Showing 189001 words to 192000 words out of 198763 words
Chapter 64 - Kanwar Maza 3&4 Original Book Complete writing by Aisha Cool .txt
aikin da ya yi mana"
Ruma ta ce "When are you exposing her?"
"Soon in sha Allah"
"Idan ba zaka yi ba, allow me to do it"
"I will in sha Allah" ya juya ya fita.
Haka ruma tayi ta aikin rarrashin Adam, dan abun ya dake shi sosai da sosai, duk iya tunaninsa bai ga ta ina zai iya jayayya da SMOKE ba.
Kuma dolensa ya haƙura da cigaba da duk wani yinƙuri a kan garkuwa da aisha, saboda rayuwar rumaisa.
***
Kwanaki uku kenan, gidajen sarautar suka shiga ɗimbin tashin hankali, komai ya damalmale, ba kama hannun yaro, aka gaza samo bakin zaren abubuwan da suka riga suka dagule, Kodayake ba komai ne zai gyaru ba, kasancewar wata ɓarakar ta samo asali ne tun shekarun da suka gabata, ba tare da an mayar da hankali an gyara su ba.
Kodaye rumaisa ta kawo gagarumin cigaba da kuma gyara wasu abubuwan.
Ba tare da wani cikakken shiri ba, Mahmud ya ce lallai sai Yasir ya tafi canada, Yasir ya so ayi bikin yaya Abubakar yana nan, amma ba dama, aikuwa sai da yayi kuka saboda rabuwa da mama da ƴan uwansa. Mahmud kuma ya ƙarfafa yin hakan ne, kar wani abu ya samu Yasir, saboda aikin da yayi musu, dan a wata fuskar laifi ne abun da ya aikata ɗin, kutse da satar bayanan mutane ba tare da izinin su ba.
Haka ya tsallaka ya tafi ya bar Nigeria.
Abdallah kuwa Bashir ya ce sai sun tafi da shi Abuja, mama ta tashi hankalinta ganin kamar ana yi wa yaranta ɗauki ɗaya-ɗaya, amma ya bata tabbacin babu wata damuwa, a kan Jamil ne ita ma rumaisa Adam ne zai wakilce ta, saboda tsohon cikinta.
Ranar da zasu tafi Abuja, takawa yayi ta rarrashin ruma, tare da bata tabbacin, Abdallah zai dawo lafiya, tun da har da shi zasu tafi.
Rumaisa suna ta shirin fara Waec, sai dai fa nauyin ciki ya hanata sukuni sosai, tun da ta dawo daga makaranta, mararta take yi mata ciwo da ƙafafuwanta, kuma takawa ya riga ya tafi, dama ya ce mata idan ba zata iya zaman gidan ba, ta tafi gida wurin mama ko ammi.
Jin ciwo yaƙi ƙarewa, ta kira Usman a waya, ta ce ya zo zata mutu.
Ya je ya tarar da ita duk a firgice, ta bashi mukullin ɗaya daga motocin takawa, ta ce ya kaita asibiti.
Suna tafe a hanya ya ce "Ko dai haihuwa zaki yi?"
"Edd ɗin bai cika ba fa"
Ya ce "Ikon Allah, muna zaune yarinyar da muka goya, muka yi wa wanka za ta haihu, haryanzu muna gararamba, bakomai akwai lokaci"
Bakin rumaisa bai mutu ba, sai da aka ce mata haihuwa ce a asibiti, ita dai ta san lokacin haihuwa da saura, aka ce usman ya je ya kwaso kayanta.
Maimakon ya kira mama a waya, ko ammi, kawai sai ya kira Aliyu da Huzaifa, sannan ya ƙarasa gidanta, ya ɗaukko akwatin da ta kwatanta masa, dan tuni takawa ya gama sayen komai na jariri.
Mamaki ya kama nurses ɗin, suka ce babu wata mace wadda za ta zauna da ita duk sai maza.
Huzaifa ya ce "Hajiya gidanmu ita kaɗai ce mace, babarmu kuma tsohuwa ce ba ta da cikakkiyar lafiya, duk abun da mata zasu yi, mu ma zamu yi"
Nurse ɗin ta ce "A dai duba dangi a samo wata"
Usman ya ce "Hajjaju, wallahi zamu iya komai, ki ƙyalemu kawai".
"To ina mijinta?"
Aliyu ya ce "Tafiya ce ta kama shi ɗazu"
Ta jinjina kai ta ce "Lallai ƘANWAR MAZA"
Rumaisa ta sare da al'amarin, saboda tun da mama ta haifeta ba ta taɓa jin masifaffen ciwo kamar wannan ba.
Mai sunan baba kuwa, ganin hankalin Adam yayi wani wurin, mahmud kuma ya warware, ya sanya ya yi wa mahmud zancen, mahmud ya din ga murna, ya ce dole su je Lagos tare, dan tabattar da wannan lamari, dan haka ya ce zai yi musu booking Flight su je, su yi abun da za su yi, saboda su koma bakin aiki.
Mai sunan baba ya kira Huzaifa a waya, yana masa faɗan duk suna ina, gida ba kowa sai mama itakaɗai a gidan.
Mama ta ce "To yarinya ce ni, da lallai sai sun zauna a gida?".
Huzaifa ya gaya masa in suka tafi, ba tare da ya gaya wa mama abun da ake ciki ba, ya tafi asibitin.
Ƙarshe sai da suka cika asibitin, Abdallah da Yasir ne kawai babu.
Gaba ɗaya suka zama abun kallo a asibitin, wai sun kawo ƙanwarsu haihuwa a asibiti.
Ruma ba ta haihu ba sai bayan magariba, babyn pre term ne, watanni bakwai da sati biyu.
Nurse ta fito ta ce "Kun ga ga mahaifa, ga kayan jini, dan girman Allah ku nemo mace"
"Sai kuma ki yi, karɓar haihuwar ma da kin matsa sai mu karɓa, ko abun da ya fi kayan jini ne zamu gyara, babarmu tsohuwa ce, bamu da ƴar uwa mace, dangi ba kowa ke son ka katse masa hidimomin sa ba, dan haka ba jini ba, ko menene zamu iya"
Mai sunan baba ya ce "Ina jaririn?".
"Nursery zamu kai shi, sa an saka shi a kwalba"
Sai da suka jira aka basu damar shiga su ga ruma, tana kwance kai da ganin idonta ka san an sha gwagwarmaya.
Nurses suka ce a kawo mata abinci, sai a lokacin mai sunan baba ya tafi gida, ya gaya wa Iman, ruma ce ta haihu.
Mamaki ne ya kamata, dan washegarin taron nan sun haɗu a gidan ammi, ta ce mata haihuwarta da saura.
Nan da nan ta yi girki, jiki na rawa tare da mamakin haihuwar ruma, ta kira ammi ta sanar mata.
Ammi ta ce "Ba dai rumaisa ba, takawa ya ce da saura ai"
"Wallahi ammi da gaske nake, yanzu yaya umar ya shigo ya gaya mini".
Nan da nan aka cika asibitin, ƴan barka, sai dai ba ganin jariri, rumaisa kuma ba baki, duk wanda yayi mata sannu, sai dai ta jinjina kai kawai, amma ta san halin tashin hankalin da ta shiga a haihuwar.
Mama ta kalli rumaisa ta ce "In ce dai ta bakin ki ka haifo ɗan naki, yau mata sun ga ta in da ake haihuwa" ruma tayi murmushi kawai.
Da ƙyar ta iya cin abincin ma, ta fara cewa ita a kawo mata ɗan ta fa, saboda lokacin da ta haife shi, tana gani ana ta fama, ya ƙi yin kuka yadda yakamata.
Abdallah ya sha tambaya a babbar headquarter Dss ta Abuja, dan sai da aka karɓi zanen aka sa shi sake yin wani, suka yi iya binciken da zasu yi, babu ko shakka Jamil ne, Wanda dama already yana hannunsu, takawa yayi kamar ya gaya musu da sanya hannun wakili, amma tayaya meye hujjarsa? Rumaisa ce kawai ta ji sun ambaci wakili, idan da wanda zai faɗi da sanya hannun wakili, to Jamil ne yakamata ya faɗa.
Duk wani report na bincike lokacin ɓatan aisha da suka yi, sai da suka gabatar da shi a wurin hukumar, laifin Jamil ya zama biyu, da na tuhumar fitar da sirrin hukumar, da kuma haɗa baki tare da yin garkuwa da ƙanwarsa, ga kuma ɓatawa Adam suna da yayi.
Ko da ana nunawa Jamil zanen nan, da Abdallah yayi, sai da ya zabura, saboda tabbas ya san shi ne.
Adam ya ce "Jamil ka tabattar wannan kai ne? Jamil me muka yi maka ni da Aisha? Idan ma wani abun na yi maka, meyasa zai shafi aisha? Ka haɗa kai da wakili ka cutar da ni?"
"Adam jin dalilin hakan ba shi da wani amfani a gareka, tun an riga an kama ni, sai ka je ka cigaba da rayuwarka, ka ƙyaleni. A kan me mahaifinmu zai fifita aisha a kanmu? Kuma duk wani abu na cigaba, ko na masarauta sai dai ya sanya ka a ciki alhalin gani. Wallahi da na san yarinyar nan ta gane ni, da ban barta ta rayu ba"
Adam yayi murmushi mai ciwo ya ce "Na gode sosai Jamil, sai dai ka sani, duk da ciwon hauka da nake fama, na tsaya ga Allah, shiyasa nake cigaba, kuma na barka da Allah Jamil, Jabir ma har shi da duk wanda ku ka cutar da ni, kamar yadda rumaisa ta faɗa, ta ce in bar ku da Allah, zan ga yadda zai yi da ku, na bar ku da Allah"
Takawa suka koma masauki shi da Abdallah, tare da Bashir.
Sosai suke bawa Adam baki, tare da bashi ƙwarin gwiwa.
A lokacin yake sanar da su abubuwan da wakili ya kira shi ya sanar da shi.
Sun girgiza sosai da sosai, Bashir ya ce "A gaskiya na girgiza, dama biri yayi kama da mutum, yadda aka kasa magance wannan Smoke ɗin. Amma ina ga kamar yadda madam ta faɗa, ka yi ƙoƙarin gano wanda suka yi maka maƙarƙashiya, amma hukunta su sai Allah".
Ammi ce ta kira Adam a waya, ta sanar da shi rumaisa ta haihu, sai dai yaron an saka shi a kwalba.
Adam kansa abun ya ɗaure masa kai, wace irin haihuwa ana zaune ƙalau, ba tare da cikakken lokaci yayi ba.
Gashi bai bai gama da abuja ba, amma ya ce dole ya koma kano. Zai bar Abdallah da Bashir ko za a buƙaci wani abun, idan komai ya lafa sai su taho, shi kansa Abdallah abun ya bashi mamaki, a kan ya aka yi rumaisa ta haihu a wannan lokacin.
Sai dai cikin ƙudura ta Ubangiji mai kyauta da ƙari, yaron da mimi ta haifa ya koma ga mahaliccinsa cikin dare, dama ana ta fama, yaƙi kuka amma d girmansa ba ka ce bai kai lokacin haihuwa ba.
Aka yi shiru ba a gayawa mimin ba sai washegari da safe, aikuwa rumaisa ta dira rigima, ta din ga kuka, tun mama na rarrashinta, sai da ta ƙular da ita, ta fara zaginta.
Mama ta ce "Ba zaki rufe mini baki ba?"
"Mama baki san me nake ji ba ne"
Mama ta ce "Dan ubanki ƴaƴa biyu na binne, da zaki ce ban san me ki ke ji ba".
Ammi ta ce "Maman rumaisa ki yi haƙuri, yarinya ce kuma dole za ta ji babu daɗi"
Aka naɗo jaririn, aka kawo wa rumaisa, kamarsa ɗaya sak da Adam.
Sabir da yake zaune a kusa da rumaisa ya kalleta ya ce "Mimi, baby ya buɗe ido" yayi maganar cikin yarinta.
"Boy babynmu ya mutu"
Ammi ce ta karɓi jaririn, ana jiran shigowar adam, ayi masa sutura.
Ƙarfe tara na dare Adam ya dira, ko gida bai je ba, kai tsaye asibiti ya taho, ammi tuni ta sanar masa da rasuwar yaran, dan haka hankali a tashe ya ƙarasa asibitin jikinsa duk a sanyaye.
Ya tarar tuni Ammi na can ita da nusaiba, mama tana wurin rumaisa.
Ya durƙusa suka gaisa, ammi ta tambaye shi ya ake ciki, ina Abdallah?.
Ya ce mata yana lafiya, yana tare da Bashir, akwai abun da zasu ƙarasa.
Ammi ta miƙa masa jaririn, ya karɓe shi ya buɗe zanin, kamar mai bacci, kamar sa ɗaya sak da shi duk da jikinsa yayi fari, amma da gani ka san yaron fari ne.
Ya miƙawa ammi shi, ya ce "Allah ya sa mai ceto ne" suka amsa da amin.
Mama tuni ta tashi ta bar ɗakin, ya ƙarasa gaban gadon mimi, ya zauna a kusa da ita ya riƙo hannunta.
Kawai ta fashe da kuka ta ce "Papa babyna ya mutu, kuma ina son shi"
Ya rungumota jikinsa ya ce "Am sorry mimi, ni kaina na ji ba daɗi, amma Allah ya fi mu sanin me ya dace da mu, kiyi haƙuri ki daina kuka"
Yayi maganar yana shafa bayanta, shi kansa ya ji mutuwar yaron, sun sanya rai da yaron sosai da sosai.
"Ko dai abubuwan da suka faru ne, ya sanya ki ka tashi hankalinki ki ka fara labor?"
Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"To shikenan, Allah ya bamu mai amfani, ya sanya wannan mai ceto ne, na sanya masa sunan mahaifina Muhammad, Allah ya bamu wani" rarrashinta ya din ga yi tana jinjina masa kai.
Iman ta shigo ita da Usman, Usman sai da ya sunkuyar da kai, kunya ce ta kama shi, ganin yadda takawa ke zaune ya rungume mimi yana rarrashinta, ga ammi a zaune.
Abun da bai sani ba shi ne, har abun da ya fi haka yi suke, ita ba abun da ya dameta bane ba, domin ita kanta bata manta lokacin da aka yi mata aure, ba shirmen da ba sa yi ita da marigayi galadima, dan haka duk taɓrar da ruma take ba ta damunta.
Usman suka gaisa da Ammi, ammi ta ce wa Iman "Ina mai sunan baban?"
"Ƙarfe takwas suka tafi Lagos shi da yaya mahmud, wai wani abu za su je su yi"
Ammi ta ce "To, ni yanzu Mahmud tsoro nake ji, kar ya sake ɓallo mana ruwa, ba a gama da wannan tarzomar ba, kodayake tare suke da mai sunan baba, ba zai bari yayi wani rashin jin ba.
Aka sallami ruma daga asibiti, tare da jaddada mata yadda za ta kula da kanta, saboda ɗinkin da aka yi mata.
Mutane suka din ga zuwa barka, Adam yayi mursisi ya ce ruma ba zata tafi gida ba, gidanta za ta koma, a ɗaukko mai kula da ita.
Ya kafa hujja da mama ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba.
Gashi ya samu labarin su Huzaifa ne suka kawota asibiti.
Mai sunan baba kuwa lokacin da suka isa lagos, suka je gidan Alhaji Aminu, suka tarar yayi tafiya, Ade kuma ta koma Gombe!.
Ayshercool.
08081012143.
*WANDA KU KA KARANTA MINI LITTAFI BA TARE DA KUN BIYA NI HAKKINA BA, BA KUMA DAN BAKU DA SHI BA, IDAN KUN SHIRYA BIYANA HAKKINA GA ACCOUNT NUMBER NA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK*
Mahmud ya ce wa mai sunan baba, bai kamata su yi sanya ba, idan da dama kamata yayi kawai su tafi Gomben su bita can.
Mai sunan baba ya ce "Tayaya ni ban san a ina take a gomben ba"
"Tambayar mutanen gidan zamu yi, ba zamu yi sanya ba"
Ba tare da wani ɓata lokaci ba, mutanen gidan suka basu kwatancen in da Ade take, kasancewar sun san mai sunan baba.
***
Rumaisa kuwa gwaggo ce ta je zauna mata, saboda biƙi, mutane suna ta zuwa duba ruma tare da jajanta mata abun da ya faru.
Tana zaune a ɗakinta, suna video call da laila, sai kuka take yi mata, wai babyn ta ya mutu.
Laila sai rarrashin ta take yi, tana kwantar mata da hankali, tare da jaddada mata, idan komai ya dai-daita, lallai ta nemi maman Khadija, da maman ilham ta gyara, duk da yaron ya rasu, akwai buƙatar ta gyara jikinta sosai.
Rumaisa ta ce "To anty laila, in sha Allah ai ina da numbern su, ina Yasir".
Laila ta ce "Yaya bacci yake yi bai tashi ba"
Ruma ta ce "Inyee su yaya manya, ina fatan dai ba ya miki rashin ji?"
"Ba wani rashin ji, rashin ji ai sai ke, wallahi na ji daɗin zuwan Yasir gidan nan rumaisa, very kind and brilliant guy, darling ya yi masa registration ma, very soon zasu fara lectures, baki ga daɗin da babansu ya ji ba zuwansa, su anam ma suna ta murna"
Ruma ta ce "Sai wani yabon sa ki ke yi"
"Dole in yabe shi mana, dole a sarawa mama, yaranta gaba ɗaya masu tarbiyya ne da nutsuwa, ke ce kawai mara ji"
Ruma ta ce "To nima papa yana yabona, yana sona a haka"
"Ai shi dama ba zai ga rashin jin da ki ke ba. Yauwwa mimi ya hatsaniyar gidan kuwa ta lafa?"
"Ina fa lafawa, suna can suna cigaba da tashin hankalin su, ni ina nan ina fama da kaina, da mutuwar ɗa na, mummy sun watse da Hajiya Lubabatu, ashe Jabir lalata suke shi da ruƙayya, abun duk babu daɗi mahmud dai ya rufe shi"
Laila ta ce "Lamarin gidan nan sai Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya sa mu dace kawai mimi, bari na bari ki huta"
"To anty laila na gode sosai"
Tana gama wayar, Gwaggo ta shigo da kunun kanwa, ta ce ruma ta sha.
Ruma ta ce ita wallahi ta gaji da wannan kunun kanwar, gudawa yake sakata.
"To idan baki sha ba nonon ya zube ki huta ai, gyara ki nake son yi, na bayar da dawa ma a niƙota in sheƙa miki tuwo, ga yajin daddawar ki nan"
"Gaskiya gwaggo ba zan ci tuwon dawa ba, in haihu ki bani wani tuwon dawa taɓ. Kunu kuma ina da sauran sabayata, yaushe zan ta shan kunun kanwa cikina yana ciwo".
"Kya ji da shi dai, ana yi miki abun arziki kina na tsiya"
Haka rumaisa suke faɗa da gwaggo, komai sai ruma tayi raki.
Yanzu ma Adam ne ya je ya tarar da ita gwaggo na ta masifa, kamar ta ari baki, a kan rumaisa ta tashi ta je ayi mata wanka, tun yamma ake dafa ruwan, amma Rumaisa taƙi yadda ayi, ta maƙale tana kuka, wai wallahi fatarta duk ta dahu saboda ruwan zafi.
Takawa ya shiga ɗakin suka gaisa da gwaggo, ya dubi ruma ya ce 'Mimi meyasa ki ke da gardama ne?"
"Saboda ba ka ga uban tururin da ruwan zafin yake ba, da wanne zan ji, zafin haihuwa ko mutuwar ɗa na, ko na ruwan zafi?"
"Ai ni kin san bana jin zafin ruwa, zo mu je" yayi maganar yana miƙa mata hannu, ba kunya ta zagaye gwaggo ta bi takawa.
Gwaggo ta saki baki tana kallon ikon Allah, daga rumaisa har mijinta ba su da kunya ko kaɗan.
A banɗakinsa ya haɗa ruwa zafin dai-dai jikinta, ya taimaka mata, ta gyara jikinta ta yi wanka, sai dai rumaisa akwai langwai.
Suka fito ya bata abinci ta ci, sannan ya ɗauki magungunan ta ya bata ta sha.
Ya kalleshi ta ce "Na gode sosai papa, ya ku ke ciki a abujan ne, yaushe Abdallah zai dawo?"
Takawa ya kwashe komai da ya faru ya gaya mata.
Tayi ta rarrashin sa, tare da bashi tabbacin, Allah baya barin zalunci, amma kar ya ce zai cigaba da dagewa sai ya ga bayan wakili, saboda yana da goyon bayan manyan ƙasar.
Ya ce "Haka ne, in sha Allah na bar wa Allah"
Cikin dare rumaisa nono ya cika, ya takura mata da ciwo, saboda ba ta shayarwa, dan haka kwana tayi kuka, har da zazzaɓi.
Gaba ɗay tausayinta ya cika takawa, su mata komai na su abun tausayi ne, ta haihu ta rasa ɗan, amma akwai wani pain ɗin na daban.
Anty laila ya kira directly ya sanar mata, ta ce su yi haƙuri, da safe su kira maman ilham a waya, su sai maganin ta na gyaran nono, mace ko yaye tayi yana hana mata jin zafi, kuma baya bari nono ya lalace.
(0813