Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 49729 words

Chapter 2 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

706

Ads at the middle of Article

kina wasa da Bintu."
Tuni ta zura tana k'ok'arin daidaita tsayuwarta. Aisha ta girgiza kai. "Wallahi ki chanja ki sanya d'ayan nan, ina jiye miki ki fad'i."
"Jikinki ko jikina? Kudai 'yan birni kun maida mutanen k'auye wasu da basu da wayewa. Tunda ke bazaki iya tafiya da shi ba sai ki bar wad'anda zasu iya suyi ai."
Daga haka ta nufi k'ofa tana taku gaba d'aya a takure.
"Ke muje."
Suka fito.
A nan farfajiyar gidan suka tarar da su Mami na k'ok'arin shiga mota. Abba yayi murmushi ganinsu. Suka gaisheshi.
"Lallai, yaran Abba sun fito. Kamar ba ku ba." Sukayi dariya kawai.
Ita dai Bintu da sauri ta fad'a mota sakamakon takalmin dake neman kayar da ita. Mami ta girgiza kai.
"Bakya ji Bintu, kinason wahalar da kanki."
Yaya Rufa'i yana dariya yace "Barta Mami, jiki magayi."
Bintu ta d'ago ido da zummar kallon Yaya Rufa'i, saidai cikin rashin sa'a suka had'a da Yaya Ma'aruf, abin mamaki yau kam babu hararar, kallon sak, kallo d'aya ya maida kansa ga tuk'i. Motar tayi shiru sai kabbara da kowanne keyi a hankali, wato(Allahu Akbar Allahu Akbar, La'ilaha Illallahu Allahu Akbar, Allahu Akbar walillahil hamd) kamar yanda sunnah ta koyar.
Bintu wacce bata iya sosai ba, sai mus-mus da baki. A karshe sai ma ta matsa daidai kunnen Aisha.
"Ke, wallahi Yaya Ma'aruf yayi min kallon arziki yau. Yayi kyau sosai."
Aisha ta harareta kawai, hakan yasa ta dauke kai tana kalle-kallen gari. Takalmi kuwa tuni ta tu6eshi tana hutawa.




[7/20, 9:56 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<05>>
Kuka har da sheshshek'a takeyi sakamakon marin da ta sha a hannun Yaya Ma'aruf a dalilin take mishi yatsu da tayi da takalminta, Mami bata ce komai ba ta bi mijinta wanda ya rigasu shigewa gidan, ba'a gabanshi akayi marin ba. Ita kanta yau Bintu ta 6ata mata rai, har kusan fad'awa tayi kan wata tsohuwa wajen idi, tsohuwa ba hakuri tayita 6a6atu, saida Mami ta sanya baki tayi shiru. Mami ta dakawa Bintu tsawa akan maza-maza ta cire takalmin ta rik'eshi a hannu saidai tayi tafiyar haka.
Bintu ta k'ara rushewa da kuka, tana murnar Mami bata doketa ba, yanzu gashinan ta takewa Yaya Ma'aruf yatsun k'afa ya mareta. Haka tayi cikin gidan, Rufa'i na kwala mata kira don ya rarrasheta amma ko juyowa batayi ba.
Tana zaune tana kuka da jaye-jayen Allah Ya isa, Aisha kuwa banda dariya babu abinda takeyumi mata. Tun Bintu na jin haushinta har itama ta hau dariya tunanowa da yanda ta dage akan takalmin. Tayi kwafa.
"Allah kuwa sai ma na tonamai asiri."
"Asirin me?" Cewar Aisha.
Bintu ta k'ara yin kwafa.
"Kedai ki zuba ido."
Kiran da Mami ta kwala musu ne ya katse hirar. Bintu tace ita babu inda zata je. Haka Aisha ta fice ta barta.
Bata fita ba saida Mami ta shigo da kanta ta d'an yi mata fad'a kafin kuma ta sauko tana rarrashinta, haka ta fito tana zum6ure-zum6uren baki. Anan saman kafet ta tarar da kowa har Abba anyi zaman cin cin abinci. Ta dubi Yaya Ma'aruf ta dauke kai, a ranta tana fad'in.
"Ai sai na tonamaka asiri kwanan nan, d'an iska kawai."
