Header Ads
Showing 18001 words to 21000 words out of 49729 words

Chapter 7 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt

Ads the beginning of article before Image

19 Jun 2024

710

Ads at the middle of Article

kenan?"
Ta d'an dubeshi, sai kuma ta sauke idanunta, gaba d'aya jikinta ya d'auki rawa. Fatanta Allah Ya mantar da shi abinda tayi mishi jiya kada yayi mata maganar. Ai kuwa dai alokacin baiyi d'in ba. Ya d'auki wayoyinsa ya shige d'aki. Nan ta zauna zaman jira, tun tana duba agogo har ta daina, idanunta tuni suka kawo ruwa ta soma zubar hawaye. Bakinciki da takaici duk suka bi suka addabeta, yana sane ya shanyata. Ta kwashi kusan rabin awa a zaune saman kafet d'in kafin ya fito daga d'akin. K'amshin turarensa ya daki hancinta, ta d'ago ta dubeshi ranta cike da jin tsananin haushinsa. Saidai kuma wani irin sanyin jiki ya ziyarci zuciyarta ganin yanda ya had'e iyakar had'ewa kai ka rantse injin matso kyau ya shiga. Sanye yake da farin boyel mai tsadar gaske, ya d'ora hula bak'a. Yayi kyau har ya gaji. Saidai ta gwammace bata dubeshi ba, don kuwa bai bita da komai ba sai harara. Baice mata uffan ba har saida ya nemi wuri ya zauna, takalminsa ya soma k'ok'arin zurawa.
"Kina sane da laifinki ko?"
Ya fad'a ba tare da ya dubeta ba. Ta saci kallonsa, ita kam duk ta tsorata.
"Don girman Allah Yaya kayi hakuri." Ta fad'a cikin muryar kuka, bil hakk'i ta tsorata ganin yanda koda wasa babu annuri a fuskarsa.
Baice mata uffan ba har ya kammala ya soma kashe futilu, ganin haka ta fito tana sharar kwallah har da sauke ajiyar zuciya duk a hangenta ta tsira.
Bayan sun isa wajen motarsa ta kama gidan gaba zata bud'e ya harareta.
"Koma baya."
Ta koma babu shiri, ai ita ko boot ne zata shiga matuk'ar ba zaiyi mata wani hukunci ba.
Ya saki kid'a lokacin da motarsu ta cilla titi. Tana kalle-kallenta a hanya, tun tana saka ran ganin sun iso Afficent har dai ta nutsu ta gane ba ma hanyar suka d'auka ba.
Fargabarta ta k'aru, gaba d'aya hankalinta ya tashi.
"Yaya ba hanyar muka yi ba kamar."
Baice mata uffan ba sai ma ya k'ara volume na rediyo. Ai kuwa ta soma kuka. Ya dubeta ta madubi ya dauke kansa yana mai sakin murmushin mugunta.
Bai tsaya ko'ina ba sai a wani k'aton gida wanda ko ba'a fad'a ba, kallo d'aya idan ka yiwa gidan zaka san akwai wani abu wai shi kud'i.
Bayan ya shiga yayi fakin ya rage muryar kid'an dake tashi. Wayarsa ya fiddo ya danna kira bayan ya bud'e speaker.
"Prince." Wata murya ta fad'a daga can 6arin, yayi wani murmushi na mugunta yana mai duban fuskar Bintu wacce take k'arewa gidan kallo ta madubi amma furucin da ta ji wata tayi ya sanyata maido hankalinta ga saurarensa.
"Gani nan a waje."
Daga can ta saki ihun murna.
"Wow!! Yau lallai ina da mugun sa'a. Ma'aruf da kansa a gidannan?"
Ya d'anyi dariya kafin ya amsa.
"Kika wuce 5minutes zan juya na koma inda na fito."
Ai sai ta d'an d'aga murya.
"A'a, na tuba don Allah. Ganinan fitowa."
Ya katse wayar. Bintu ta rushe da kukan bak'in ciki, tsabar ma rainin wayo yau itace ta zama 'yar rakiyar zance?
"Rufemin bakinnan."
Ya fad'a a hankali, dolenta tayi shiru. Ya d'an karkato yana dubanta.
"Ko tari ban yarda kiyi ba har mu bar gidannan wallahi, idan kikayi wani kwakkwarar motsin da ta fahimci kina motarnan sai kin raina kanki. Bani wayarki."
Da sauri ta mik'a mishi tana kokarin danne kukan da ya taho mata, wata irin tsana da haushin Ma'aruf kawai take ji.
Ya kashe wayoyinsu ya ajiye.
Mintuna uku kawai, sai ga wata budurwa kyakkyawar gaske. Fara tas da ita, ta ci ado har ta gaji cikin wani rantsesan yadi. Tana taku cike da yanga. Bintu sai kuka ya tsaya cak, shakka babu ta had'u iyakar had'uwa. Ita kuwa budurwar ko kusa bata ganinsu kasancewar gilas din tint. Ta k'araso, Ma'aruf ya bud'emata gefensa ta shigo ta zauna.
Nan ta bishi da wani sassanyar kallo.
"Prince ka shayar da ni mamaki, na kasa gask'atawa. Don Allah mu shiga daga ciki mana."
Ya d'an ja fasali kafin ya amsa yana wani yamutse fuska.
"No, kiyi hakuri, ina da uzuri ne banason na jima. Don kin damu da ganina ne na daure na zo yau."
Bintu fa ta ga abinda ya fi k'arfinta. Ashe daman haka mata ke yiwa Yaya Ma'aruf? Mamakin da takeyi bai wuce yanda wannan mace mai shegen yauk'i da ji da kanta ba ta marairaicewa Ma'aruf har tana rok'onsa ya dunga kulata ko yayane tunda mai sonka yafi mak'iyinka.
Ta saki ido da baki tana duban yanda shi kuwa yake faman shan k'amshi. Gaba d'aya ta samu abin kallo ta mance da batun dinner. Wannan shine karon farko da ta ji Ma'aruf ya burgeta...!!
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<23>>


Yana zaune gaban Abba domin amsa kiransa. Abba ya dubeshi.
"Ina sauraron ra'ayinka game da maganarmu ta kwanaki."
Ma'aruf ya k'ara yin k'asa da kanshi.
"Na amince." Ya fad'a da kyar, Abba ya ji wani farinciki ya lullu6eshi. Ya yi hamdala a fili kafin ya bi Ma'aruf da kyawawan addu'o'i. A k'arshe ya sallameshi.
Ma'aruf ya mik'e jiki babu kwari ya bar falon.
Kai tsaye falon Mami ya nufa. Tun kafin ya k'arasa ya jiyo dariyar Bintu da Aisha saidai na Bintun yafi na kowa d'aguwa. Takaici ya sanyashi fasa shiga ya juya ya koma sashensa. Wai meya kaishi amincewa auren wannan yarinyar ne? Wane su6utar baki ne haka?
Kai gaba d'aya ji yayi ya tsani kansa, ya tsinci kansa cikin yanayin 6acin rai da damuwa matsananciya. Ganin ba wani sauk'i ya sanyashi barin gidan batare da ya d'auki motarsa ba.
* * *
Bintu tayi shiru tana duban Mami wacce ke k'ok'arin zama gefenta a saman gado. Mamakinta bai wuce na kiran da Mamin tayi mata ba har da rufe d'aki da korar Aisha.
Mami ta soma da kiran sunanta.
"Fatima Bintu, takwara kuma d'iya awajena."
Bintu tana murmushi ta amsa.
"Na'am."
Shiru ya d'an biyo baya, ita kam tana jin nauyin ma gayamata maganar, saidai ba yanda ta iya tunda Abba ne ya sanyata jin ta bakinta.
Cikin hikima irin ta manya Mami ta soma da kwantar mata da hankali da nunamata lallai ita mai k'aunarta ce, ba zata bari a cutar da ita ta kowane hanya ba. Tana k'aunarta tamkar yanda take k'aunar yaranta. A k'arshe ta sanarmata da buk'atar Abba ta son had'ata aure da Ma'aruf har ta k'ara da sanarmata cewa Ma'aruf ya amince da aurenta.
Bintu ta ji gabanta ya mugun fad'uwa, Ma'aruf kuma?! Innalillahi!! Meyasa tunanin Abba zai kawomishi hakan? Ya zatayi da rayuwa idan har Ma'aruf ya kasance mijin aurenta? Idanunta suka ciko da kwallah. Mami ta kauda duba daga gareta cikin sanyin jiki tace.
"Bazan bari a kwareki ba Bintu, zan jiraki daga nan zuwa kwanaki uku, matuk'ar baki k'aunarsa, kada ki kwari kanki, ki fito fili ki sanarmin, bazan ta6a bari a aura miki shi ba. Ki tsayar da tunaninki wuri guda, ki kuma dunga addu'a."
Daga haka Mami ta fita daga d'akin batare da ta k'ara dubanta ba ballantana ta fahimci komai a fuskarta.
Bintu ta zame ta zauna dirshan a saman carpet. Yaya Ma'aruf fa?!! Me ya burgesu har sukayi tunanin wannan had'in? A rasa ma wanda za'ayi tunanin had'asu aure da shi sai mutumin da ya k'i jinin walwalarta? Koyaushe burinsa ya k'untata rayuwarta?
Abar batun haka ma, ta nunamusu wata alama na cewar aure take buk'ata ne? Eh lallai, sun bi son zuciyarsu kawai zasu yiwa d'ansu gata. To ai itama tana da nata gatan, don haka ba zata k'ara kwanan gidansu ba daga wannan rana, gobe Rano zata nufa.
Gaba d'aya tunanin Bintu ya birkice, kukanma babu sai ruwan hawaye kawai. Ranta banda k'una babu abinda yakeyi. Ba Ma'aruf d'in kad'ai ba, gaba d'aya gidan saida ta ji ta tsanesu.
A ranar haka ta wuni babu walwala, Mami na lura da ita saidai batace uffan gareta ba. Gaba d'aya itama ta ji ta damu, tayi da na sanin yi mata maganar nan, daman ita tasan da wuya abin ya yiwu. Da dai ace Rufa'i ne, wannan kam tana da tabbacin ba lallai ne Bintu ta k'i ba.
Gidan bai musu dad'i ba ko kad'an, daman Bintu ce mai rayamusu shi, yau ita kuwa babu kanta. Fuskarta tamkar an aikomata sak'on mutuwa.
Washegari da wuri ta fito, ta lissafa kud'inta zasu isheta hawa motar zuwa Rano. Kai tsaye kuwa inda zata sami motar ta nufa maimakon makaranta.
Inna suna zaune sai ganinta sukayi. Nan k'annenta suka hau murna. Umma kishiyar Inna batanan, hakanan Saifu da babansa suna kasuwa. Kallo d'aya Inna tayi mata ta fahimci babu lafiya. Abin akwai mamaki matuk'a.



[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<22>>
Ya kwashi kusan rabin awa kafin yayi niyyar tafiya, a hakan ma budurwar wacce ya kira da Sa'a bata so ba, haka sukayi sallama tana rok'onsa da ya k'ara dawowa. Abin har ya bawa Bintu haushi, ta k'ulu iyakar k'uluwa, dubu yanda mace ba kunya take karya murya, shi kuwa sai shan k'amshi, haka kawai ta ji wata muguwar tsanar Sa'a ta dirar mata. Can kuma dai tayi tunanin me zai dameta?


Bayan tafiyarta ya juyo ya dubi Bintu wacce sai lokacin ne ta tunano inda suka nufa, ta turo baki ta 6ata rai. Murmushi kawai yayi baice komai ba, ai kwalliyar ta biya kud'in sabulu, yayi ribas maigadi ya bud'e mishi (gate) ya fita.
Sun kusa Afficent ya tsaida motar a gefen hanya. Ta dubeshi, hannu yasa ya bud'e mazaunin gefensa.
"Dawo gaba, don ba direba kika ajiye ba."
Ta yi jim kamar kada ta fito sai kuma ta bud'e ta dawo ta zauna ranta a 6ace. Tsaf ta fahimci manufar kaita wajen budurwarsa, wato dai ya nunamata lallai akwai mata 'yan gayu da suka damu da shi fiye da zatonta.
Ya dubeta ya maida kansa ga hanya lokacin da ya sha kwanar da zata kaishi d'akin taron.
Suna isa ya mik'a mata wayarta, a fusace ta fice daga motar. Saida ya kammala kunna wayoyinsa sannan ya kashe motar ya rufeta ya shiga.
Tun kafin ka k'arasa cikin hall d'in kana jiyo tashin kid'e-kid'e. Tana k'arasawa ciki kuwa ta daburce ganin taron jama'a. Mafi yawansu, dangin Abba ne. Ta dawo baya da zummar kiran Aisha a waya. Sai jin maganarsa tayi a dab da kunnenta sakamakon k'arar kid'an da bazai barta ta ji maganarsa ba.
"Illar 'yan k'auyen kenan, ko shekara nawa zasuyi a birni, wayewarsu, suna ce kawai."
Daga haka ya zarce ciki, kai tsaye 6angaren maza ya nufa. Ta bishi da kallon takaici. Ji tayi an dafa ta ta juya, ganin Aisha yasa ta sauke ajiyar zuciya, ta kasa magana kawai sai ta soma kuka. Ganin haka Aisha ta ja hannunta suka nufi waje.
"Ke ina kuka tsaya? Ga Mami can cikin damuwa. Me Yayan ya yi miki?"
Bintu tayi kwafa. Ta kwashe labarin komai ta bata, Aisha abin ya so bata dariya jin yanda take faman kushe Sa'a, ita kam tasan wacece Sa'a, d'iyar wani d'an majalisa ce, tun kafin ma ya auri Ma'u tana sonsa yanzu kuwa bazawara ce ma mijinta ya saketa adalilin shaye-shayen da takeyi ya zamar mata jiki. Tasan ko a mafarki, Ma'aruf bazai ta6a auren Sa'a ba ballantana kuma a farke. Saidai kuma jin abinda yace mata yanzun ne yasa jikin Aisha sanyi.
"Kiyi hakuri, kinsan halin Yaya Ma'aruf, ba yau ya soma ya6amiki magana don kawai ya k'ular dake ba. Ke kika nuna kina da saurin fushi shi kuma anan yake samun damar yi miki son ransa. Ni yanzu ba wannan ba, muje Mami ta ganki hankalinta ya kwanta."
Bintu ta share idanunta gami da yin kwafa kawai, Aisha ta gyara mata inda ya 6aci, tana janta da zolaya har Bintu ta saki ranta suka shiga ciki.
Mami ta yi murnar ganinta kafin ta hau fad'an meyasa bata hau adaidaita ba tunda Ma'aruf d'in ya biya hira. Bintu tayi shiru da mamaki, ko kusa Ma'aruf baisan yayi k'arya ba babu kwakkwarar dalili.
