Showing 48001 words to 49729 words out of 49729 words
Chapter 17 - BINTU Book Complete Document by Rufaida Umar .txt
mijinta yayi tafiya, kasancewar gidansu basu da sa ido ballantana har abin ya zama wani babban al'amarin da zai shafi ZUMUNCI A YAU.
Sai hira sukeyi suna kyalkyala dariya. Rabin hirar kuwa Atika ke basu akan matar saurayinta. Yanda yake bala'in shakkar daukar koda wayarta a gaban matar.
Wayar Bintu da tayi k'ara ya sanyasu dubanta suna tsokana.
"Toh sarakan soyayya."
Ta murgud'a baki tana dariya kafin tace suyi shiru ta d'aga da sallamarta.
"My king, fatan dai ka bar fushin?"
"Idan kinaso na daina, zo ki sameni anan d'akina. Ta zaro ido.
"Lah, baka tafi gida ba? Karfe goma fa " Yayi 'yar dariya.
"Kina wasa, ai na gayawa Mami saidai nima na kwana a gidannata."
Ta hadiye dariyarta, suma tasu suka gimtse don kuwa a hands free wayar take.
"Allah Sarki My King, shikenan ai, da safe Dan dolo sai ya mik'o maka kayan karinka. Allah Ya tashemu lafiya."
Ta kashe wayar gaba d'ayanta, me zasuyi banda dariya. Aisha ta d'akamata duka a cinyarta.
"Wallahi kina daukar alhakin yayana, kinsan dai abinda yake nema."
"Ai idan batayi hakan ba, babu mai kiranta da Bintu." Cewar Hafsa cikin dariya.
Ta zaro ido.
"Lallai ma, kunyi zaton nima ina iskanci ko? Ba abinda na iya."
Sukayi dariya. Kasancewar basusan labarin ba yasa Aisha fesa musu. Ai kuwa nan sukayita tuntsire dariya. Ranar kwanan farinciki sukayi, ita kuwa tana sane ta k'ular da Ma'aruf.
Har washegari daurin aure da yini, babu abinda ya sake hadasu, koda tayi kiransa a waya sai ya k'i dauka. Hakanan ko sun hadu d'akin Mami bai ko kallonta. Jikinta yayi sanyi, da kanta ta soma neman shiri.
Don haka ana ta shirye-shiryen tafiya dinner, itama ta shirya cikin ankon da sukayi kalar pink, ta ci ado har ta gaji da haduwa, jikinta babu dadi, daurewa kawai takeyi don tana bala'in son zuwa fatin.
Ta dubi Aisha,
"Kuna iya tafiya, kinsan ni tare da King dina zan taho."
Sukayi murmushi kafin ta fita zuwa sashensa na gidan. Saidai yayanta Saifu ta iske, shi ke sanarmata yana can gidansa. Haka Mami ta saka aka kaita don ta tafi kafe saidai su tafi tare.
Da shigarta ta iskeshi saman doguwar kujera a kishingide yana amsa waya. Sam baiji shigowarta ba, ta karaso da sallamarta, alokacin ya ji ya amsa saidai bai ko dubeta ba. Ta zauna da sauri sanadin jiri-jiri da ke kwasarta, jikinta yayi zafi, ta tuna rabonta da abinci tun wajen k'arfe d'aya na rana da ta ci.
Bayan ya kammala wayar ya mik'e zaune. Sai lokacin ya dubeta, tayi mishi kyau kwarai. Ya yi kamar bai ga kwalliyar ba ya kauda kansa. Ta marairaice fuska gami da mik'ewa tsaye. Babu shiri ta soma kokarin zubewa awajen, da azama ya tarbota.
"Lafiya?" Ta soma kukan shagwa6a.
"Kaine kake fushi da ni, duk ka tayarmin da hankali."
Ya dagota.
"Abar wannan maganar, jikinki fa da zafi, kin kuwa ci abinci?"
Ta girgiza kai. Ya mike yana fad'in "Ina zuwa."
Ta kwanta a saman kujerar tayi lamo tana tunanin yanzu watakil ansoma shagalin fatin.
Can sai gashinan ya fito cikin kananun kaya. Ya dagata zaune yana jan tsaki.
"Wannan kayan ma ai k'arawa kanki wani nauyin ne Queen."
Zai ragemata ta nok'e har da hawayenta.
"Nifa wajen Dinner na biyo mu tafi."
Ya zaro ido.
"Kina a wannan halin? A'a muje dai na nema miki abinci sai mu wuce asibiti."
Ya nace, itama ta kafe harda kukanta, ya zaayi ma bataje dinar nan ba bayan ta ci buri akansa? Haka ya amince suka tafi, tayi-tayi ya chanja kaya ya k'i. Ta lafiyarta yakeyi.
Yaso su soma zuwa asibitin, ganin haka nan da nan ta mike ta daure tace ita fa ta samu sauki daman yunwa ce.
Ya girgiza kai kawai. Bintu akwai k'arfin hali.
Sun shiga yana rik'e da ita har mazauni. Bayan sun zauna, ya sanya aka kawomata abinci tun kafin ma a soma ciye-ciye. Ta ci tayi nak ta ture, sai lalla6ata yakeyi, sun burge mutane da yawa musamman sarakan soyayya, wato 'yan ROF whatsapp.(lol).
Fauza kasa jurewa tayi ta isa wajensu ta daukesu hoto, tana fatan kasancewa da habib dinta haka wataran. Sally ta k'ara kankame hannun Hashim dinta a kunne ta radamishi. "I love you." Shima ya ji sanyi, don soyayyar abokinsa da Bintu na burgesa.
Ba'a je ko'ina ba ta soma shek'a amai. Hankulan mutane ya dawo kansu, Ma'aruf ya ja ta sukayi waje, ma'aikatan wurin suka gyare wajen tsaf aka cigaba da shagali kowa hankalinsa yana ga Bintu. Ko meke damunta?
Kai tsaye shi kuma yana kaita mota suka nufi asibiti harda Atika wacce yasa ta hau su je.
Likita ya aunata ya buk'aci fitsarinta, ai kuwa result ya nuna tana da ciki. Hamdala kawai Ma'aruf yayi ta yi har suka fito hannunsa cikin nata.
Suna shiga mota ya sumbaci goshinta. Hawaye suka zubomata na farinciki.
Nan dai zance ya cika gidan ta bakin Atika cewar Bintu na dauke da juna biyu.
Kowannensu ya hau murna, Bintu bata da masaniyar wainar da ake toyawa don yayannata cewa yayi gidanta zata kwana ta huta.
Har aka kai Aisha babu inda ta fita, Mami ma ta goyi bayan Ma'aruf a wannan karon.
* * *
SANNU BATA HANA ZUWA...!
[7/28, 9:29 PM] +249 99 842 9948: ¶°°BINTU°°¶
©Rufaida Omar
(July...2016)
<<49&50>>
A yau har ga Bintu ta cika watanni tara cif dauke da cikin bebinsu da Ma'aruf. Sai kuma a wannan lokacin ne ta shiga damuwa sosai, ba na komai ba sai na tsoron haihuwa. Sau da yawa Mami ke kwantar mata da hankali don tuni ta komo gidan Mamin duk kuwa da ba da son ran mijinnata ba wanda yaso ta zauna gabansa ta haihu.
Takan ce, tana tsoron mutuwa kamar yanda Ma'u ta rasu. Ma'aruf da zarar ta soma zantuka haka har ma ta hau rok'on gafararsa, sai ya ji hankalinsa ya tashi, akwai sadda ya zubda hawaye yana rok'onta akan ta bar sanyamishi damuwa.
Haka dai har wata ranar litinin da daddare nak'uda ta taho gadan-gadan. Babu shiri Mami ta kwasheta sai asibiti. Cikin ikon Allah, mintuna baifi arba'in ba da zuwansu, ta haifo d'iyarta mace santaleliya.
Ma'aruf wanda ya zo tun wayar da Mami tayi mishi, suna tare da Mamin a tsaye suka ji kukan jaririyar. Sai kuma nos ta fito ta sanar dasu haihuwar.
"Ya lafiyar uwar?" Shine farkon abinda Ma'aruf ya nemi sani. Hankalinsa ya kwanta jin tana cikin koshin lafiya.
Murna kam ba'a cewa komai, washegari haka yan uwa sukayita zuwa gidan Mami don a washegari aka sallamesu.
Abinda ya burge Ma'aruf ga Bintu, bai wuce ganin da kanta ta nemi a sanya sunan Ma'u ba, shi kam ya so sanya sunan Innarta. Haka nan aka yiwa yarinya hud'uba da Asma'u suna kiranta BINGEL(lol).
* * *
BAYAN WASU SHEKARU...!
Barrister Fatima Bintu bakinta ya k'i rufuwa adalilin yau ake bikin yayesu daga makaranta. Tana rik'e da hannun Hanif da Bingel ta rungumosu Yaya Rufa'i ya daukesi a hoto. Ta k'arasa ta sumbaci goshin bebinta Amir mai sunan mahaifinta Muhammad dake rik'e a hannun Abida sabuwar 'yar aikinta. Nan ma ta kar6eshi akayi musu hoto, kafin ta k'arasa ta rungume Maminta tana hawayen farinciki.
"Yau ga Bintunki ta fito a yanda kikeso, I am now a Barrister.'
Sukayi dariya, itama Mamin ta sharce hawayenta na farinciki.
"Allah Shine abin godiya."
Sukayi dariya. Ta janyo Aisha wacce ke rik'e da d'anta Mustapha suka had'u suka sanya Mami a tsakiya aka dauki hoton.
Daga bisani kuma gaba dayansu har Abba suka dauka. Bintu ta cika tayi fum saboda rashin zuwan Ma'aruf akan lokaci. Har da hawayenta. Koda Abba yayi niyyar kiran wayarsa, hanawa tayi.
Har suka bar wajen suka dunguma zuwa gida babu shi da labarinsa.
Ganin an nufi gidan Abba bata damu ba ko kad'an, fushin da takeyi da mijinta yasa ta yanke koda kwana ta kama ta kwana anan ba zata k'i ba.
Saidai ta cika da mamakin yanda aka faka motoci a kofar gidan, su d'inma anan sukayi fakin suka fito cike da mamaki tattare da su.
Fitowar Saifu yayan Bintu dauke da d'ansa a hannu ne ya basu mamaki. Ya gaidasu Abba da fara'arsa, baice komai na daga tambayoyin da suke mishi ba yayita musu iso zuwa ciki.
A babban falon na Mami suka tarar da mutane cike, Ma'aruf na tsaye gaban wani k'aton cake yana kunna kendir. Ya dago ya sakarwa matarsa murmushi, tuni dukkan wani 6acin ranta ya gushe.
Nan fa bakin kowa ya gaza rufuwa ana ta murnar ganin juna.
Bayan Bintu ta yanka cake tayi kamar zata sanyawa Ma'aruf sai tayi azamar turashi bakin Hanif, akayi dariya.
Duk da iyayen dake a falon, baisa yayi dabarar yi mata magana ba.
"Ina sonki fiye da kullum. Babbar kyautarki shine, na biyamiki umrah."
Ta dago dara-daran idanunta ta dubeshi tana dariyar farinciki. Da ace akwai hali da ta rungume mijinta, kawai sai ta soma fidda hawayen farinciki tana dubansa. A haka Rufa'i ya daukesu hoto ana dariya.
TAMMAT BI HAMDULILLAH
Inda mukayi kuskure a gafarcemu. Nagode sosai yan uwana masoyana, shakka babu kun nunamin kauna, fatana Allah Ya hadamu haka a aljannarSa. Amin.
Godiya ta musamman ga Ummu Abdool, Bingel. Kun zamo wasu jigo a rayuwata, Allah Ya bar zumunci, amin
Ban manta 'yan ROF na Facebook da whatsapp, wlh ina kaunarku!
Sai: DDM, DM(ciwon ido kenan), HDY(Abin Tunk'ahona), Fikrah Writers Association. Dss.
Da duk masoya masu kirana dain text, da kurame masu karantawa babu magana, fatana dai su tsinci sak'onnin..lol. Nagode gaba d'aya.
Sai Allah Ya had'amu a goron babbar sallah in sha Allah...!
((RUFAIDA OMAR IBRAHIM M))