Showing 87001 words to 90000 words out of 198763 words
Chapter 30 - Kanwar Maza 3&4 Original Book Complete writing by Aisha Cool .txt
lilon, ki ka fasa kai ba zaki koma ba".
Mai sunan baba ya yi sallama a falon mama, suka amsa rumaisa ta tashi da gudu ta rungume mai sunan baba.
Ya ɗan yi murmushi, ya dafa kafaɗarta.
Iman ta ce "Ina wuni"
"Lafiya ƙalau" ya amsa, ya saka hannu ya ɗauki sabir yana ɗaga shi sama.
Iman na son ɗaga kai ta kalli mai sunan baba, amma ta kasa, shi kuma a wayance yake ƙare mata kallo.
Iman ta tashi ta ce "Mama bari na tafi, zan je aiken mama, maman sabir ga kayan abincinsa nan a wannan jakar".
Mama ta ce "Iman ki bari ayi azahar ki ci abinci"
"A'a mama, na ƙoshi ni sai na kai yamma daga yanzu, ban ci abinci ba ma".
Mai sunan baba ya kalli iman ya ce "Nemi wuri ki zauna" tsit kowa ya yi yana kallon mai sunan baba, ai ko motsin kirki ba ta yi ba,ta zauna ta na wuri-wuri da ido.
Ya basar kamar bai yi komai ba, aka cigaba da hira har da shi, haka nan yau yake jin daɗin ganin rumaisa a gida.
Sai dai bai ji daɗin yadda iman ta takure sosai ba.
Har azahar iman ba ta samu umarnin tafiya da ga mai sunan baba ba, sai da aka gama girki.
Sabir sai rarrafwa yake, kwano-kwano ya ci na wannan ya ci na wancan.
Yadda rumaisa take a cikin yayyenta, ba ƙaramin burge iman yayi ba.
Sai da mai sunan baba ya fita, sannan iman ta samu ta tafi.
Rumaisa da yaya usy ta keɓe, suna magana.
"Yaya yaushe za ka zo, akwai labari fa?"
Usman ya ce "Labarin me?".
"Ni dai kawai ka zo dan girman Allah"
Ya ce "Kar ki damu, zan zo in sha Allah".
Ana idar da sallar magariba, Adam ya zo tafiya da rumaisa, amma ta ce Alla kar ta ba in da za ta" sai da aka kai ruwa rana, sannan ta ɓanɓaru daga gidan nan, suka tafi, sai dai ta sha kuka sosai da sosai, mama ta harhaɗa mata ƴan kayayyakin amfani da za ta tafi da shi.
Sam Adam bai kulata ba, har su ka je gida, dan haryanzu bai huce da abun da ta yi masa ba.
Ya ajiyeta a gida, tana jiran ta ga ya fito daga motar, ta ga ya juya ya tafi da sabir.
Hakan ba ƙaramin haushi ya bata ba, hakan ya sanya ta shiga ɗakinta, ta yi ta aikin kuka.
Da ya dawo daga mayar da sabir, bai nemi ruma ba, sai da safe, shi ma dan yana tsoron, kar ya kawar da kai a kan ta, ta yi wani rashin jin.
Sai dai ya tarar tana banɗaki, ya ƙarasa gaban gadon, ya kai hannu ya ɗau littafin da yake buɗe, da fensira a kai.
"Duk wanda ya duba littafin nan, ba da izinina ba, Allah ya isa!!!"
Tsaki yayi, ya buɗe shafin gaba.
"Zan so ace ni marubuciya ce, da sai kun fi fahimtar abun da zan rubuta, amma gaskiya ba zan iya ba, ban sani ba ko ku gane me nake nufi, idan na zana abu mai muhimmanci da ya sameni a rayuwa, da wanda ya tsaya a zuciyata har in mutu ba zan manta ba, ina fatan ku ji irin abun da na ji, ko za a samu mafita".
Zane ne tiryan-tiryan, zane mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, daga fitarsu daga gida zuwa tasha, tare da taƙaitattaun bayanai, a gefe, na abun da ya faru". Nutsuwa ya nutsu yana bi, sai dai duk da haka ta cire wasu abubuwa masu muhimmanci.
Daga banɗakin ta fito, tana kokowa da towel, sai dai ta yi turus da ganinsa, saboda ba ta san ma yana gidan ba.
Kallon-kallo aka shiga yi tsakaninsa da ita, kamar ɓarawo da mai kaya.
"Meye wannan?" Yayi maganar yana nuna mata littafin.
"Waye ya ce ka ɗaukar mini littafi? Ba ka ga gargadin da na yi a farko ba?".
"Me wannan zanunnukan suke nufi, bayan kin ce mini, ke baki san komai ba? Meye ƙarashen wannan zanunnukan, kuma a wace tashar motar ku ka hau mota?"
Tura baki ta yi ta kawar da kai, ya nufeta gadan-gadan, nan take ta ga idonsa ya fara wannan hayaƙin.
"Yi haƙuri, ka bani zan yi maka bayani"
Ya miƙa mata littafin, sai dai tana karɓar littafin, ta riƙe towel ɗin ta, ta kasa da gudu ta bar ɗakin.
Ayshercool.
08081012143
Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Susbcribe my YouTube channel please 🙏
Bai yi wata-wata ba ya rufa mata baya, tuni ta yi downstairs, tana riƙe towel ɗin ta, ko da ya sauka ƙasa ya neme ta ya rasa.
Ya kalli Asiya da take mopping a falon, ya ce "Ina ta shiga?"
Ta nuna masa kitchen, da sauri ya shiga kitchen ɗin, ya tarar da ita da barira, ta yi wuƙi-wuƙi da ido ta na kallon sa, sai dai ta ɓoye hannunta a bayanta.
"Ina yake ina littafin? Ina ki ka ajiye shi?"
Shiru ta yi masa ta na bin sa da kallo.
Takowa ya fara yi, yana cigaba da tambayarta, sai dai ta fara ja da baya, ganin idonsa ya cigaba da wannan hayaƙin.
Sai da ta dangana da jikin bango, ya zo ya tsaya a kanta.
"Wannan abu ne da ya shafi rayuwata, kacokan da iyalina, ba na wasa da duk wani abu da ya shafi aisha, zuwa yaushe zaki cigaba da wahalar da ni ne? Ki gaya mini abun da nake buƙata, ki yi mini bayanin zane-zanen da ki ka yi?".
Kawar da kanta ta yi gefe, daga kallon fuskar sa, tare da bawa kanta ƙwarin gwiwar jure duk wani abu da zai yi mata.
"Am talking to you!" Yayi maganar cikin shouting.
"Ni ka ƙyale ni, ai ba da iznina ka ɗau littafin ba" ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin jan jikinta ta wuce.
Dannata ya yi a jikin bango, ya zura hannunsa bayanta, ya banƙara hannunta, ta zunduma wani uban ihu, sai dai babu littafin a hannunta.
Hayaƙin da kitchen ɗin yake yi ne, ya sanya shi ɗaga kai, kawai ya hango littafin ta tura a cikin gas, yake ƙonewa.
'Innalillahi wa Innalillahi raji'un ' ya faɗa a zuciyarsa, bai taɓa ganin halitta mai azabar taurin kai da masifa, kamar wannan yarinyar ba'.
Baba uwani kuwa, magiya take yi masa a kan ya taimaka ya rabu da rumaisa, saboda yadda take kururwar zai karya mata hannu.
Da sauri ya nufi gas ɗin, barira ta ja da baya, saboda gaba ɗaya fuskarsa har ta fara sauyawa, saboda azabar ɓacin rai da fushi. Sai dai kash tuni littafin ya babbake, ya zama toka.
Rumaisa kuwa zubewa ta yi a wurin, tana yarfa hannunta, saboda yadda take jin sa tamkar ba a jikinta ba.
A fusace ya waiwayo ya kalleta, ya zo ya sake danƙar hannunta, ya ja ta daga kitchen ɗin.
Baba uwani ta bi shi tana yi masa magiyar ya rabu da rumaisa, amma ya shareta, rumaisa ta saka hannunta ɗaya, ta riƙe towel ɗin da yake barazanar faɗuwa. Duk wannan masifar da haƙilon, idon rumaisa mursisi, ba ta yi dana sanin abun da ta aikata ba.
Ɗakinsa ya wuce da ita, ya rufe ƙofar gam, ya tankaɗata kan gadonsa, ta zauna daɓas, ita kokowarta kar towel ɗin ta ya faɗi ƙasa.
"Ki gaya mini me ki ka sani game da mutuwar aisha, da saceta?".
"Wai ya ka ke tamabyata kamar ni na sace ta? Ni ban san komai ba, ni ma fa sace ni aka yi".
"Amma kin san wani abu, akwai abun da ki ke ɓoye wa, atleast a bayaninki akwai wani abu da zai taimaka, na gane idan saceta haɗin baki ne".
Ta ce "Oho, ni dai ban san komai ba, zanena kawai nake yi, idan kun ji haushi, tun da ku jami'an tsaro ne ku din ga aiki tsakani da Allah, ni ka daina yi mini masifa, ba abun da na sani".
Cikin matsananci fushi, ya ce "So ki ke na illataki ko? Idan ki ka bari na yi miki illa, na yi wa banza, ke zaki nakasa ba ruwana. Kin san muhimmancin aisha a wurina kuwa? She don't deserve, such kind of death, ki yi mini bayani kan na yi miki illa"
A karo na biyu ta sake kawar da kai, ta na zumɓura masa baki.
"Kalleni"
"Ni ba zan kalleka ba, kai baka ganin abun da yake fitowa daga idonka?".
Ba ta yi tsammani ba, ta ji ya riƙe gashin kanta ya ja, sai da ta kusa shiɗewa, ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin ƙwacewa.
Ga mamakinta, sai ta ga fuskarsa ma ta fara baƙi, duk ya yi wani iri.
A take mafarkin da ta taɓa yi, ya fara ƙoƙarin zama gaskiya, dan faratansa ya fara karta mata a wuyanta, ya kuma shaƙeta ya na wani irin kakari.
Da fari su barira sun biyo bayan baba uwani, baba Uwani ta kasa kunne a jikin ƙofar, ta na jiyo abun da suke cewa, sai dai tun da rumaisa ta yi ƙara suka ji shiru.
Jiki na rawa barira ta ce "Baba uwani, ko mu kira masu gadi, a ceto ta, kar ya yi mata illa".
Baba uwani ta ce "Ke ina ruwan ki? Dalla ku wuce ku je ku cigaba da aikinku"
Rumaisa kuwa bayan ya yi mata wannan shaƙar, sai da ta suma, ya saketa ta faɗi ƙasa, sannan ya yanke jiki ya faɗi a gefenta, cikin yanayi mai kama da bacci.
Asiya kasa nustuwa ta yi, ta ce "Barira, tsoro nake ji fa, kar ya kasheta, ko police station aka kaimu bayar da shaida an cucemu".
"Bari kawai, wallahi nima a tsorace nake, ga matar nan ta hana a nemo taimako".
Asiya ta ce "Bar ƴar rainin hankali mana".
"Ita ma dai, ta na da azabar taurin kan tsiya, ni ina girki kawai na ga ta shigo da gudu, ta tura abu a wuta, zan yi magana ta ce in yi shiru, sai ga shi ya biyo ta, amma na ji yana magana a kan Aisha, wataƙila abu ne mai muhimmanci da ya shafe ta".
"To waya sani, ni dai fatana kar ya illata kawai".
Bayan sa'oi uku, Adam ne ya fara yin juyi, dan ji yake kamar barci yake yi, kawai ya ga rumaisa a kwance a ƙasa, ita daban towel ɗin ta daban, da ga ita, sai gajeren wando.
Tashi ya yi zaune yana ƙoƙarin tuna abun da ya faru, kawai dai ya iya tuna yadda ya janyota har ɗakinsa, amma daga nan komai ya goge a kansa.
Tsura mata ido ya ɗan yi, yana tunanin ko barcci take yi ne? Amma sai ya ga yanayinta bai yi kama da haka ba.
'Ko wani abun na yi mata?' ya tambayi kansa.
Matsawa ya yi kusa da ita, ya ɗagota, ya ga jikinta a sake.
A gigice ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, i lose my sense again?" Rabon da ya fita completely daga hankalinsa haka, an kai shekaru goma, ko ya yi loosing control, ya na iya tuna abun da ya faru, amma completely yau ya kasa tunawa.
Wuyanta ya kalla, duk shedar an karceta da farce.
Ya ɗan girgiza ta ya na kiran sunanta.
"Rumaisa!" Amma shiru ba ta motsa ba, ya taɓa hannunta, ya ji zuciyarta na bugawa, numfashi da take yi a hankali.
Ya kwantar da ita ya shiga banɗaki, ya ɗebo ruwa a hannunsa, ya dawo ya shafa mata a fuskarta, ya ƙure gudun Ac da na fanka.
Bai ɗaura mata towel ɗin ba ya ƙyaleta, ya lulluɓe ta da shi, ya tsura mata ido yana fatan Allah ya sa ta farka, dan kuwa idan ya ɗauketa ya kai ta asibiti, asirinsa zai iya tonuwa, dan babu lallai ta yi shiru, kuma dole a tambayi mai ya sameta, ya cigaba da addu'a Allah ya sa ta tashi.
Babu tsammani, kawai ya ga ta tashi zaune, tana ganinsa ta ja da baya, ta kare jikinta da hannunta.
Sai a lokacin ya yi ajiyar zuciya "Ki ɗaura towel ɗin mana" ya faɗa a sanyaye.
"Dole ka ce na ɗaura mana, bayan ka yi mini tsirara, za ka kasheni, wallahi gida zan gudu, ba zaka kasheni ba? A hakan zan gaya maka abun da na sani ɗin? Dama ban san komai ba ma, wallahi ba zaka kasheni a banza ba, ka shaƙeni kamar wata ɓarauniya".
A hankali ya ce "Ya ilahi, i attempt to kill her?'
Ta saka hannu ta ja towel ɗin, ta rufe jikinta, ta yinƙura ta tashi, ta fice daga ɗakin.
A hankali ya lumshe idanunsa, ya bawa hawayen da suka taru a idonsa damar zuba, ba zai so ammi ma ta ji wannan maganar ba, iya rayuwarta a hanyar nema masa magani take, ana murna abu ya ɗan yi sauƙi sai abun da ba a rasa ba, kwatsam yau abu ya dawo kamar da.
Sai ya ji tashin ciwon nan nasa, ya shafe abun da rumaisan ta aikata masa.
"Mahaukaci ne ni? Ko kuma maye? Ko kuma namiji mai mutanen ɓoye, wato aljanu?" Tambayar da tun da ya shekara takwas a duniya, yake yi wa kansa da ya gaza samun amsarta.
Ba shi da tabbacin rumaisa ta rufa masa asiri, haka zalika bai san ta ina zai fara yi mata bayani, ta fahimce shi ba, sai a lokacin yake ganin rashin kyautawar da aka yi, na rashin yi musu bayanin larurarsa.
Madigar kuwa ta na zuwa ɗakin ta, gado ta hau ta cigaba da bacci.
Baba uwani kuwa, ta fita ta zagaya, jikinta na tsuma, ta kira lambar Mummy.
Aka yi sa'a mummy na kusa, ta ɗag wayar, gulma na cin ta ta ce "Allah ya taimake ki"
"Ina jin ki".
"Akwai abun da ya faru".
"Je ki kai tsaye".
Baba uwani ta waiwaya sannan ta ce "Ranki ya daɗe, muna cikin aiki muka ga ya biyota afujajan, a kan wani littafi, sai dai kan ya cimmata ta tura shi a wuta, na ji yana magana cewa, abun da ya shafi aisha ne, baki ga shaƙar da yayi mata ba, ƙarshe dai ya shiga da ita ɗakinsa, ya rufe su, sai yanzun nan ta fito".
Mummy ta ce "Good, kin fuskanci ya yi mata wani abu ne?"
"Ban san me yayi mata ba da ya rufe su, amma na ga ta fito tana kamar magagin bacci".
"Kin sanar da samha ne?"
"A'a Allah ya baki nasara".
"Kar ki sanar da ita komai, sai abun da na umarce ki".
"In Allah ya yarda".
"Ki koma, ki cigaba da sanya mini ido a kan duk wani motsinsu".
Baba uwani ta ce "An gama uwar ɗakina". Ta katse wayar ta koma.
Adam kuwa ya yi sallar azahar, ya jingina da jikin gado, ya yi shiru yana tuna abubuwan da suka shuɗe, gaba ɗaya jikinsa ya yi sanyi.
Kiraye-kirayen, sallar azahar ne ya tashi rumaisa, ta je ta yi alwala, ta saka kaya, ta tsaya a gaban mudubi, ta na kallon wuyanta, da ya shata yake mata zafi.
Shiru ta yi tana tunanin tabbas ta taɓa ganin wannan abun a mafarki, ko kuma ya taɓa faruwa.
"Wallahi sai na gaya wa mama, tun da kasheni zai yi, sai na gudu na bar gidan nan"
Can kuma sai wata zuciyar ta tunatar da ita, muddin mama ta ji a kan meye, ya yi mata abun da yayi mata, ba zata goya mata baya ba, faɗa za su yi, a bata rashin gaskiya, kuma a kirsheta ace sai ta faɗi abun da ta sani, bayan ta riga ta ce ita ba ta san komai ba.
'Subhanallah, na fasa faɗa, bari na yafe masa, wataran ya na da kirki, amma wallahi ko zai kasheni ba zan faɗa masa komai ba, sai lokacin da na ga dama, bari na lallaɓa na san yanzu ji yake kamar ya kashe ni' sai kuma ta ɗan yi shiru ta ce "To da ya shaƙe ni kuma sai na yi bacci, oho dai? Ta gama abun da Allah ya nufe ta da yi, ta yi salla ta fito dan yunwa take ji.
Adam ya tashi ya nufi ɗakinta, domin ya duba ko ta na lafiya ta gama wartsakewa, sai dai ya jiyo motsi a kitchen.
Ya leƙa kitchen ɗin, ya hango ta taka kujera, tana saka ɗan wake, kamar babu abun da ya sameta.
Abun har mamaki ya bashi, kamar ya yi mata magana, sai kuma ya fasa ya fita.
Baba Uwani na ganin fitar Adam, ta lallaɓo ta hawo benen.
"Sannu ƴar nan, ina fatan bai yi miki komai ba?"
Rumaisa ta waiwayo ta kalli baba uwani ta ce "Yayi mini me?".
"Ai ganin yadda ya janyo ki ɗin nan, abun ya tsoratani, ke ma da ko me yake buƙata kin bashi kin wuce wurin, idan ransa ya ɓaci hankalinsa gushewa yake wasu lokutan, zai iya yi miki illa. Ko dai hakkinsa ki ka hana shi ne?"
Rumaisa ta juyo gaba ɗaya ta kalli baba uwani ta ce "Wane irin haƙƙi kuma?".
"A'a haƙƙin aure mana".
"Meye haƙƙin aure kuma?"
Baba uwani ta ce "Ahh shikenan, bari maganar kawai".
Har baba uwani za ta fita ta ce "Kenan papa da gaske maye ne?"
A razane baba uwani ta waiwayo ta ce "Me ki ka ce?"
"Kin ji me na ce ai".
"Ke waye ya gaya miki?"
Rumaisa ta ce "Ke ce ki ka gaya mini yanzu"
Baba uwani ta ce "Ke, yaushe na gaya miki? Ki ji tsoron Allah"
"Ke ki ka faɗa, wannan ne karo na biyu ki na gaya mini, zan kuma tambaye shi".
"Dan girman Allah ki rufa mini asiri, da wasa nake yi ma fa, dan Allah kar ki gaya masa"
Rumaisa ta juya ta cigaba da saka ɗan wakenta, baba uwani kuwa ta toshe baki ta na fatan, Allah ya sa kar garin neman gulma, ta janyo kwaɓarta ta yi ruwa, domin kuwa ta lura bayan ƙuriciya, har da wauta ke damun rumaisa.
***
"Hajiya Lubabatu, ki na free gobe in Allah ya kaimu". Mummy ta yi maganar da waya a kunneta.
"Ya aka yi ne?".
Mummy ta ce "wurin malam na gidan dutse, zaki rakani, akwai case ne".
Hajiya Lubabatu ta ce "Wane irin case kuma?".
"Ɗan maje ne ya turo mini saƙo, wai ya ji mai martaba zai wakilta turaki, zuwa taron bunƙasa al'adu da harsunan afrika, rainon burtaniya, wai ya ɗauki mutum biyu a matasan yaran nan ya tafi da su, kuma da alama za a samu cigaba, wai ya ji turaki ya ce har da Adam za ayi tafiyar".
Hajiya Lubabatu ta ce "To ba sai su yi ta yi ba"
"Ina ba fa zai yiwu ba, wai ke meyasa ki ke ɗaukar al'amuran nan da sauƙi, komai sai dai shi, duk wannan miyagun fentin