Abba na murmushi yace "Haba Bintu, wanene ya ta6aki? Zo ki gayamin."
Ta k'arasa ta zauna, saidai bata iya cewa komai ba ganin Ma'aruf.
Suka soma cin abin, Abba na janta da hira har ta sake.
Bayan sun kammala, ita da Aisha suka kwashe kwanukan suka nad'e ledar cin abincin sukayi kicin.
Ranar sun sha yawo tare da Rufa'i.
* * *
Washegari sai wajejan k'arfe goma Bintu ta farka. Ta kasa kunne sosai jin hayaniyar mutane daga falon Mami. Hakan yasa ta fito daga ita sai riga da wando na bacci. Ta d'an la6e, tana kyallara ido ta gane duk 'yan uwan Abba ne, babu wacce ta soma ganewa sai Anti Ma'u. Kwafa tayi, har cikin ranta ta ji dad'in ganinta, a fili tace "Yau asirinku zai tonu."
Ta koma ciki ta fad'a wanka itama. Bayan ta fito tayi kwalliyarta harda jagira irin k'atuwar nan saidai nata yayi girma da yawa. Ta dubi matar jikin kwalin eye shadow, ta dubi kanta kafin ta ja tsaki, ba iri d'aya bane kwalliyarsu. Cikin ikon Allah, sai ga Aisha ta shigo. Tana kallon fuskar Bintu ta soma kyakyata dariya. Bintu ta hau tayata.
"Don Allah zo ki yimin kwalliya wacce ta ci uban ta jiya. Yau zan nunawa wata bata da wayo."
Aisha ta saki baki ta kama"Toh, wacece kuma?"
"Baruwanki Malama, yimin don Allah."
"Goge, ke wanke fuskara gaba d'aya."
Da gudu-gudu ta fad'a band'akin ta wanko ta dawo ta zauna. Cikin kwarewa irin na Aisha, da baiwarta da Allah Yayi mata na iya tsantsara kwalliya tayi mata kwalliya gami da sanyamata eye-shadow wanda a baya sam Bintu bata amincewa ta sanya. Ai kuwa tayi kyau fiye da zato. Banda "Masha Allah, Subhanallah." Babu abinda Aisha ke ambata, ta k'arashe da "Wallahi kin fi koyaushe kyau tun zuwanki baki ta6a kwalliya irin na yau ba."
Bintu tayi farr da ido, kai kace wata budurwar azo a gani ce.
"Nasani." Aisha ta kai hannu zata goge mata ta kauce tana dariya.
"Au godiya zanyi fa."
Aisha zata fita ta tsaidata.
"Aramin wayarki." Ta mik'a mata ta fita.
Ta hau dannawa, gaba d'aya ta mance yanda Aisha ta koyamata daukar hoto. Ta dire wayar da zummar da zarar ta kammala zataje d'an dolo mai wankinsu ya koyamata don batason Aisha tasan abinda zata aikata.
Ta had'e tsaf cikin atamfa ja da fara, d'inkin ya zauna d'abas a jikinta, tayi d'aurin d'ankwalinta na sabo, ta sak'alo jelun wuyanta ta k'ulle. Cikin sa'a sai ga Aisha ta dawo d'akin, tana ganin haka ta gyara mata. Bayan fitarta, Bintu ta fesa turare ta janyo flat shoe din da Rufa'i ya za6omata ta sanya. Aganinta bayar da kai ne ta fad'i a gaban Anti Ma'u, ita daman sam jininta bai had'u da ita ba, sai kuma yanzu ta k'ara gano silar rashin had'uwar jininsu, 'yar iska ce.
Ta d'auki wayar Aisha ta fito da niyyar zuwa wurin d'an dolo.
¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<06>>


"A'ah Bintuuu!!" Fad'in 'yan matan kenan sa'anninta. Kasancewar gaba d'aya sun santa. Tayi musu murmushi kafin ta k'araso kamar wata mutuniyar kirki ta zauna. Nan suka gaisa, ko kallon Anti Ma'u batayi ba. Har saida Anti Ma'un tayi magana.
"A'a, Bintu yau abin ba magana?"
Sai lokacin ta d'an yamutse fuska tace "Ina wuni."
"Bazan amsa ba tunda saida na rok'a." Fad'in Ma'u cikin fushi, bata ga abinda ta tarewa yarinyar nan ba da ta tsaneta. Ta kusa daina shiga harkarta. Bintu ta mik'e tana dariya.
"Ina zuwa."
Bata saurari kowa ba ta fice daga falon tana wani jijjiga jiki a dole tafiyar Ma'u take kwaikwaya. Aisha dariya ta su6uce mata sakamakon ta fahimci ko da wa Bintun take. Ma'u ta gane saidai ta basar.
Tana fita harabar gidan fa nutsu ta soma tafiyarta sak. Ta dubi hagu da dama, bata hango d'an dolo ba, dole tayi gaba wajen maigadinsu. Yana ganinta ya washe baki. "A'a, d'iyata, wannan cakarewa haka?"
Bintu ta rik'e k'ugu tana murmushi.
"Nagode Baba, kasan inda d'an dolo ya shiga?"
"Ganinan!"
Cewar d'an dolo da babbar murya a sa'ilin da yake bud'e kyaure ya sanyo kai, hannunsa rik'e da mp3 yana jin wak'a.
"Yauwa, zo muyi sirri."
Tayi gaba ya bi bayanta har zuwa wajen shukoki. Ta dubi kusa da su babu kowa, ta mik'a mishi wayar Aisha.
"Gwadamin yanda zan d'auki hoto."
D'an dolo yayi dariya.
"Kai, sau biyar kenan ina gwadamiki. Wane irin kwanya gareki?"
Ta harareshi. "Malam idan bazaka koyamin ba, bani waya."
"A'a yi hakuri." Ya soma nunamata yanda zatayi, kafin tace bari ta gwada. Ta nunoshi da wayar. "Gyara nayi maka hoto mugani."
Yayi tsayuwar DAB😜, ta kyalkyale da dariya kafin ta daukeshi.
"Lah kaga ya yi."
Suna cikin haka, Yaya Ma'aruf yazo wucewa. Ai da sauri D'an dolo yabar wurin. Ma'aruf ya bishi da kallo kafin ya maido dubansa ga Bintu cikin d'aurewar fuska.
"Ke, banyi miki gargad'i ba akan wasa da yaron nan ba ne?"
Ta turo baki, bata da niyyar magana don har lokacin bata bar jin haushinsa ba. Ya matso, ta matsa a tsorace. Ganin yana shirin cafkar kunnenta ya sanyata yin magana babu shiri.
"Wayyo, kwa.. Au, wallahi abu ya nunamin. Kayi hakuri bazan sake ba."
Ta k'arashe tana dafe da kuncinta. Ya zubamata ido cikin kallon raini. Ganin kamar bai wuce ba tayi magana.
"Anti Ma'u ma ta zo."
Jin abinda tace ya bashi dariya, hakan ya sanyashi murmushi mai ban sha'awa. Bintu bata ji. Tayi sak'ale tana kallon abin kamar a mafarki har ta saki kuncinta. Ai kuwa ya mintsili kumatun ya ja.
"Sa'anki ne ni?"
Daga haka ya saketa ta juya sai gida. A ranta tana fad'in.
"Yau zan sanyaka kuka ai." Ta k'arashe da dariyar mugunta.
Nan ta zauna ta saki jiki anata hira, sai gashi ya shigo.
Kowannensu ya gaisheshi. Bintu ta zubamusu ido kamar talabijin, sai wani murmushi suke sakarwa juna.
K'arshe yayi mata wata magana k'asa-k'asa sannan ya mik'e ya fita. Fitarsa da mintuna biyu, ta mik'e ta bi bayansa. Gaba d'aya manya da k'ananan 'yan matan irinsu Bintu suka saki shewa. Mami ta fito daidai lokacin tana tambayar abinda yayi musu dadi.
"Bakomai." Suka amsa. Bintu ta faki idonsu ta fice ta hanyar kicin. Yau kam komai zai shiga wayarnan. Kai tsaye ta nufi sashen Ma'aruf.
Sad'af sad'af take takawa a barandar har ta kai jikin k'ofar. Ai kuwa ta ci karo da takalmin Ma'u. Ta numfasa ta waiwaya bayanta. Babu wanda ke tahowa. Taji k'arar kid'a, wannan ya bata tabbacin koda ta murd'a babu wanda zai ji cikinsu.
