Showing 6001 words to 9000 words out of 49729 words
Chapter 3 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt
Jss1 aka ajiye Bintu, zatayi repeating. Ita kuwa Aisha ta wuce Jss3.
* * *
BAYAN SHEKARU BIYAR...!
[7/20, 9:56 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<08>>
"Mamina!!"
Budurwa mai shekaru sha tara cif a duniya ta fad'a cikin d'aga murya alokacin da ta shigo falon a guje.
Mami itama da sauri ta fito daga kicin tana mai cike da murnar ganinta. Ai da sauri ta k'arasa gami da fad'awa jikinta tana dariya, Mami tayi mata kyakkyawar runguma tana murmushi mai bayyana hak'ora kafin ta d'agota.
"Bansan yaushe zaki ajiye shiriritar nan ba."
Budurwar ta turo baki.
"Kingani ko? Daman nasan yanzu za'a soma takuramin a gidannan. To dai babu inda zan k'ara tafiya, atoh."
"Inji wa? Sai mu turaki can k'auyen Rano kije can ki cigaba da haukanki."
Cewar Rufa'i wanda ya shigo mata da akwati, Aisha na biye da shi.
Sukayi dariya har Mami. Bintu ta dubeshi da fararen idanunta masu kyau manya da su. Ya harareta a wasance, ta dauke kai tana fad'in.
"Tab, ai dai dad'in abin bana gudun Innata. Kuma matarka ai itama a k'auyenmu ka kwasota."
"A'a malama, Hajara ta fiki kyau da wayewa. Kin manta da yanda kikayi karatun?"
Duk wannan maganar suna yinta ne a tsaye. Sai lokacin kuma suka zauna ana dariya. Idan da sabo, ya saba da tsokanar da Bintu ke yiwa Hajara matarsa. Kasancewar kusan sa'anni suke, kuma itama 'yar gida ce. A yanzu ta kusa haihuwa, har lokacin kuwa Ma'u ko 6ari bata yi ba. Allah bai kawo haihuwar ba.
Bayan shigarsu d'aki, Bintu ta dira saman gado ta saki k'aramin ihu.
"Home sweet home, shikenan babu k'ara kwana a makaranta, ba wani takura kai da karatu."
Aisha ta d'aka mata duka.
"Karatu yanzu kika soma, wa zai je miki jami'ar?"
Bintu tayi murmushi mai k'ara fiddo tsantsar kyawun fuskarta.
"Ai gwara jami'a tunda jeka ka dawo zanyi, ke nifa banason kwanan makaranta, wai da yaya na kammala? Ni abu d'aya ma nakejin haushi yanzu."
Ta yamutse fuska tana mai zame d'ankwalinta, hakan ya tona asirin gashinta wanda ko kusa bata shafawa relaxer, yana d'aure da ribon, ya cika taf saidai babu tsawo.
"Wannan yayan naki mai kama kwara."
Aisha ta zaro ido, "Au, iskancin naki har ya kai ki kirashi da kwara? Lallai ma, baruwana."
"Abinda yafi haka ma ai zan kirashi. Mutum babu walwala, sai wanda kakeso kad'ai ke ganin hak'oranka. Ji dan Allah idan yana gaban wannan siririyar matar tasa kamar a hure. Ke nan da kike ganina har na mutu bazan ta6a taka gidansa ba. Banje ba ina k'arama ba ballantana kuma yanzu da na k'ara sanin ciwon kaina? Hum um!"
Aisha tayi dariya.
"Kuma wallahi Anti Ma'u tana damuwa sosai akan rashin zuwanki. Amma tana tsoron rashin kunyarki ne shiyasa itama bata shiga harkarki."
Bintu ta yiwa Aisha wani kallo.
"Ita Ma'un ta gayamiki haka?"
"Kai Bintu, Ma'u babu Anti ma?"
Harararta tayi kamar idanun zasu fad'o.
"Na fad'a d'in, munafus jeki ki gayamata. Toh wallahi ko mijinta ke kanki kin sani rabona da ganinsa tun ina Ss2 ballantana kuma ita. Kin tuna ko ancemin gashinan a falo bana fitowa indai ina gidannan nazo hutu ballantana wata matarsa. Amma gobe zakimin rakiya gidan Yaya Rufa'i, kinsan shine nawa."
Aisha dake kallonta ta ta6e baki kawai.
"Kanki akeji."
Dariya kawai tayi ta mik'e a saman gadon ta hau rage kayan jikinta tana wak'arsu ta 'yan bodin na rabuwa da sukayi. Nan kuma hirar ta koma ta rayuwar makaranta, suna yi suna darawa abinsu.
* * *
Bak'a ce, saidai bak'inta mai shek'i da kyawu ne, kana ganinta kasan tana hutawa. Doguwa ce ba can sosai ba, tana da 'yar k'iba hakanan tana da diri mai kyau da burgewa. Hancinta bai cika sirantaka ba, ba kuma zaka sanyata a layin marasa hancin ba(Lol). Tana da magana(Idanuwa) masu k'arawa fuskarta kyau. A yanzun tana da shekaru goma sha tara cif a duniya.
Tana sanye da leshi ruwan madara, anyi mata d'inkin riga da siket da ya kama jikinta ya zauna d'abas. Taci kwalliyarta.
Fuskarta a tur6une, tana tsaye daga bayan kujera.
"Kinji abinda nace ko?"
Ta kauda fuskarta daga kallon Mami.
"Naji."
Aisha wacce dariya ta so su6uce mata, dole ta maida shi sakamakon kallon da Mamin ta jefomata.
"Shikenan, kuje, a kula da abin hawa."
"To Mami, sai mundawo "
Cewar Aisha, Bintu dai tayi gaba. Haka kawai Mami ta sanyata zuwa gidan Ma'aruf dole, ita kam batasan meyasa Mami ke son 6ata ranta akan wanda bai damu da harkarta ba itama bata damu da shi ba.
A cikin adaidaita sahu, dole ta saki fuskarta tana hira sakamakon Aisha da ta tunano mata wautar da tayi a baya kafin tariyar Ma'u a gidan Ma'aruf. Itama dole ta biyemata suna dariya wanda suka saba duk sadda suka tuna wani abu cikin wautar da Bintu tayi.
"Ke, ni sai yanzun ma nakejin kunya fa, hm, Allah Ya kyauta shirmena dai."
"Amin, ai gwara ki dunga yiwa kanki addu'a."
Ta ta6e baki.
"Mu soma zuwa gidan nasa banaso mu dade, kinga sai mu fito mu nufi gidan Yaya Rufa'i."
Aisha murmushi kawai tayi. Dayake ba nisa, nan da nan suka isa. Bayan sun sallami mai napep suka rankaya ciki.
Maigadinsu ya bud'e suka shiga. Ta dubi harabar gidan, bashi da wani girma, amma yayi kyau don an k'awata shi da shuke-shuke. Suka k'arasa ciki.
Falon ya had'u, abinka da 'yan boko (Lol), babu wani tarkace sosai amma fa an zuba kujeru masu tsada, hakanan kafet da labulaye. Babu kowa a falon sai Sa'ade yarinya mai shekaru goma sha uku dake taimakawa Ma'u da aiki.
Bintu ta zauna gami da d'ora k'afa d'aya kan d'aya sannan ta dubi Sa'ade.
"Ke, masu gidan basanan ne?"
"Suna nan."
Aisha ta dubeta. "Mu jira, nasan sun ji shigowarmu."
Ta ta6e baki gami da yin k'as da cingam dake bakinta.
"Minti biyar, idan basu fito ba sai mu k'ara gaba zuwa gidan karamci."
Harararta kawai Aisha tayi batace uffan ba. Bintu ta d'aga kafad'a alamun batasan tana yi ba ko a jikinta.
Suna zaune har suka ci mintuna uku, a fusace Bintu ta mik'e. Ta rattaba sallama cikin d'aga murya. Har sau uku. Zatayi na hud'u ta ji an murd'a k'ofar dake a bayanta. Wannan yasa ta fasawa. Ta juyo duk a zatonta matar gidan ce.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<09>>
Fuskarsa ba walwala kamar yanda ta riga ta sani. Yana sanye da singilet bak'a da wando (three-quater) fari k'al. Rataye a wuyansa, tawul ne. Ganin yanda d'igo-d'igon ruwa ya d'an kwanta a fatarsa ya tabbatar daga wanka ya fito.
Kallonta yakeyi ido cikin ido, hakanan itama fargaba ta hanata d'auke nata idon.
"Yaya ina kwana."
Maganar Aisha ta maidoshi tunaninsa, kallon da yake binta da shi na rashin sani ne ko mantuwa. Yasan kamar dai fuskar ba bak'uwarsa bace, saidai bazai iya tunano ko wacece ba.
Bintu ta koma ta zauna, maimakon ya amsa gaisuwar sai ya zarce ga abinda ya fito da shi.
"Ke wane irin mugun d'abi'a ne wannan? Idan kunga ba kowa falon ba zaku iya hakuri har matar gidan ta fito ba. Wace iriyar k'awa kika samu haka?"
Ya k'arashe yana maida kallonsa ga Bintu. Bintu ta dubi Aisha. Aisha ta amsa.
"Lah Yaya, Bintu ce fa."
Jin abinda tace ya sanyashi k'ara dubanta da mamaki. Ta cigaba da taunar cingam.
"Ina kwana."
Ta gaisheshi a tak'aice. Ya gyada kai.
"Ok, sabon rashin kunyar da kika koyo kenan a Boarding d'in? Toh ki kula, ina nan a Ma'aruf d'in da kikasani, ban chanja ba."
Daga haka ya juya zuwa d'aki. Ta bi bayansa da harara cikin k'aramar murya ta amsa.
"Nima Bintun da ka sani ce. Kuyi wani iskancin yanzu ku gani mana."
Suka tuntsire da dariya ita da Aisha.
"Kai Bintu, wallahi baki Smda kirki."
Tayi kwai da cingam kafin ta fiddo ta mik'awa Sa'ade.
"Yardar min. Ke kuma malama tashi mu tafi."
Ta mik'e ta soma kiciniyar yafa mayafinta. Kafin Aisha ta tanka, Ma'u ta fito cikin doguwar rigar atamfa, fuskar ta sha hoda da jan baki.
"A'a ya da haka? Bintu ina murnar ganinki kina yafa mayafi. Oyoyo."
Tana maganar ne cikin sakin fuska sosai. Bintu ta yamutse fuska.
"Ai naga..."
Sai kuma ta fasa maganar. Ma'u ga basu hakuri, suka gaisheta ta amsa kafin ta zauna ta hau tambayar Bintu game da makaranta. Jefi-jefi Bintu ke amsawa don kacokam ta mayarda hankalinta ga danne waya.
Ma'u ta maida hirar kan Aisha, wacce ke sanarmata sun d'anyi hutun makaranta. A k'arshe ta mik'e.
"Kuyimin hakuri bari na had'awa yayanku karin kumallo."
"Lah Anti bari mu tayaki."
Cewar Aisha tana mai mik'ewa. Tuni Ma'u takai k'ofar kicin, tana dariya tace. "Bari kawai nayi."
Aisha duk da haka ta bi bayanta, ta juyo don ganin ko Bintu ta taso, saidai ga mamakinta kamar bata san wainar da suke toyawa ba, k'arshe ma talabijin ta nufa ta kunna ta dauki remote ta zauna ta soma controlling. Aisha ta shige kawai ta kyaleta.
Hankalinta ya tafi a kallon wani series wai Saloni(gwalo) wayarta ta d'auki k'ara.
"Suhail." Shine sunan da ta gani
Saurayi ne k'arami wanda koda zai girmeta bai fi ga bata shekaru biyu ba, aboki ga k'awarta, Maijidda. Ta dubi k'ofar da Ma'aruf ya fito d'azu, babu alamun fitowarsa yanzun, hakan yasa ta d'agawa.
"To sarkin takura rayuwa, kaidai bansan wane irin saurayi bane. Babu kud'i sai afkin kiran waya ka cikani da 6a6atu."
Suhail daga d'aya 6angaren ya kyakyace da dariya, yana son bugowa Bintu ko don abin dariyarta.
"Amma kin raina ni wallahi, haba 'yanmata, a cikin samarinki goma da wuya ki samu biyu irina."
Ta yamutse fuska kafin kuma ta saki dariya.
"Waya gayamaka ina da samari da yawa? Kai d'aya ne na k'arfen."
Farinciki ya mamaye Suhail. Sun jima suna hira da wasa da dariya kafin tace ya kyaleta ya isheta da zuba. Bayan ta ajiye wayar tayi magana a fili.
"Banza, yaro da shi sai karambanin tsiya. Ni dama zai aikomin kati ya fiyemin wannan zantukan marasa alkibla."
Tana d'ago kanta sukayi ido hud'u da Ma'aruf tsaye, saidai bai k'arasa fitowa daga d'akin ba. Sanye yake cikin shadda fara tas. Ya d'ora' bak'ar hula a kansa. Kallonta yakeyi kallon tuhuma, gaba d'aya ta tsorata. Ta had'iye miyau.
"Yau babban yaya da la6e." Ta fad'i a ranta. Ya k'arasa fitowa ya zauna a gefenta kafin ya sanya hannu ya d'auki wayarta. Ya gama bincikensa a contact, abin mamaki sunayen da ta sanyawa samarinta ya bashi dariya sai murmushi kawai yakeyi. Akwai Banki, Malam K'eya, Sarkin Nanaye, sai Suhail 6a6atu. Ya dubeta.
"Abinda kikeyi kenan a makarantar? Duk a ina kuka had'u?"
Ta sunkuyar da kanta tana wasa da zobunan yatsunta biyu kamar wata saliha.
"Ni babu wanda na janyo."
Kamar yayi magana sai kuma ya barta, ya ajiye wayar ya d'auki remote.
"Ina Aisha?"
Ta tsuke baki. "Tana taya Ma'u girki."
Cikin tsananin mamaki ya dubeta.
"Ma...what?"
Sai lokacin ta tuna a inda take.
"Su6utar baki ne wallahi Yaya. Ina girmamata ai, Anti Ma'u."
Baice komai ba har ya kamo Al-jazeera. Ta yamutse fuska, ta mik'e. Ta gwammace ta koma kicin wajen su Aisha da dai ta zauna kallon wani Al-Jazeera.
"Zo nan."
Ta tsaya kafin ta juyo ta dubeshi. Shima ita d'in yake kallo. Gaba d'aya sai yayi mata kwarjini, ta tako a sannu ta zauna saman kujera inda ta tashi.
"Gani."
Ya k'ara murya kad'an.
"Zauna, ki dunga fassaramin abinda suke fad'a naji ko da gaske yanzun kin iya (English)."
Ta d'an dubeshi. Amma Yaya Ma'aruf ya raina mata wayo, lallai ma.
"Ina jinki."
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<10>>
Ta muskuta tana duban talabijin. Yau zata rainamishi wayo tunda abin nashi hakane.
Tayi tsai bayan ta gama fahimtar inda labarun ya dosa. Akan yara masu (kwashiorkor) ne, har gasunan ana nunosu ana jawabinsu. Ta turo d'ankwalinta gaba, kafin ta soma magana.
"Ana magana akan wad'anda k'iba tayi musu yawa ne, da ace duk zasu koma kamar wad'annan da kwarai sun ji dad'in rayuwa kuma..."
Ba zato ya sakarmata rankwashi a tsakar kanta.
"Banga amfanin karatunki ba. Tashi ki bani wuri kafin na kwasheki da mari. Dak'ik'iyar kawai."
Ta mik'e da saurinta ta nufi kicin d'in, tana shiga ta kwashe da dariya, Ma'u da Aisha na tayata kasancewar suna jin abinda ke wakana tsakaninsu.
"Baki da kirki wallahi. Kin raina mijina Bintun Mami."
Bintu tana 'yar dariya ta amsa.
"Atoh, ya cigaba da takurawa rayuwata ya gani."
Sukayi dariya. Sun riga sun kammala, ta ja kujera ta zauna tana dubansu yayinda suke jerawa saman babban faranti.
Tana ta afkin girgiza k'afa, d'abi'ar da Mami ta hanata. Ma'u kawai take k'arewa kallo ganin yanda fatarta ta murje ta k'ara k'iba sosai.
"Tab, Anti Ma'u wallahi ki rage k'ibar nan, nan gaba zaki iya illah."
A mamakince suka dubeta.
"Illa wace iri kuma?" Cewar Ma'u.
"Yanzu misali, Yaya Ma'aruf ya k'ara aure tsab zaki tomasheta,wannan duka d'aya da wannan mulmulallan hannun naki kin kasheta."
Aisha ta ji hanjin cikinta sun kad'a. Yau Bintu ta janyomusu, mai fitar da ita sai Allah. Ma'u tayi murmushin yak'e.
"Hum, ballantana ma bana tunanin Mijina na sha'awar k'ara auren. Sam, ba shi da wannan ra'ayin. "
Ta d'auki farantin ta fice. Dukan da Aisha ta d'aka mata a cinya ne ya maido da idanunta gareta ga barin kallon Ma'u.
"Kinsan abinda kike fad'a kuwa? Wallahi naga alama kina neman sanyamu cikin blacklist d'in anti ma'u. Yau mun shiga uku."
Bintu ta tsayar da ita ta hanyar yarfamata hannu.
"Ke dallah can kyaleni, ta sanyamu mana sai me? Nifa ba tsoranta nakeji ba. Ai duk laifinku ne, saida nace bazan zo ba kuka matsamin. Maganin kar ayi kar a soma."
Aisha dai tayi lamo kamar wacce kwai ya fashewa a ciki.
"Aisha!" Muryar Ma'u ya katse mata tunani. Ta zaro ido
"Shikenan, ta sanarwa Yaya."
Bintu ta ta6e baki ta bi bayanta suka fito.
"Kuzo ku karya mana."
Bintu ta girgiza kai.
"Nidai na k'oshi, Mami fa cikamin..."
Kallon da Ma'aruf yayi mata ya sanyata yin shiru.
"Toh Aisha fa?"
Aisha ta girgiza kai.
"Na k'oshi Anti, mun karya kafin mu fito."
Zama sukayi suna duban TV. Bintu sai afkin satar kallonsu takeyi. Sai hirarsu sukeyi akan abinda ya shafi ambaliyar ruwan da ake nunowa anyi a wani gari a Aljazeera.
Can kuma tayi magana.
"Yaya zamu wuce."
Ba tare da ya dubeta ba ya jefo mata tambaya.
"Daman ba yini kuka zo ba?"
"Eh, gidan Yaya Rufa'i zamuje."
Sai lokacin ya d'ago ya dubeta.
"Ba zaku bar gidannan yanzu ba tunda ba a kurkuku kuke ba, idan na dawo anjima da rana sai na saukeku."
Ran Bintu ya 6aci, ta daure dai ta had'iye 6acin ran sannan ta koma ta zauna.
Aisha bataso furucin Yayan ba, don gaba d'aya ta tsorata da Bintu, tana tsoron kato6arar da zata k'ara yi musu.
Saidai Bintu ta bata mamaki, sakewa tayi kamar batace komai ba, itama Ma'un bata nuna komai a fuska ba. Saidai har zuciyarta ta ji ta tsani yarinyar, ta lura tantiriya ce ta bugawa a jarida. Dole tayi takatsantsan.
Sai bayan da Ma'aruf ya dawo suka tafi. Bintu zaune a baya. Tana ji yana tambayar Aisha ko itama tana kula samari. Tayi kamar batasan wainar da suke toyawa ba.
Can ta d'ago kanta, suka had'a ido, ta sauke nata tana murmushi kawai. Ba koyaushe takeson magana ba.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<11>>
Yana saukesu yayi gaba bayan ya basu dubu d'ad'd'aya. Sukaui godiya.
Hajara uwar surutu, nan suka had'u sukayita zuba kamar ruwan famfo. Yaya Rufa'i baya gidan bai dawo daga ofis ba. Nan sukayita kyakyata dariyar abinda Bintu ta yiwa Yaya Ma'aruf da matarsa.
"Ke dai Bintu zanso naga mijin da zai kwashi shiriritarnan ta ki." Cewar Hajara. Bintu tayi dariya irin ta rainin hankali.
"Mijin Bintu? Tab, yana k'asar waje yana karantar masters yanzu."
Suka gwalalo ido.
"Waye?" Suka tambaya har suna had'a baki.
Ta dubesu kafin ta cigaba da rainamusu wayo
"Yana nan, kulkum muna waya. Duk randa ya zo k'asar nan, zaku ganshi."
"Mts, mak'aryaciya kawai."
Aisha ta fad'a bayan ta d'agota.
"Ina batun k'arya anan?"
Aisha tayi murmushi tana duban Hajara.
"Ai nasan halinta ciki da bai. 'Yar iska kawai, wallahi k'arya takeyi.'
Bintu ya kyalkyale da dariya.
"Ho ni, ranar aurena akwai rawa da gira d'aya." Suka dara.
Ranar sun jima cikin nishad'i har dawowar Rufa'i. Shima ya biyemusu sukayi tayi, saida Mami ta kira wayarsu sannan sukayi azamar tafiya, Rufa'i da kansa ya kaisu gidan.