Showing 33001 words to 36000 words out of 49729 words
Chapter 12 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt
da Ma'aruf ya tanada don d'anshi kad'ai wanda aka k'awata da kwalliya da ya kamatu a d'akin yaro. Can kuma sai ta nufi kicin ta d'auko duster ta goge. Kallonta kawai yakeyi, hakanan kuma ya ji ta burgeshi. Yana so yaga ana son d'ansa Hanif. D'an soyayya kenan. Bintu kuwa, a wannan 6angaren ya tabbatar ba shi da matsala ko kad'an da ita. Tana son d'anshi.
Yana kammalawa ya fice gidan. Sai wajejan biyar na yamma Aisha ke tabbatar mata yazo ya taho da Hanif, zuwa lokacin ya sallami Atine da goma ta arziki, Atine har kuka tayi saboda murna.
Ai kuwa nan Bintu na jin sun taho ta mik'e ta fad'a kicin, har ta kammala tuk'a tuwon semovita miyar ku6ewa babu labarinsu.
Can kuma sai ta ji k'arar bud'e gate wanda ya bata tabbacin shine.
Ta bud'e k'ofar, bayan yayi fakin ya fito yana rik'e da Hanif a hannu. Yaron ya k'ara narka uban k'iba, ya k'ara wayo. Ga shi fari k'al da shi kamar mahaifinsa. A kammani kuwa, zuwa yanzu sai ka kasa bambance kamannin wanda yafi rinjaye, tsakanin babansa da mamarsa.
Sunayin sallama ta amsa da saurinta ta kar6i Hanif ta cillashi sama ta cafe tana dariya. Shima Hanif d'in ganin haka ya kyalkyale da dariya. Tuni ta juya ciki tana fad'in.
"Oyoyo d'an Mami."
Ya shigo da 'yar jakar Hanif ya rufe k'ofar. Kallonsu yakeyi domin kuwa alal hakika sun burgeshi. Yana zama ta dauki jakar yaron sukayi d'aki. Ya shafi sumarsa yana murmushi, lallai Bintu ba k'aramin so take yiwa Hanif ba
[7/21, 9:23 AM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<34>>
Bintu fa ansamu abokin hira. Ai kuwa bata fito falon nan ba sai bayan sun gama wasa da Hanif. Tayi mishi wanka ta chanja mishi kaya bayan ta shafa mishi hoda a jikinsa da fuskarsa, sannan ta sanyamishi riga da wando jikin cotton, na baccinsa. Ta dubeshi tana dariya irin wacce ake yiwa yaro na wasa.
"Inye, kaga bebina yayi kyau. Zo muje falo muci abinci."
Ta d'aukeshi, yana rik'e da d'an ball sai ihu yakeyi yana sanya bakinsa a jiki. Tayi mamakin ganin Ma'aruf zaune saman carpet ga filet a gabansa har ya kammala cin abinci ma. Ya hard'e k'afa yana kallon The Dr's a Mbc4. Ganinsu ya sanyashi juyowa. Nan ya mik'awa yaronsa hannu yana murmushi.
"Come to me my boy."
Bintu ta dire mishi yaron sannan ta d'auki filet tayi kicin. Jimawa kad'an sai gatanan ta fito rik'e da faranti itama ta zubo tuwo. Ta ajiye ta koma ta d'auko ruwan roba saboda Hanif, marar sanyi. Itama ta d'aukowa kanta pure water mai d'an sanyi-sanyi.
Ta dawo ta zauna.
"Zo mu ci abinci." Ma'aruf ya tankwashe k'afafu.
"Juyo da abincin nan zan ba shi."
Ta dubeshi, kai har takan yi mamakin irin wannan so da yake yiwa d'ansa. Ba musu ta juyo da filet din. Tana ci a yangance ne saboda wai tana gaban miji, ta ji ance ba'ason yin loma babba. A gida ma bata fiye yi a gabansa ba saboda tsoron fad'ansa, da dai Rufa'i ne, to shi kam babu kalar lomarta da baisani ba.
Bayan ta kammala ta ja baya tana shan ruwa.
"D'aukomin tissue a d'aki." Ta mike zuwa d'akin. Ta k'ara k'arewa d'akin kallo tamkar bak'onta. Zata d'auko ne, ta hangi BlackBerry dinsa da ke jone a chaji tana faman (vibrating) alamun dai kira ya shigo. Ta nufi wayar ta duba.
"Lawisa" Shine sunan da ta gani kawai, babu wani sakaye. Ai kuwa bata manceta ba, k'awar Yaya Abida yayar Ma'u dake yawon zuwa gidansu neman soyayyar Ma'aruf tana fakewa da duba d'ansa. Ta rik'e k'ugu, yau zatayi maganin shegiya ashe. Ta d'aga.
"Hello." Bintu tayi shiru. Sa'a ta k'ara magana.
"Haba Ma'aruf, so fa ba hauka bane da zaka dunga wulakantani, don kayi aure shikenan sai kuma ka daina kulani gaba d'aya. Me zakayi da yarinya wacce batasan rayuwa ba?"
"Uwarki da ubanki zaiyi dani."
Cewar Bintu a zuciye. Lawisa tayi shiru kafin tace.
"Ni zaki yiwa rashin kunya? Ina mai wayar?"
Bintu ta dubi k'ofa babu alamun mutum, ta cigaba da magana a hankali.
"Ya shiga wankan sunnah. Ke wai bakyajin kunya ne Lawisa, don yau bazan kiraki antin ba. Babba dake, iskancinki ya rasa kan wa zai fad'a sai tatta6a kunnenki(cewar bintu, don Lawisa bazata fi talatin da wani abu, ta girmewa Ma'aruf). Toh wallahi kika k'ara kiran mijina sai na bazaki a duniya na kiraki karuwa. Ai ina sane cewar ba son Allah kikeyimai. Idan kuma don wannan ne, karki damu, mace mai karfin mata goma ce ni."
Ta katse kiran da sauri jin Ma'aruf ya kwalamata kira.
"Na'am!"
Ta amsa murya a d'age, a fili tace.
"Shima Yaya Ma'aruf, ya rasa wacce zai kula sai Lawisa. Ai wallahi ko ni mace banga abin burgewa awajenta. Idan Yaya dan iska ne ya k'are a Lawisa ya ci baya wallahi."
Ta zari tissue ta fito tana masifa a zuciya, a gefe d'aya kuwa, ta ji dad'in yanda ta ci mutuncinta, daman ba tun yau take dakonta ba.
Ya jefata da wani irin kallo.
"Me kika tsaya yi?"
Fuskarta a sake tace "Babu komai."
Kamar yayi magana, sai kawai ya fasa. Ya kar6a ya gogemishi inda ya 6ata a jikinsa da baki. Ta dauke filet d'in ta maida kicin sannan ta kawo ruwan wanke hannu. Bayan sun wanke ta kai kicin ta zubar.
Ta tsaya tana dubansu, babu alamun dai Hanif yana jin bacci. Ita kuwa Allah Allah takeyi ta shiga makwancinta kafin ta6argazar da tayi ya fito.
Ta zauna don tasan sai an kammala koda zai shiga d'aki. Hanif ya rarrafo wajenta, nan kuma tabar batun kallo ta k'ara shagaltuwa wajen yi mishi wasa. Ta dubi Yaya Ma'aruf wanda yake satar kallonsu.
"Yaya, wallahi yanzu na rasa da wanda Hanif ke kama, idan na hango kamanninka sai na hango na mamansa."
Ya lumshe ido ya bude da murmushi saman fuskarsa.
"Kamannin wa kika fi hangowa?" Yayi furucin hankalinsa na ga tv. Ta k'urawa Hanif ido, sai kuma ta dago tana yiwa Ma'aruf kallon k'urillah. Sannan ta maido dubanta ga Hanif.
"Kaga hancinku d'aya, bakinku ma haka, duk k'aramin baki gareki. Idanuwan ne dai kamar na Mamansa."
Ya kwantar da kai jikin kujera yana dubanta da murmushi, Ma'aruf bai fiye hayaniya ba sai akan Bintu wacce ke sanyashi dole don muddin bazata kiyaye abinda baya so ba, to fa za tayita wahala a hannunsa.
Ta kauda kanta ganin ba shi da niyyar magana.
"Ai dole yafi kama da ni don na fi sonshi akan mamansa dama."
Bintu ta amsa.
"Allah Yasa dai kada ya dauko halinkuuuu. Allah Yasa da halayen Annabinmu (s.a.w) zaiyi koyi."
Abinda ta fada a farko ya fusatashi saidai jin kalamanta na k'arshe yasa ta d'aureshi, babu abinda zai iya ce mata.
Ganin ta tsira yasa ta yi mishi saida safe. Zata shige ya dakatar da ita.
"Ki kula, nasan kalar baccinki, muddin na lek'o naga kin danneshi ni da ke ne."
Bata ce uffan ba ta fad'a dakinta. Bayan ta ajiye Hanif ta fita ta dauko jakarsa da ruwan zafi a flask wanda ta dafa saboda shan firisocrim dinsa.
Kulle k'ofarta tayi harda mukulli, tasan yau ya shiga d'aki ya dauki wayarsa to babu abinda zai hanashi kusan ci mata zarafi.
Acan kuwa Lawisa an k'ulu an kuma ci alwashi akan Ma'aruf ko babu aure! Daman kamar Bintu ta sani, abinda ta fi bukata kenan da shi bawai auren ba.
[7/21, 1:45 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<35>>
A 6angaren Ma'aruf kuwa, yana shiga d'akin ya ajiye wayarsa k'arama marar tsada sosai k'irar Samsung, da ruwan shan da ya shigo da shi. Ya rage kayan jikinsa ya fad'a wanka. Bayan ya fito ne ya shirya cikin riga mai hannun singilet da wando iyaka gwuiwa na bacci. Alokacin ne kuma ya zare wayarsa daga chaji. Yayi mamakin ganin kira rututu na Lawisa. Kamar bazai kirata ba sai kuma ya kira, don baisan dalilin wannan yawan kiran ba duk da ba yau ta saba kiransa ba saidai muddin ta kira sau d'aya zuwa biyu bai d'auka ba bata matsawa kanta.
Bayan ta d'auka, yayi mata sallama, ta amsa. Kafin ya kai ga tambayar ko lafiya ta hau magana.
"Ka gargadi matarka ta kiyayeni, domin nafi k'arfin wulak'anci."
Yayi shiru kad'an, menene had'inta da Bintu kuma? Ya had'e gira.
"Idan zakiyi magana yanda zan fahimta kiyi, idan kuma bazakiyi ba, lokacina ba na shirme bane ok?"
Nan ta shiga zayyane mishi dukkan abinda ya had'asu. Kusan dariya ya so yi sakamakon kalaman da Bintu ta jefata da su. Har yakai ga murmushin mamaki. Wato har tasan wani wankan sunnah? Hum. Shi fa yana yi mata kallon wacce batasan komai ba.
"Kana jina kayi shiru!"
Ta fad'a ranta a 6ace.
"Duk abinda matata ta fad'a hakane anyi, kiyi hakuri banji dai dadin zagin da tayimiki ba, zan gargad'eta. Ya dace zuwa yanzu ki bar rayuwata Lawisa, ni na gayamiki bazan iya biyayya ga abinda kikeso ba, ba kuma zan iya aikatawa ba. Lokaci yayi da zaki kyaleni, daman ina kulaki ne ba don komai ba sai don girmemin da kikayi da kuma kaunar da kike nunawa d'ana kafin ki 6ullo da wannan batun naki marar kyawun ji. Kiyi hakuri Bintu bata kyauta ba da ta zageki wannan kuma zan gargad'eta."
Tayi shiru don takaici, kawai ta kashe wayar. Ya ta6e baki ya jona Samsung d'insa a chaji. Kamar ya je yanzun ya samu Bintu, saidai ya hak'ura zuwa gobe.
Haka ya kwana zuciyarsa babu ko d'igon damuwa.
Washegari tun tashin Bintu da asuba bata samu damar komawa ba adalilin Hanif, bataso ya tashi neman abincinsa. Tasan mai yiwuwa ya tashi cikin dare amma nauyin baccinta bai barta ta ji ba ballantana ta had'amishi abincinsa.
Tana farkawa ta had'a ta ajiye yanda zai d'an huce kafin ya farka.
Ta mik'e ta koma falon ta tsaftace har kicin, saida ta kammala komai misalin takwas da rabi ta d'ora abin kari. Kafin ta kammala Hanif ya tashi, ta koma gareshi, tana d'aukarshi tayi bandaki, daga zuwa cire famfas ta 6ige da yi mishi wanka, suna fitowa ta tuno da ruwan da ta dora. Da gudu ta direshi saman gado ta nufi kicin. Har ya k'one sauran kad'an, haka ta k'ara wani ruwan akai da Lipton. Ta fito tana jinjina kokarin mata. Haka suke fama ashe.
Ta koma dakin ta shirya Hanif cikin riga fara mai adon purple da bakin jeans bayan ta sanyamishi wando. Ta sanya mishi safa mai fari da purple itama. Ta d'ora mishi bif a wuyansa gudun kada ya 6ata jikinsa. Haka ta daukeshi suka fito falon. Anan k'asa ta zaunar da shi, ta koma ta dauko abincinsa da ta dama ta ajiye saman tebur sannan ta fad'a kicin ta kashe ruwan zafi ta juye a flask. Daman shi kadai ya rage mata tayi.
Ta jera komai saman faranti ta kawo ta ajiye saman tebur.
Sai lokacin ta samu nutsuwar dawowa ga Hanif ta shiga ba shi a baki. Ai kuwa ya hau sha da sauri. Ya bata tausayi, ta tallafi kumatunsa.
"Sorry bebina, na barka da yunwa."
Fatansa ta cigaba da ba shi. Saida ya shanye tas har yana gyatsa sannan ta bashi ruwa ta gyara mishi bakin ta cire bif din.
Bayan ta kammala ta mik'e. Saida ta gama gyara komai a kicin ta dawo ta daukeshi zuwa d'akinta, kayan wasanshi ta dauko ta dire mishi kayan wasa kala-kala. Nan kuwa ya rikice yayita iface-ifacensa yana wasa.
Ganin haka ta hau gyaran gado ta kwashe kayan wankinsu, saukinta akwai mai wanki. Ta ware na Hanif tunda kala d'aya ne bazai gagareta wankewa ba, ta hada nata a inda ta saba sati-sati ake wankewa.
"Bari na shiga wanka bebina, banda rigima." Baimasan tana yi ba, sai wasansa yakeyi yana jik'a kayan wasan da miyau.
Ganin su biyu ne kuma batason yayi rigima yasa ta bar band'akin a bud'e. Duk kuwa da cewar bata hangoshi, amma tafison ta dunga jinsa kada ya hau kuka.
Saida ta kammala wankan ta hau wanke mishi kayansa da ta cire.
Bangaren Ma'aruf kuwa, tara da mintuna ya tashi. Wanka ya soma yi ya zura jallabiya mai hula irinta 'yan Morocco sai dogon wando daga k'asa marar nauyi. Ayau kam koda zai fita baya tunanin fita da wuri.
Yana fitowa falon ya shak'i iska mai dadi, a 'yan zaman da sukayi ya tabbatar Bintu ba yanda ya d'auketa take ba, ba mai son jiki bace wajen kula da gida.
Ya hangi kayan kari a saman tebur, saidai kuma jin iface-ifacen yaronsa yana wasa ne ya sanyashi nufar d'akinta.
Anan tsakar d'akin ya tarar da shi yana wasa, ya k'arewa d'akin kallo, kafin ya sanya hannu ya dauki yaron ya cillashi sama yana dariya. K'arshe ya sakar mishi kiss a le66ansa. Yaron sai k'amshi yakeyi.
"Hey, ina Mamanka?"
Ya tambaya cikin kunnen yaron. Hanif sai dariya yayi kawai.
Jin dariyarsa yasa Bintu fitowa rik'e da rigarsa da ta matse, daga ita sai tawul, bai kai ga rufe cinyarta ba.
Ido hud'u sukayi da Ma'aruf, tayi azamar komawa ciki.
"Au Yaya kaine?"
Bai amsa ba don babu k'arfin amsawar, ya juya kawai ya fita daga d'akin zuwa falo.
Ya tsinci kansa cikin wani yanayi, lallai shi d'in bai zamo dutse ba, yana da buk'ata. Ganin Bintu a haka ya dagula lissafinsa, babu laifi yarinyar tana da abin gani a fad'a a jikinta.
Ya kai kusan mintuna biyar anan yana waya da Abba da Maminsa kafin ta fito, ajiye wayar kuma yayi daidai da fitowarta.
Kallonta ya jazamishi jin wani irin shock tun daga tsakar kansa har tafin k'afarsa.
Ya gaza d'auke idanunsa daga kanta. Wata shegiyar riga ce a jikinta wacce ta matseta. Hannun rigar d'aya irinta vest, d'ayar kuma hannun 3-quarter. Ruwan toka ce rigar, sai wando shima iyaka gwuiwarta bak'i mai kamar roba, hakan yasa ya kamata ya fiddo da zahirin halittarta. Sai hula da ta rufe kan da shi.
Ta sakarwa Hanif dake gefensa murmushi tayi kamar bata ga kallon da Ma'aruf ke binta da shi ba.
"Bebina, bari na shanya kayanka ko?"
A haka ta nufi hanyar waje. Sai lokacin ya dawo hayyacinsa.
"Baki da hankali zaki fita a haka?"
Ta tsaya, saida ta kammala murmushinta kafin ta juyo ta yi mishi wani irin narkakken kallo...
[7/21, 7:33 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<36>>
"Ya Ilahi."
Ya fad'a a ransa. Baisan lokacin da muryarsa ta sanyaya ba.
"Kada ki fita haka please."
"Please?" Ta maimaita a zuciyarta da mamaki. Yau kuma Ma'aruf ke bata oda harda rok'o. Sai kuma ta ji jikinta yayi sanyi.
"To a ina zan shanya?"
Ya kauda kai ga dubanta.
"Jeki zan sanya a shanya. Sannan please ki ringa suturta jikinki saboda aljanu."
Ta yi murmushi kawai sannan ta koma d'akinta. Tsalle tayi ta fad'a saman gado kafin ta tuntsire da dariya. Yaya Ma'aruf kenan, yana wasa da ita. Ta yi kwafa. Zaiyi bayani ne. Ganin ta soma jin yunwa ne yasa ta mik'ewa dole ta chanja shiga zuwa doguwar riga ta shan iska, jallabiyar mata. Ta fito, baya falon saidai ya sauke Hanif daga saman kujera. Abin ya bata dariya, ta had'a tea abinta ta soma karyawa tana yiwa Hanif wasa. Ranta fari sol, ganin mazan sun soma russuna, ashe ma abin a baki ya tsaya?
A d'aki kuwa, Ma'aruf ya shiga wani hali, dole saida ya had'a da fad'awa band'aki gami da sakarwa kansa ruwa. Kusan shekara kenan, shi d'in dai mutum ne kuma mai lafiya. Tunaninsa ya soma kuncewa akan Bintu. Ya soma jin wani abu a ranta yana tunani. Eh! Tunani kawai yakeyi, don ba shi da tabbas. Kawai ya dauki abinda yakeji da wani suna na daban wato sha'awa! Banda haka babu wani abu. Acewar Ma'aruf Abdullahi. Wannan ne silar share maganar Lawisa baiyiwa Bintu ba.
Da daddare tana ji tana gani ya shirya maida Hanif wajen Mami, ranta bai so ba saidai jarabawa zasu soma a makaranta gashinan babu mai rik'o. Akan hakan yace Mami ta nemar musu yarinya da zata iya rik'eshi su je makarantar tare ko su zauna gida har Bintu ta dawo.
Tun faruwar hakan sai ya zamana Ma'aruf ya rage zaman falon lura da yayi na zata fasa shigar kananun kaya ba. Ita kuwa wani sa'in ba da gayya takeyi ba, sai don hakan ya zame mata sabo. Tun bata rufe kanta har ta zo ta saba adalilin yawan tunasar da itan da yakeyi ta hanyar rankwashin kan.
Watarana tana zaune a falo, fitowarta kenan bayan ta idar da sallah. Ranar ya kasance juma'a. Sai ga shi shima ya shigo dawowarsa daga masallaci kenan. Tayi mishi sannu da zuwa.
"Shirya zamu fita."
Wani sanyi ya mamayeta, daman zaman ya gundureta. Tayi shiga ta manyan kaya. Leshi ne light blue dinkin riga da siket ya zauna d'abas a jikinta. Ta k'ara gyara kwalliyar fuskarta sannan ta yafa mayafi dark blue hakanan takalminta mai d'an tsini shima dark.
"Kina ina?"
Jin muryarsa yasa ta saurin d'aukar jakarta wacce ta yiwa ciko