Ta murd'a k'ofar ta tura a hankali. Ashe dagaske 'yan iskan abinda zasu kuma yi kenan. A tsaye ta hangesu ya yiwa Ma'u kyakkyawar runguma. Hannunta na rawa ta ciro wayar Aisha daga rigarta ta saita ta d'aukesu hoto. Har kala uku, ta ci sa'a akwai wanda fuskokinsu gaba d'aya suka fito sosai. A sannu ta mayar da k'ofar ta rufeta kamar yanda take. Babu wanda ya ji cikinsu sakamakon kid'an dake tashi.
Saida tayi nesa kad'an da wajen ta hau kyakyata dariya har tana rik'e ciki.
"Zakuyi bayani ne."
* * *
Misalin takwas na dare babu kowa a falon Mami bak'o, dukkansu sune. Har Abba yana zaune tare da su ana hira. Can sai ga Bintu ta shigo, bayan tayi zaman dirshan akan gado tayita bincike har ta gane yanda ake bud'o hotuna. Ta dubi kowa tana murmushi. Babu wanda ta ji dad'in gani kamar Ma'aruf. Ya dubeta ta sakarmai murmushi, shima fuska a sake yake kallonta. A yau yana cike da farinciki baison abinda zai dagula lissafinsa.
Ta k'arasa ta gaida Abba. Ya amsa fuska a sake.
Can ana hira Bintu ta katse ta hanyar kiran sunan Abba. Kowa yayi shiru yana dubanta.
"Na'am 'yar Abba, ya akayi?" Cewar Abban.
Ta dubi Ma'aruf sannan ta dubi Mami sai kuma tayi shiru.
"Bintu ya akayi? Yi magana mana." Mami ta fad'a.
"Daman wani iskanci akeyi a gidannan nakeso yau kowa ya ganewa idanunsa."
A tsorace Aisha ta dubeta, haka su Abba, abin ya basu mamaki.
"Innalillahi, a gidana? Me kika gani?"
Ta fiddo wayar Aisha ta bud'o hoton ta mik'awa Abba.
"Kagani."
Abba ya kar6i wayar yana dubawa. Nan da nan ya daure fuska gami da mik'awa Mami, mik'ewa kawai yayi ya nufi falonsa.
¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<07>>
Mami ranta ya 6aci, ga tsananin kunya da ta kamata. Ta rasa wa zata watsawa harara tsakanin Ma'aruf da Bintu wacce sam bata da wayo. Kunya ta sanyata mik'ewa bayan ta bar wayar anan ta bi bayan mijinta.
Ma'aruf ya sanya hannu ya d'auki wayar, tuni Bintu ta ja baya a tsorace. Gaba d'aya fuskarsa ta sauya kwarai, farar fatarsa ta koma ja. Ya dubesu. Da sauri Aisha tayi magana.
"Na rantse da Allah bansan abinda tayi ba, tace dai na ara mata waya."
Gadan-gadan ya nufi Bintu, ya damk'eta kafin ya kwasheta da lafiyayyen mari. Ai tuni ta fasa k'ara.
"Wayyo na shiga uku Innata!"
"Ma'aruf!"
Ya ji muryar Abba cikin tsawa.
"Saketa!!"
Dolensa ya saketa.
"Zo inason magana dakai."
Daga haka Abba ya koma ciki, Ma'aruf a kunyace ya bi bayansa.
Rufa'i wanda wayar ta koma hannunsa ya goge hotunan gaba d'aya, shi kansa a yau Bintu ta k'ona ransa. Ya ja tsaki ya girgiza kai.
"Bintu baki da wayo sam, bakisan ya kamata ba." Ya mik'e tsaye gami da duban Aisha.
"Daga yau sai naga wanda zai k'ara baku waya tunda amfaninta kenan a hannunku. Banda abin Abba ma, ina ke ina rik'e waya a shekarunki. Mts." Ya fice bayan ya jefa wayar aljihun wandonsa.
A can kuwa Ma'aruf ya sha fad'a kwarai. Abba yace dole Ma'u ta tare a d'akinta babu wani sai ta kammala SS3 kuma. Ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, a k'arshe ya gargad'eshi kada ya kusa yace zai k'ara ta6a lafiyar Bintu, yarinya ce.
Wajejan tara na dare, Aisha d Bintu suna d'aki babu mai kula juna cikinsu. Aisha tana fushi da ita akan ta sanya Rufa'i kwace wayarta, daman sam baya so aka bata wayar, ayau gashinan Bintu ta janyomata. Itama Bintu gaba d'aya haushinsu take ji ganin babu wanda ya goyi bayanta. Ga fad'an da ta ci sosai a wajen Mami akan d'abi'ar da takeso ta mayar da ita jiki, wato la6e. Kuma ta k'ara jaddada mata Ma'u matar Ma'aruf ce. Daga haka ta fice, ko uffan basu cewa juna ba da Aisha har bacci yayi awon gaba da su.
Sai zuwa safiya Aisha ta sauko, daman bata kasance mai rik'o ba. Itama labari ta samo wajen Mami cewa za'ayi bikin Ma'aruf bayan sati biyu. Har sunyi magana da Hajiyar Ma'un, itama ta nuna jin dad'inta.
Bintu ta mik'e zaune.
"Wai da gaske ba'ayi musu fad'a ba?"
Aisha ta ja tsaki.
"Banza, ai bazaki ta6a ganewa ba. Bud'e kunne ki ji menene aure."
Nan ta dunga yi mata karatu dallah-dallah. Bintu tayi shiru tana sauraro. K'arshe ta saki baki da mamakin inda Aisha tasan duk wannan.
"A'i wai ina kikejin duk wadannan?"
Aisha ta d'aure fuska.
"Na gayamiki banason wata A'i."
"Yi hakuri, gayamin."
"Kinga ga Rai Dangin Goro. Kuma ga whatsapp na matan aure ina ciki. Maman Faruk sunana ma. Amma ko Mami batasani ba."
"Kin shiga uku wallahi."
Aisha tayi dariya.
"Kuma k'awata Safiya Bingel ta koyamin ba."
Sukayi dariya kafin alamun tsoro ya bayyana saman fuskar Aisha.
"Allah dai ya rufamin asiri na jima da ficewa ciki, da bansan me Yaya Rufa'i zaiyi min ba."
Tun bayan faruwar lamarin, ko kallon inda Bintu take Ma'aruf baya yi. Hakanan baya amsa gaisuwarta, a k'arshe ma ya gargad'eta akan kada ta k'ara gaisheshi baya buk'ata. Sannan koda wasa ya k'ara ganinta a sashensu sai ya kakkaryata.
Itama tun lokacin ta shareshi.
Bayan sati biyu akayi 'yar liyafa sai yini na gida, Ma'u ta tare a gidan mijinta wanda babu nisa sosai da gidansu Ma'aruf. Hatta Innar Bintu wacce kanwa ce ga Mami, ta halarci bikin. Ta ji dadin ganin da ta yiwa 'yarta gaba d'aya ta chanja ta k'ara girma. Matsalar da Bintu ta gayamata guda d'aya, wato karatu. Ita ta gaji da zuwa makaranta gashinan kwata kwata bata da wani basira, bata mayarda hankali. Inna tayita yi mata fad'a, a k'arshe ta rarrasheta da nunamata wataran zata ji dad'in karatun. Jinta kawai tayi, amma sam bata so haka ba, a sonta Inna ta cewa Mami a kyaleta kawai. Babanta ma yazo, shima sai washe baki yakeyi ganin yanda Bintunsu ta koma. Yayita shi wa Mami da Abba albarka yana binsu da addu'o'i na alheri.
* * *
Kuka sosai takeyi, ta fito daga cikin motar a guje ta rungume Mami.
"Dan Allah Mami kiyi hakuri wallahi zanyi karatu, kada a kaini bodin bana so."
Mami ta soma karaya, saidai tana so taga Bintu tayi karatun addini da boko. Shiyasa koda Ma'aruf ya kawo shawarar kaita Bodin batayi musu ba.
"Kiyi hakuri Bintu, zaki dunga ganinmu lokaci zuwa lokaci, ga 'yar uwarki nan kuna tare. Kada ki damu kinji ko?"
Aisha ta lek'o ta windo tana dariya.
"Mami ki kyaleta, seniors zasu jibgeta a banza dole ta nutsu."
Mami ta harareta. Dakyar ta rarrashi Bintu, ta shiga mota. Rufa'i ya ja suka tafi.

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads