Showing 30001 words to 33000 words out of 49729 words
Chapter 11 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt
mai k'atuwar murya?"
Ta sanya hannu ta rik'o hannunsa amma k'arfin ba d'aya ba, ko gezau yatsunsa basu motsa ba.
"Zan mutu! Don Allah kayi hak'uri Yaya."
"Daga yau kika k'ara kiranta mai k'aton murya ni da ke ne. Ke meye a muryarki?"
"Wallahi muryata tafi... Wayyo!"
Ta kasa k'arasawa adalilin k'ara jan gashin da ya yi.
"Au, ashe bakinki bazai mutu ba? Lallai idan zaman da kika za6a kenan muyi zaki d'and'ana kudarki."
Tuni ta soma hawaye. Ya saki gashin. Ya kama hanyar fita yana fad'in.
"Ki kammala ki sameni a falo."
Ta tur6une fuska ta bishi da harara.
"Duk abinda ka tanada nima shi na tanada gareka."
Bayan ta kammala wanke komai ta ajiye ta d'auki d'ankwalinta ta d'ora shi tana fad'in, ba zata fasa murza d'aurinta yanda ranta ke so.
Ta share fuskarta, ba fa zatayi saurin karaya ba, yanzu aka fara wasan tsakaninsu tunda bazai gaji da zaluntarta ba.
Ta fito da wannan takunnata mai cike da yanga. A haka ta k'araso cikin falon, idanunsa a kanta yana duban ikon Allah. Ta zauna saman kujera. "Ganinan."
Ya ja fasali sannan ya soma maganarsa.
"Inaso ki kiyaye bakinki. Ki kuma kiyaye dukkan wani abu da zaki janyowa kanki na d'ora hannuna a jikinki. Banason raini, shine kuma babban abinda yafi had'amu kema kinsani. Sannan kina sane cewar Ma'aruf ba k'azami bane ko? Sai ki kiyaye ayyukanki, daidai da d'akina da toilet ban d'agamiki k'afa ba."
Yana murmushi ya d'aga mata gira. "Ai amarya ce, bata buk'atar 'yar aiki yanzu."
Takaici ya isheta, ta dauke idanunta ta turo baki.
"Ni ko a gida fa bana wankin band'aki, Aisha ke yi."
Ya harareta. "Gida daban, gidan aure daban. Banason maimaici. Na gama maganata ok?"
Ta amsa da toh sanin halinsa. Ta mik'e ta bar falon.
Kan gado ta fad'a tana tunanin yanda zata soma rayuwar nan a gidan Ma'aruf.
Bata kai ga tunanin komai ba har ta ji tsayuwar mota. Da sauri ta mik'e ta lek'a. Wani ihun murna ta saki ganin wadanda ke fitowa daga motar. A guje ta fito, bata lura ko da mutum ko babu ba a falon, ita dai burinta ta bud'e k'ofa ta ji ta ajikin 'yan uwanta. Ba zato ta ji an dakamata tsawa wanda ya sanyata juyowa ba shiri.
"Menene hakan?!"
Kafin ta ba shi amsa suka jiyo sallamar mutane tun kafin su k'araso jikin k'ofar. Ta shareshi ta juya ta bud'emusu. 'Yan Rano ne, yanmatansu da iyaye amma duk ciki banda Inna. Da sauri ta rungume Aisha tana murna sai kuma ra fashe da kuka. Wata cikin su, mai suna Gwaggo Sadiya ta kama baki
"Haba kekuwa Bintu, menene abin kukan kuma?"
Ma'aruf na murmushi ya amsa a kunyace.
"Shagwa6ar fa gwaggo?"
Suka k'araso ciki suna dariya. Aisha ta ja hannunta zasuyi d'aki saidai wata gwaggonsu ta dakatar da ita.
"To kekuma haka akeyi? Baki bari ta gaishemu sannan kuyi sirrinku?"
Aisha ta saketa suna dariya. Ta k'arasa ta fad'a jikin gwaggo Sadiya sannan ta gaishesu.
"Bintu da son jiki. Ashe sai abinda yayi gaba."
Ita dai murmushi tayi kawai. Ma'aruf take duba yanda yake wani sunne kai shi a dole kunya ga surukai. Ya dubi Aisha.
"Ke me ya hanaki tafiya makaranta?"
Ta sosa kai.
"To Yaya ai ba wani abun akeyi ba."
Ya harareta.
"Kedai kinzo ki takurawa Amaryata da gulmace gulmacenku."
Akayi dariya, Aisha dariyarta da biyu ce, har da mamaki. Ta dubi Bintu kallon ashe an shirya. Bintu ta murgud'a baki gefe kawai ta watsar. Ta lura wannan ce sabuwar kissar da Ma'aruf ya 6ullo da ita. Tayi kwafa, ai kuwa zata nunamasa ta fishi iyawa.
Ta narke fuska tana mishi wani irin duba.
"Allah Yaya ba wata gulma zamuyi ba, kaima kasan tun jiya nake kukan kewarta."
Bataji kunyar furucinta ba, sai gwaggonnin ne sukaji, 'yan matan kuwa sukayi makwas suna dariya ciki-ciki. Shi kuwa gogan ya maze, lallai ma yarinyar nan, kawai sai ya mik'e a kunyace yana murmushi kamar gaske ya bar wajen bayan ya jefeta da kallon zamu had'u. Ta bishi da murmushin da ta saba idan tayi wata muguntar. A ranta kuwa tace "Yanzu ka soma gani indai irin salon da ka za6a mana kenan."
Bayan fitarsa, yanmatan suka kwashe da dariya, gwaggonnin kuwa mik'ewa sukayi suka zagaya d'akunanta biyu da kicin, daman basu zo ba.
Aisha ta samu ke6ewa da Bintu.
"Gayamin Tawan, ya lamura?"
Bintu tayi murmushi, ai itama tasan me takeyi, ko Aisha bazata bari ta gane komai ba.
"Ke na durzu a hannunsa, ashe daman duk wani jan ajin da yakemin na k'arya ne, ban dauka komai zai wakana ba tsakani."
Aisha ta saki baki.
"To ya na ganki garau?"
Bintu ta ja tsaki.
"Kefa 'yar iska ce, wayagayamiki dole sai na kwanta ciwo? Saida fa ya had'a da kuka da magiya na amince. Ya kuma dauki alk'awarin daina musgunamin."
Aisha dagaske ta yarda, ai sai tayi wata shewa da dariya. Atika ta dubesu.
"Anayi babu mu."
Aisha ta harareta. "Maganarmu ce ta aminan juna."
Bintu tayi dariya kawai. Wannan Aishar ma karatun litattafanta ya tashi a banza.
"Amma da banason fallasa don Allah."
"Tsakaninmu babu haka Bintu, don Allah ki k'ara zage damtse wajen janyo hankalinsa. Ga k'ananun kayanki can acikin akwati da sauran kayayyakin ma, na had'omiki. Kada ki yarda ki ba shi (chance) na k'orafi."
"Naji karki cikani."
Aisha tayi dariya.
"Zan taho miki da books."
Bintu ta harareta. "Sanin kanki ko a gida bana karatun Hausa ballantana a gidan aure."
Aisha ta k'ara numfasawa.
"Wallahi mamaki nakeyi, daman fa na zargi yaya yana sonki kawai yana k'ok'arin 6oyewa ne irin abinnan."
Bintu ta ta6e baki.
"Shiyasani."
Aisha tace "Bawani, kukasani dai, kema ai kina so kike wani sharewa."
Dariya kawai Bintu tayi.
Basu jima sosai ba suka tafi. Bayan tafiyarsu shima ya fice ko sallama baiyi mata ba don dagaske yarinyar ta bashi mamakin furucinta.
Har sukayi sati cikin wannan zama nasu na doya da manja. Ta koma makaranta abinta shima ya koma aikinsa.
A gajiye ta dawo gidan misalin biyar na yamma, bayan sun gaisa da Audu maigadinsu ta shige ciki. Anan farfajiyar gidan ta hangi motarsa a fake. Wannan ya bata tabbacin ya dawo. Ta k'arasa shiga ciki a zatonta ya k'ulle da muk'ulli saidai tana murd'awa ta ji k'ofar a bud'e. Baya falon, wannan ya bata damar zubewa kawai akan doguwar kujera.
"Wash!" Ta fad'a a fili cike da jin wata iriyar gajiya. Ta lumshe ido jin dad'in iskar fankar dake kad'awa. Ta kwashi mintuna kusan uku anan kafin ta mik'e ta k'arasa d'akinta. Ta rage kayan jikinta ta fad'a wanka. Saida ta fito ta shirya cikin riga mai k'aramin hannu T-shirt ja an rubuta Baby a jiki, da wando short bak'i ko gwuiwarta bai k'arasa ba. Wannan karon dai ta samu kitso wajen 'yar wata makwafciyarsu. An yarfa mata su k'ananu. Ta tufke da manyan ribbons biyu bak'i da ja. Hoda kawai ta shafawa fuskarta sannan ta fito zuwa kicin domin d'ora girki. Har lokacin baya falon saidai ta ji muryarsa yana amsa waya daga d'akin. Ta ta6e baki tayi kicin, tasan bazai wuce sauran cocaine ba(Sa'a).
Ta rasa me zata girka, a k'arshe dai ta yanke shawarar yin jellop din taliya. Ta soma aikin ne tana yi tana wak'e-wak'enta ta ji kamar motsin mutum a bayanta. Wannan ya bata damar juyowa ta dubeshi.
Ganin haka ya nufi firij yana k'ok'arin bud'ewa.
"Yaushe kika dawo?"
Ta yi kamar bata ji ba. Ya gama shan ruwansa sannan ya juyo gareta.
"Ban hanaki yawo babu d'ankwali bane?"
Tayi narai-narai da fuska.
"Wallahi Yaya d'ankwalin takura gareshi."
Ya dubeta duban da ace ba matarsa bace bai kamatu ba.
"Nikuma bazan d'auka ba a gidannan, sai ki wuce ki rufe kanki."
Kamar bazata ajiye aikin ba, dole ta ajiye ganin ba shi da niyyar barin wajen. Ta giftashi ta fita. Ya sauke ajiyar zuciya, bai bita da kallo ba, don ba shi da jarumtar nan. Saida ya tabbatar ta shige sannan ya fito ya koma d'akinsa.
Acan d'inma duniyar tunani kawai ya lula, saidai duk yanda zuciyarsa ta kai ga fahimtar da shi wani abu, sam ya k'i aminta balle kuma ya bata dama. Ya ja tsaki ya mik'e, bayason tunanin abinda bazai amfana da shi ba.
* * *
[7/20, 8:05 PM] +249 99 715 2061: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<32>>
Ta kammala tsaf ta zubo nata a filet bayan ta bar mishi nashi cikin flask. Kasancewar ba sallar takeyi ba, yasa ta zaman cin abincinta.
Ta soma ci kenan tana kallon wata tasha da ke hasko wrestling. A haka ya fito da zummar tafiya masallaci. Yayi mata kallo d'aya ya cigaba da tafiyarsa baice uffan ba. Ta bishi da kallo, wataran rashin son yawan magana irin na Ma'aruf yakan bata mamaki matuk'a. Kodayake daman bashi da hayaniya, bar shi dai da son girma. D'an hayaniya sai mutuminta, Yaya Rufa'i.
Bayan ya dawo ya zauna a falon alokacin ta kusa kammala cin abincin. Ya dubi abinda take kallo sannan ya dubeta.
"Bani remote."
Ta narke fuska.
"Yaya don Allah ka bari na gama kallo."
Ya yamutse fuska batare da ya dubeta ba don baya buk'atar cigaba da dubannata saboda dalilai.
"A matan ma bansan sunan da zan baki ba, me mace zatayi da wrestling idan na rashin abin yi ba? Malama bani na kalli abinda zai fissheni."
Ta mik'a mishi remote d'in ta d'auki filet tayi hanyar kicin ganin ya kamo Aljazeera. Daman ai ba yau suka soma fad'a akan tashar kallo ba.
"Ina abincina?" Bata ko juyo ba ballantana ta dubeshi ta amsa.
"Yana kicin."
"Kawomin."
Ta had'o mishi komai ta ajiye, zama tayi gami da janyo wayarta.
"Malama tashi ki suturta jikinki kafin zuciyata ta tashi."
Wani gululun bakinciki ya turnuk'eta, kai bafa zata amince da wannan cin fuskar ba. Dole ne tayi maganin Yayan nan.
Ta fasa zaman falon ta koma d'aki. Batasan sadda ta soma hawaye ba, kewar Maminta da Aisharta suka mamayeta. Yanzu da ace tana gaban Mami da duk wani abu da zai mata ba dai yayi a gabanta ba. Gashi kuma babu damar kai k'ara, to tace me? Alhalin ta riga ta nunawa Aisha komai lafiya ke tafiya tsakani. Ganin zata sanyawa ranta damuwar babu gaira babu dalili ne yasa ta janyo wayarta. Whatsapp ta soma k'ok'arin downloading, a baya sam bata chatting, tana ganin yanda Aisha ke haukar karanta books da kutsawa groups na matan aure amma ita ko a jikinta. Wannan karon kam, tayi niyyar somawa don ya d'ebemata kewa.
Bayan ta gama downloading, ya kammala updating contacts dinta da komai. Bata d'ora hotonta ba, tabar wajen fayau.
Dad'i ya cikata ganin Aisha online, hakanan da yawa daga cikin 'yan uwansu na Rano da 'yan uwan Abban Aisha ma duk sunayi. Kai tsaye ta yiwa Aisha magana. Aisha harda 'yar rawarta na murnar ganinta. Nan ta sanyata a groups, na matan auren ma ta sanya (Admin) ta sanyata ciki.
Nan ta soma ganin abubuwa, saidai tafi maida hankali a na 'yanuwansu na Rano. Suka isheta da shewa suna tambayar ya amarci. Ta biyemusu da dariya, koda suka tambayi mijin, sai cewa tayi gashinan yana mata tausa. Nan aka dauki dariya har da masu turo Audio. Kai Bintu ta rasa inda zata sanya ranta don dad'i. Ashe dai wataran zata ga amfanin chatting? Haka tayi ta biyemusu tana darawa.
Shima Ma'aruf bai k'ara bi ta kanta ba. Misalin tara ta ajiye wayar ta fito. Fitilun a kashe, sai hasken tv saidai waya yakeyi. Ta fahimci da abokin aikinsa yake yinta, ta wuce zuwa kicin domin d'aukar ruwa. Bayan ta fito ne yayi mata nuni da hannu wato ta kwashe kayan abinci. Kamar bazata tsaya ba, sai kuma dai ta dawo da baya. Yana wayan yana binta da kallo sakamakon hasken tv da ya hasketa. Ita kuwa kamar tasan yana kallonta ta wuce tana wata rausaya wacce da gayya ta yi ta.
Ai kuwa har da d'an mik'ewa zaune. Tuni kuma ya soma mance bayanin da sukeyi ta wayar. Ta gabansa ta shige da robar ruwa a hannunta.
Ajiyar zuciya yayi, ya runtse ido. Dole ya yiwa abokin aikinsa sallama ya tattara ya kashe kayan kallo ya fad'a d'akinsa. Yarinyar nan zai gargad'eta, don bazai lamunci ta dunga yi mishi yawo da duk suturun da ta so ba acikin gidannan.
* * *
Ita kuwa shigarta d'aki ta chanja zuwa kayan bacci doguwar riga mai d'an kauri saidai da kad'an ta wuce gwuiwarta, bata da nauyi. Daga haka ta kashe fitila ta kunna (gwamna ya gaza..lol)ta hau whatsapp bayan tayi male-male asaman gadonta. Kai tsaye group na matan aure ta lek'a, nan ta soma cin karo da sirrika kala-kala da akeson duk mace ta iya ta kuma sansu. Ta soma karantawa tiryan-tiryan. Ajiyar zuciya kawai ta saki, wai ana nufin itama zata iya yiwa Ma'aruf? Ta runtse ido ta bud'e, kai bata fatan har mutuwar aurensu wani abin ma ya had'asu. Ta yarda akwai sha'awa a rayuwa, soyayya ce dai ta kasa gaskatawa yana faruwa domin acewarta ita bai ta6a kamata ba.
"Toh idan kuma kika soma son Yaya Ma'aruf fa?"
Cewar wata zuciyarta. Ta ja wani iri. Kai Allah ma bazai jarabceta da wannan ba in sha Allah. Me zata so a wajen mutumin da baya sonta?
"Ni mugani ma ko yana online."
Ta fad'a a fili sannan ta hau lalube contacts. Baya online, hotonsa ta gani a dp hakan yasa ta bud'owa. Saida ta furta "Wow" a fili tun bata kai ga k'arewa hoton kallo ba.
[7/20, 10:42 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<33>>
Ta bud'o hoton tana kalla. Yana zaune cikin motarsa a mazaunin direba. Ya juyo har da wani tankwashe k'afafu, hannunsa na dama dafe da ha6arsa yana murmushi har da wani k'ank'ance idanu. Ya gama had'ewa cikin lemon-green na shadda ta sha aiki. Farar hula ce mai adon lemon-green a saman kansa. Ta bishi da kallon tsaf, tasan yanada kyau, bayan wannan ma, yana da wasu nagarta na mutunci da yake nunawa jama'a da dukkan wad'anda yakeso kad'ai, amma idan bai k'aunar mutum, to fa anan ka shiga uku. (Atunanin Bintu kenan).
Sai kuma ta tsinci kanta da fad'awa kogin tunanin wanda ya d'aukeshi hoton. Ta k'urawa hoton ido, anan ta gane alokacin Ma'aruf da k'ibarsa wuyansa a cike ba kamar yanzun da ya rame ba. Hoton zai dan kwana biyu da alamu. To kodai Hashim ya d'aukeshi? Sai kuma ta girgiza kai, ba zai kashewa Hashim idanu haka ba. Ta yi jim, sai kuma ta ja tsaki ta kashe wayarta. Me zai sanya ta damu kanta da tunanin abinda bai dameta ba. Ta lumshe ido a haka bacci yayi awon gaba da ita.
Abinda ya bata mamaki bai wuce yanda tayi mafarkin Yaya Ma'aruf ba, wai gashinan ta tsareshi da tambayar wacce ta daukeshi hoto har ya kawo mata duka.
Koda ta farka, sai mafarkin ma ya bata dariya da haushi. Lallai jiya ta ci ta k'oshi.
Washegari ya kama asabar babu makaranta, wannan yasa dukkansu babu wanda ya taka waje. Lokacin k'arfe sha biyu na rana ta kusa saidai Ma'aruf ko falon bai lek'o ba, haka itama Bintu, tana kammala gyare-gyaranta ta koma d'aki abinta ganin bai tashi ba ballantana ta gyara.
Sai wajejan sha biyu da rabi ta ji fitowarsa falon. Anan kuma ta ji yana kwala mata kira. Ta ajiye wayar da take dannawa ta fito.
Yana zaune ya hard'e kafafunsa a saman tebur, yayi wankansa yana sanye cikin riga ja da wando fari na jeans. Kallo d'aya yayi mata ya had'e rai. "Wai ban hanaki yin shiga anyhow a gidannan bane?"
Ta dubeshi sannan ta dubi abinda ke a jikinta. Doguwar riga ce 'yar kanti saidai tana da fiddo halitta kwarai. Ta turo baki kad'an sannan ta zauna tana dubansa kad'an.
"Wallahi Yaya kaima kasan manyan kaya suna takuramin a rayuwa. Ko a gida bana sanyawa."
Ya furzar da iska kawai, bazai iya fitowa ya sanarmata dalilinsa ba. Shi kansa yana jin ma kunyar tuna wai surar yarinyar da ya raina ke d'an hargitsa shi ba.
"Kawomin breakfast."
Ta saci kallonsa tayi murmushi lokacin da ta mik'e. Ai tasan manufarsa ta hanata sanyawa. Ita fa ba yarinya bace. Tana shiga kicin tayi kwafa.
"Lallai zakayi ka bari." Ta ayyana a ranta. Ta k'udurta a ranta ba zata bar shiga irin yanda ta so ba don ko a can gida ma bata fasa ba.
Ta had'omishi kayan kari ta fito. Ya sauke k'afarsa saman teburin ta ajiye sannan ta koma ta zauna. Ya d'an dubeta kawai ya basar, ya soma k'ok'arin had'a tea.
"Yaya, baka kewar Hanif? Don Allah ka rok'i Mami su dawo nan."
Ya d'an ji sanyi a ransa. Kamar bazai amsa ba sai kuma yayi magana.
"Munyi magana da ita jiya, zan iya tahowa da shi a yau."
Haba Bintu ta hau murna har tana washe hak'ora.
Yana lura da yanda tayita faman shige da fice, daga d'akin