Har aka tashi taron bata sanyashi a ido ba. Tun kafin ma a tashin ashe ya tafi, haka ta ji a bakin Rufa'i sadda Mami ke cigiyarsa.
Washegari da yamma aka mik'a amarya Hafsa gidan mijinta. Babu inda Bintu ta je, saboda makaranta, ranar a gajiye ta dawo lik'is. Agaban idanunta Mami suka wuce, tana kwance saman doguwar kujera bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita.
Dab da magrib, Ma'aruf ya shigo. Dawowarsa kenan daga ofis, tuni ya yi wanka ya chanja zuwa k'ananun kaya na shan iska.
Sam bai ko lura da ita a falon ba, duk a zatonsa, gaba d'aya gidan ne suka fice sai masu aiki ya rage da Atine da Hanif wadanda ya hanesu fita acewarsa, yaron ya gaji, kwana biyu kenan ana fita da shi.
Saida ya shiga kicin ya nemi Iya da ta d'oramishi ruwan shayi, sannan ya doshi falon. Alokacin ne idanunsa ya kai gareta.
Bacci takeyi, kallo d'aya zakayiwa fuskarta ka fahimci bata da wata matsala. Gashinta wanda ko kusa batason kitseshi ya mik'e tsaye kamar na mahaukaciya, ribon d'in kuwa tuni ya fad'i.
Daga ita sai vest da dogon wandon da bai matseta. Ya ja guntun tsaki kafin ya d'auki filon kujera a gefensa yayi jifa da shi saman fuskarta.
Bacci na Bintu fa, saida ya gwammace bai jefeta ba, juyin da ta yi yasa shi mik'ewa dole ya bar mata falon.
D'ayan falon ya koma ya jinginar da kanshi saman kujera yana mai lumshe idanunsa. Wani yanayi ne, wanda tunawa da Ma'unsa kad'ai kan janyo mishi.
Cikin k'arfin addu'a ya bagarar da tunanin ta hanyar buga game a wayarsa. Har Iya ta kawomishi ruwan shayin kamar yanda ya buk'ata.
"Ki tashi mai baccin nan, lokacin sallah ya kawo kai."
Ya fad'a yana duban Iya. Iya tayi 'yar dariya.
"Au, mutuniyarka? Bintu ko rigima, ai saida na hanata bata fasa ba."
Ta fice. Ta gabansa Bintu ta shige d'akinsu, bai ko dubeta ba. Bayan ta kimtsa ta k'ara fitowa cikin doguwar jallabiya da hula a kanta.
Tayi kamar bata ganshi ba zata fice.
"Ke bakisan ki gaida mutum ba?"
Har lokacin haushinsa takeji. A ciki ciki ta gaisheshi bayan ta d'an russuna. Bai amsa ba, itama ta shareshi ta fice daga falon.
Ya numfasa, har lokacin zuciyarsa ta kasa yanke tayashi yanke abinda ya dace. A gobe ne kuma zai bawa Abba amsa. Shi dai yasan Bintu ba ta daga cikin matan da yakeso, ina zai iya da shiriritarta? Ba k'aramin aikinsa bane wataran ya zaneta yayi mata raga-raga. Saidai kuma yanajin nauyin k'in amincewa aurenta. Da wane idon zai dubi Abba yace a'a? Mami kam, ya sani ba zata ji dad'i ba ko kad'an idan ya k'i jininta.
Da wannan tunanin ya kammala ya fito. Zai fice ya hangota daga d'akin Hanif, rik'e da shi a cinyarta tana kai lomar abinci tana d'an lasa mishi miyar a baki, sai kuma ta kyalkyale da dariya. Sun burgeshi burgewa, yasan tana son d'ansa, yana girmamata a wannan wajen.
Ya numfasa ya fice jin an soma kiraye-kirayen sallah.
[7/20, 9:57 PM] Aysha Abe: ¶°°BINTU°°¶


©Rufaida Omar
(July...2016)


<<24>>
Bayan sun shiga d'aki ta kora yaran zuwa tsakar gida. Bintu tuni ta soma hawaye.
"Ke, sanardani meke faruwa? Ina Yaya Fatima, ya na ganki ke d'aya?"
Inna ke jero dukkan tambayoyin nan cike da tsananin rud'ani. Bintu ta tsaida kukanta.
"Wai Mami ce, wai.." Kuka ya hanata k'arasawa. Inna ta soma fusata.
"Ki gayamin mana, me yafaru?"
"Cewa sukayi zasu auramin Yaya Ma'aruf."
Mamaki ya rufe inna, ta tsaya kyam tana dubanta.
"Shi ne kikace musu me?"
Ta turo baki.
"Gudowa nayi don ni..."
Marin da Inna ta shek'a mata ya haneta k'arasawa. Cikin tsananin tashin hankali take dubanta, kamar ba wannan Innar mai sanyin hali kuma mai tsananin nuna k'auna gareta ba. Kallo d'aya ta hangi tsananin 6acin ran dake kwance saman fuskarta.
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un!" Inna ta maimaita har sau biyu. Kawai sai kuma ta kece da kuka.
"Kaico wannan rayuwa, ni Dije wane zamani muke ciki da d'an Adam ke saurin manta halacci? Da ace kinsan menene kawaici da girmamawa da lallai baki baro gidan 'yar uwata ba bisa wannan k'aramar maganar. Idan ban ta6a gayamiki ba yau ki sani, Yaya Fatima ko dukkan yarana ta nema na bata ta rik'esu zan iya, babu irin sadaukarwar da bazan iya yi dominta ba matuk'ar bai sa6awa addini ba. Ban taso naga mahaifiyata ba, Yaya Fatima nasani, bayan mahaifina, bani da wata gata sai ita. Idan nace zan tsaya gayamiki ire-iren abubuwa na kyautatawar da Yaya Fatima tayimin a rayuwa zamu iya cinye lokaci wanda bazan so hakan ba. Bazan so Yaya ta ankara da cewar nan kikazo ba, ban haifi d'iyar da zata k'i biyayya ga 'yar uwata ba, yanda banyi ba, to muddin ina raye ba zan aminta da d'ayanku ya aikata hakan ba. Kin bani kunya! Kin kuma shayar da ni mamaki kwarai, ko a mafarki banyi zaton 'yar uwata zata bijiro miki da

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads