zuciyarta.
Ta juya ta koma ciki ta rufe d'akinta, saidai bata sanya muk'ulli ba.
Wayarta ta nufa kai tsaye ta kunnata. Kira ta dannawa Mami. Mami tana d'auka kawai sai ta fashemata da kuka.
"Haba Bintu, kukan na menene kuma? Meyafaru?"
Ta ja ajiyar zuciya.
"Mamina kewarku nakeyi wallahi." Ta fad'a a shagwa6ance. Mami tayi murmushi mai sauti.
"Muma munyi kewar Bintuna, saidai dole zamuyi hakuri saboda gidan mijinki shine babban gata da rufin asirinki. Shi kuma kad'ai ne wanda zai nunamiki so tamkar mu ko ince fiye da mu. Kinji ko?"
Bintu ta share hawayenta, lallai ma Mami, batasan abinda ya yi mata ba yanzun. Amma ai bakomai, Inna ta haneta kai k'ara kasafai. Itama ai ba kanwar lasa bace. Shine abinda ta barwa zuciyarta. A fili kuwa ta nunawa Mami ta gamsu, ta hau rok'on a kawomata hanif amma Mami tace ba yanzu ba sai an kwana biyu. Dole ta hak'ura.
Gama wayarsu, ta mik'e ta fad'a wanka. Bayan ta fito ta nufi akwatin da Aisha ta had'omata. Tsaki tayi, Aisha sai a barta, duk ta had'ata da manyan kaya bayan ta sani ko a gida ba damunta sukayi ba. Tayi ta d'age-d'agenta, can dai ta hak'ura ta d'auko wani atamfa ja mai adon fararen fulawoyi manya. Simple d'inki akayi masa na riga da siket saidai ya zauna sosai a jikinta. Ta k'ara fesa turare. Ta dubi kan gadon, kayan da ta cire babu linki, haka ta tattara komai ta linke ta gyara gadon gami da adana kayan sallarta.
Har zata fita falo ta tuno da batun d'ankwali, ba k'aramin aikin Ma'aruf bane ya zubamata rankwashi a kanta, ba don ta so ba ta d'auka, saidai koda ta tashi yin d'aurin batayi na kirki ba, sai wani da ake kira da Ture Kaga Tsiya. D'ankunne kawai ta sanya sai zobunanta, babu sark'a da abin hannu. Fuskar fayau babu kwalliyar kirki, acewarta wa zata yiwa?
Batayi tsammanin ganinsa a falon ba, saidai ga mamakinta yana zaune saman carpet yana karyawa abinsa. Mamaki tayi kwarai, ta shaida kulolin, daga gidan Mami suka fito. Ya dubeta duba na wacce bata isa ba ya kauda kansa fuskarnan tamkar wanda aka aikowa sak'on mutuwa. Shi fa ba'a kyauta mishi ba, ina shi ina Bintu ne? Wannan ta gama ganinsa ai ta cuceshi. Gwara suyita zaman doya da manja.
Ganin irin kallon da yayi mata ne yasa tayi murmushin mugunta. Kicin ta shiga ta d'auko kofi da cokali bayan ta d'aurayesu ta dawo.
Ta zauna d'an nesa da shi ta janyo flask na ruwan shayi fuskarta a sake.
"Wane irin d'an iskan d'auri ne haka kamar wata ka..."
Bai kai ga k'arasawa ba wayarsa ta d'auki k'ara. Saida ta kusan yankewa sannan ya d'aga tare da sanyawa a loudspeaker.
"Hello."
Bintu ta yagi kwai ta tura a baki batare da ta kalleshi ba.
Daga can ita kuma wacce ke akan layi ta fashe da kuka. Kukan da ya sanya Bintu kusan sakin dariya sakamakon wata k'atuwar murya da ta ji marar dad'in sauraro tamkar ba muryar mace ba saidai ta cije.
Shi kansa yayi mamakin jin ta da babbar murya haka, ashe kenan idan zasuyi magana da shi ne kawai take ragewa. Yau kam gayun murya babu shi.
"Prince ka cuceni, ka ci amanar k'auna. Ashe daman aure za'ayi maka da 'yar uwarka shine baka sanardani ba? Na shiga uku."
Sai lokacin Bintu ta gane ko wacece, itace dai wacce ta yi mishi rakiyar dole zance wajenta.
Ma'aruf ya d'an rarrasheta ta kasa shiru har ya gaji, ganin zai kashe wayar dole ta sauko. Yace ta kwantar da hankalinta, shi aure ai nufin Allah ne. A k'arshe kuma tayita rok'onsa akan ya shigo tayi mishi kallon k'arshe don itama zata koma Kaduna wajen yayarta.
Ya tabbatar mata zai shigo. Bayan sunyi sallama ya kwantar da kansa saman kujera ya lumshe ido kawai. Can ya tsinci muryar Bintu.
"Yaya, wallahi wannan matar 'yar yaudara ce. Bakaji muryarta ba? Allah Ya kamata, ranar da na raka ka zance tana ta faman k'ank'ance murya, yanzu kuma dubi yanda ta bud'e murya tana zuba kuka tamkar ana ruwan sama."
Yayi cak, ya kuma gaza bud'e idanunsa, gaba d'aya tunaninsa ya tafi ga matakin da yafi cancanta ya d'auka akanta. Ita kuwa wani sanyin dad'i ne ya dirar mata ganin ta kashe bakinsa. Ta kammala ciye-ciyenta a tsanake ta kora da ruwan shayi kafin ta mik'e ta kai kayan kicin.
Kafin ta kai ga juyowa, ta ji an cakumi gashinta da k'arfi. Ai tuni ta soma ihu.
[7/20, 1:55 PM] ‪+249 99 842 9948‬: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<31>>
Tuni d'aurinta ya kunce.
"Wacece

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads