Showing 39001 words to 42000 words out of 58708 words
Chapter 14 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt
ya janyo hannu na, ya ce, "muje Amrah ".
Muka fito waje ta wata ƙofar yabi damu, ai kuwa sai cikin gidan har ƙofar ɗakin da muke da kayan mu a cikin sa, yazo zai wuce da sauri na ce, "wannan shine ɗakin da kayan mu suke ciki".
Kallon Amrah yayi ya nuna mata ta buɗe, ai kuwa ta buɗe muka shiga daga ciki a, tsakiyar gadon ya kwantar da Shuraim nima ya janyo hannu na, ya ce, ki kwanta, anan sai ki san dabar da zakiyi kafin ta shigo cikin ɗakin ki fito falon ki zauna, Amrah ke kuma ki kula da motsin Shuraim kin dai san wane mataki, ake cikin sa yan zun gashi yan zun ƙarfe biyu ta kusa na dare, kar ku ɓata lokaci please".
Gyaɗa masa kai mukayi, ya juya ya fita, muka rufe ɗakin muka kwanta, muka sanya Shuraim a tsakiyar mu, muna shafa sa har yayi bacci.
Waya na ɗauko nayi ta kiran layin Mrs barr amman ba'a ɗauka ba, Mrs Nazeer na kira, tayi saurin ɗauka, na ce, "kin kira layin Mrs barr kuwa?, nifa nayi ta kiran ta, har yan zun babu reply, to kodai kunyi tafiyar ku ne kun bar ni".
A cikin damuwa nake maganar gashi murya ta muryar kuka ce, dan har ta soma shaƙewa.
Da sauri ta ce, "nima fa tun ɗazun nake kiran ta, babu, reply anya dai ko mijin ta ya dawo ne, ta manta da maganar cika alkawarin bokan, ai kuwa kada tasa mu tafka asara, ki kira muna Mrs Naseer mu gani ko suna tare? "
Kashe wayar mukayi, na shiga kiran wayar Mrs Naseer itama sai da nayi mata kira ukku ta ɗaga, na ce, "haba taya zakuyi tafiyar ku, kubar mu, nida Mrs Nazeer, sai kiran wayar Mrs barr mukeyi taƙi ɗagawa kema sai da nayi kira ukku zaki ɗauka, da kun san ba zakuyi dani ba, da baku sa na kwaɗai tuba, da wannan aikin haba dan Allah! ".
Cikin tashin hankali tace, kika ce bata ɗaga wayar ki keda Mrs Nazeer anya kuwa tana lafiya dan ban taɓa ganin ta kasa cika wannan alkawarin ba, bayan daga wannan ta gama wahala nifa inada shakku a kai, indai ba ta ɗauki wayar ku ba, to batada lafiya, nima bacci ne ya sace ni dan ina zaune ina jiran ta kira ni, amman shuru kake ji kamar anshuka dusa, gaskiya da alamar tambaya "!?.
Kashe wayar mukayi muka ci gaba da kira ba amsa har Asubahi Amrah kuwa murmushi takeyi, tana ƙara gyara wa Shuraim kwanciyar sa, alwala muka ɗauro muka fara nafila, har aka kira assalatu, mukayi raka atainin fijri, mukayi sallar Asubahi, mukayi lazumi da azkar, sannan na fito cikin falon gidan nayi zaune na buga uban tagumi, sai kusan ƙarfe takwas ta fito a har gitse bata ma lura dani ba zata raɓani ta wuce nayi saurin shan gaban ta.
Na ce, "madam miye ya same ki ne mukayi ta kiran ki duk hankalin mu a tashe? "
Dafe kai tayi ta zauna daɓas a ƙasa tace, "nashiga ukku ni Haulart na rasa wannan damar ban san miye ya same ni ba, nayi wannan kuskuren nayi bacci mai mugun nauyin gaske, kira mani su a wayar ki suzo yau a gidan nan mu san abunyi, tun kafin guguwar nan ta taso ta dun ƙule guri ɗaya ta haifar da illar da aka ce, zata shafemu dukan mu! ".
Gir giza mata kai nayi, na ce, "duk suna a hanyar zuwa gidan nan saboda kowa da far gaba ya kwana saboda kiran da mukayi ta maki harda Mrs Yaseer a ciki ".
Shiru mukayi dukan mu ƙofar aka buɗe Miss Nazeer Mrs Naseer Mrs Yaseer a tare suka shigo a har gitse dukan su, indon su na akan Haulart saboda yan da duk ta birkice.
Mrs Nazeer ce ta ce, "Bafa zama zamuyi ba, kawai shawara ce, zamuyi mu samu mafita "
Mrs Naseer ta ce, "mafita kam babu ta, ta tashi kawai ta shirya mu ɗauki saƙon mu doshi cikin dajin nan wannan shine mafitar kawai ".
Ai kuwa duk sunyi na'am da wannan shawarar da sauri ta shiga cikin ɗakin ta har tan tun tuɓe da capet, ko wanka batayi ba, ta chanza kayan jikon ta, ta fito ko mayafi babu.
Kallon su nakeyi cike da mamaki Mrs Yaseer ta ce, "kinyi brush kuwa?.
Cike da masifa Haulart ta ce, "ke brush ya dama ni damuwa ta, ta fiye mani komai malama, kallona sukayi suka ce, muje, kada ki sa mu ƙara ɓata lokaci ".
Waya tace tayi ringing na ɗauka, nayi shiri na ajiye wayar na kalle su da kyau na ce........
"Comment and share*
*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
💐💐 *NARJEESAH* 💐💐
*Rubutawa*
*NANA KHADEEJATU*
*_UMMU IHSAN_*
*ELEGANT ONLINE WRITERS*
_*Bismillahir Rahmanin Rahim*_
4⃣1⃣⏭4⃣5⃣
➿➿➿➿➿➿➿➿➿ kafin na furta wata kalmar, Mrs Yaseer ta dakatar dani gurin faɗar, "kamar motar mijin ki nagani a waje shida yaran sa, kodai ido nane yake yi mani gizo? "
Cikin da mamaki Haulman ta ce, "barrister ka? ki kagani kuwa? ".
Da sauri Mrs Nazeer ta ce, "kina nufin cewar baki san ya dawo ba ko miye? "
Cikin fushi ta ce, "taya zan san ya dawo ne, bayan nayi nauyin bacci amman wallahi sai ya haɗu da fushi na, bari nadawo gurin da zani zai gane kuren sa wallahi, ke kuma NARSAL tashi muje dallah! "
Dariya nakeyi harda dafe ciki na gir giza kai na, nace to ina ajiyar taki ne ko duk fushin yasa kin manta ne".
Tsaki kawai tayi tace, "nama manta ne" da sauri ta nufi hanyar kichin, ni kam da ido nabi bayan ta dashi, tayi kusan mintina goma sai gata ta dawo a har gitse cikin tsananin tashin hankali, ta ɗora Hannuwan akai duka biyun ta kwatsa uban ihu tana faɗar, "na shiga ukku na lalace sun sace, mani shi sun gudu dukan su, ban same su ba! "
Tafaɗi ƙasa tana shure_shure ƙafafuwan ta, a ƙasa, kowa cike da tashin hankali suke faɗar su waye ne wai!?.
Ƙofar da ta fito take nuna masu, duk suka saka salati suna faɗar, "mun shiga ukku dai zaki faɗa" duk sukayi zaune daɓas a gurin da suke, ai kuwa wata irin uwar dariya ce, na kece da ita har ina tafa hannu, na tashi tsaye ina kallon su ina ci gaba da dariyar, ai kuwa suka tsare ni da ido cike da mamaki in banda Miss Yaseer.
Takowa nayi har inda suke ina fara zagayen su duk su ukkun, ina tafa hannu, sakin baki da hanci sukayi suna kallona harda murza ido.
Sai da na gama zagayawa na tsaya a tsakiyar su, nace, "to yau dai anyi walkiya an haska kowa, yau ne zaku girbi abunda kuka shuka, Miss Nazeer Mrs Naseer Haulman, ina son ku bani aron ɗan sauran hankalin ku da ya rage a nan, tun kafin ya ƙarasa ɓacewa".
Kallon su na sakeyi ɗaya bayan ɗaya, na sauke mayafin nawa na ɗaure a ƙuna, na ci gaba da faɗar, "Amrah...! "Da ƙarfi yanda zata jini, na ce, "ki shigo daga ciki mana".
Ai kuwa duk suka maida idon su gun da Amrah ta fito ai duk sai suka tashi a tsaye suna sauke ajiyar zuciya, harda su faɗar wai har hankalin mu ya kwanta a gaskiya ki daina yi muna irin wannan wasar yan zun ba lokacin wasa bane, da sauri Mrs Naseer tayi niyar tun karar gurin su Amrah wadda take ɗauke da Shuraim a hannun ta,
Da sauri na dakatar da ita gurin faɗar, "dakata saurin miye kikeyi ne, ai bari kiji ƙarshen zan cen wanda kike ɗaukar sa da wasa, wannan yaron da kuke gani da kun san waye shi da hankalin ku yafi hakan tashi ba kamar Haulman "
Sake ɗaure fuska nayi ganin irin kallon da suke bina dashi naci gaba da faɗar "yan zun lokaci yayi da wannan guguwar da kuke tsoro zata haɗu guri ɗaya" Shuraim na kalla ina murmushi na ce, my lovely Son Come with me, "
Ai kuwa da gudu ya sauka jikin Amrah yayi kaina da gudun gaske ya ce, "Mommy I miss you ".
Da sauri na ɗaga shi sama ina juyi dashi muna dariya ina faɗar ɗan farin fitilar gida, ɗan farin mai maye gurbin soyayya ko wace, iri ce, ina son ka ɗana ɗan albarka ".
Dariya mukeyi, cikin giɗima da fir gita suka haɗa baki gurin faɗar, "ɗan kiii.....! Kuma!? Ta ya ya hakan ta faru ne!?.... Kodai kinyi hauka ne!? ".
Kallon ban za nayi masu nace, "eh amman ba irin taku haukar ba, yan zun ɗan wannan abun har ya isa ya firgita ku hakan kuma harda zufa, ina ga nace, daku Shuraim ɗan manyan mutane ne, ɗan masu mulki masu, gari ba irin muƙamin iyayen wasu ba, wanda suke ƙare rayuwar su a gidan yari ba? "
Sannan na ce, Shuraim ina Daddyn ka su gan shi, ko da yake nasan yana kusa bisimillah ".
Ƙofar falon suka maida idon su dan ganin mai shigowa, kawai suka ga Salman ya shigo, suka ƙara kafe ƙofar da ido ko zasu ga wani ya sake shigowa amman sai sukaga babu kowa a bayan sa, sai suka maida idon su a kaina suna yi mani kallon raini.
Dariya nayi nace, "Shuraim Daddy...! " na nuna masa, ai kuwa da gudu yayo kan Salman, shi kuwa ya durƙusa ƙasa, ya tara masa hannu ya ɗauke sa, ya shigar dashi cikin jikin sa, yana juyi dashi, suna dariya.
Ai sai Haulman ta daka masa uwar tsawa kamar wani bawan ta, ta ce, "wannan wane irin salon wulaƙanci ne, malam ku ajiye wannan diramar haka, kuma wallahi sai ka gamu da matsanan cin fushi na! ".
Dariya ya yi, ya tako yazo inda nake, ya haɗani da Shuraim ya rungume mu, ya sakar muna pick ni a goshi Shuraim a kumatu, wani irin uban ihu Haulman ta saka, tayo kan mu amman kafin ta ƙaraso, taji muryar Salma na faɗar kada ki kus kura ki kai gurin da suke wallahi idan kuma ba haka nan ba, jikin ki ne zai gaya maki! "
Da sauri suka maida idon su akan Salma, sai suka ga Muhseen a tsaye yana murmushi shida Salma, Muhseen ya ce, "bisimillah ku shigo daga ciki ".
Ai kuwa Mai martaba ne ya fara shigowa shida fulani da Mom da Dad, sai Naseer da Nazeer da Yaseer, da Jafar Aliyu Humaira Hindu Auta Nusaiba sai Baban mu, hannu duk suka ɗora akai cikin fir gici, suka faɗi zaune sai jikin su ke rawa.
Salma ce tayi gyaran murya tace, "Narjeesh kici gaba please ".
Ni kuwa muna can muna halin da muka saba, mintsil sa nakeyi, harda cizo idan na faki idon mutane, shi kuwa magana yakeyi ƙasa_ƙasa, "yarinya komai abun ki tunda kika kawo kanki gida na ba zaki koma zuwa wani gurin ba, ehe! Kima zauna a kusa da mijin ki uban "ya"yan ki, wata kila naɗan sama maki guri a zuciya ta".
Tsaki na doka masa wanda ya fito fili, Amrah tace, "Auta jeki gurin su, kiyi masu magana suna can suna aikata halin su".
Ai kuwa da gudu tayo kan mu ta rungume ni ta baya, tana faɗar, "Anty Narjeesh nayi kewar ki keda my Shuraim".
Sai alokacin ne ya sakeni na jiyo na run gume Nusaiba muna dariya Shuraim da sauri ya ce, "Anty nima ban ganki ba, ki ɗauke ni ki goya ni kuma ki rama mani dukan da wan can tayi mani taci zali na, harda baki na ta doke har da jini da hannu na, kuma bata bani abinci bata, goya ni inyi ta kuka kuma bana buga boll bana, yin komai...! "
Hannun sa yana kan Haulman yana nuna ta da yatsan sa, da sauri Nusaiba ta ɗauke sa ta fashe da kuka tayi gurin Amrah dashi, itama Amrah kukan takeyi shi kuwa Baban ganin Nusaiba bata gane sa bane ya saka shi kamo hannun ta ya zaunar a kusa dashi, ya anshi Shuraim yana goge masu hawaye yana lallashin su.
Kallona, na maida akan, su Haulman naci gaba da faɗar, "Haulman kike koma waye, nasan yan zun kin fahimci wani abun, amman bari kiji yanda abun yake, na shigo cikin kune da tsabar wayau na da ɗaukar fansa, da ceto yaro na, Haulman tun kafin nazo garin nan nasan ki da ƙawayen ki da halin ku baki ɗaya, sai dai sam ban riga da nasan halin Miss Yaseer ba, sai da naji daga gareku, him! Haulman kama Dila sai an shirya tunda shi sarkin dabara ne, shi yasa sai da na shiryo na shigo cikin ku,
Tun ranar da kika sanar dani cewar Sunan ki Haulman ne, na fahimci Sunan ki ne dana Salman, ma'ana Haulart Salman, shine kika haɗa farkon sunan ki da ƙarshen sunan Salman, wato Haul Man, ni kuwa shi yasa na , buɗe sunan naku wato Haulart Salman, nayi dariya nima shine na sanar dake, NARSAL wato, Narjeesah Salman, kin ga na ɓatar dake, tun daga nan nabaki labarin dana ƙir ƙira, da kaifin basira ta, dan na daki cikin ki, naji sirrin ki, kuma Alhamdulillah kwalliya ta biya kuɗin sabulu, nasan komai naki kuma na sami yarina ƙarin farin ciki harda mahaifina na".
Na nuna Baban mu, da hannu na, da sauri Nusaiba ta kafe sa da ido ya sakar mata murmushi ya rungume ta, haka gurin kowa yake mamakin taya hakan ta faru.
Kallon Yaseer nayi nace, Yaseer a jiya dana tafi gidan ku, kai da matar ka, ban san tan da akayi kuka gane wace, ce niba, kuma narasa taya akayi har kuka san shiri na wallahi badan matar ka, tayo mani test ba, akan kada na yarda da nadamar Miss Naseer ba, da kun saka asiri na ya tuno, amman Allah ya kyauta, Haulart ni ban taɓa kawo wa kaina cewar zaki iya sace, Shuraim ba, saboda nasan baki san niba, baki san wace ce niba haka Shuraim duk da kuwa kammanin Salman da ya ɗauko, na manta cewar kina bibiyar duk wani motsin Salman, kuma na manta cewar zaki iya aikata komai akan Salman, sai da aka lurad dani hakan na fahim ta, koshi kuwa sai da su Jafar suka tuna sar dani cewar har na manta yanda akayi kika sato ni kika haɗa da mijin ki har zan kasa fahim tar, aikin ki? ".
Cikin da razana take kallona, nayi dariya na ce, "kwarai kuwa ban san kammanin ki ba, amman nasan labarin ki, sai da Salma ta turo mani photon ki dana kwayen ki iri daban_daban da bayanin garin ku da shige da ficen ku, da gurin da kuke zuwa, da yanda al'adar ku take, dan haka ne, aka shirya mani wannan tafiyar wadda ban san wanda ya biya kuɗin jirgi da direban da suke zirga_zirga damu, ke harma da gidan da muke zaune, nidai nasan Salma ce ta tsara, amman ita da waye shine ban sani ba, Salma ya abun yake, a ina kika sami wannan shawarar?
Dariya Salma tayi tace, "am dafatan duk kuna biye damu, to a zahirin gaskiya kowa yasan bana shiri da matar Yaya Salman ballema nasamu photon ta, dan bana jin zan iya ajiye photon ta, a waya ta, haka zalika ni ko kallon ta bana son yi ballema naji labarin ta, to abunda yasaka na ce, ita ce zata iya aikata hakan saboda, nasan yanda take bibiyar rayuwar bro, kuma nasan yanda bata son ya raɓi kowa ne, ɗan adam nasan zatayi tunanin yana da alaƙa dashi duk da, kuwa a lokacin shi kan sa bro da Anty Narjeesh basu san, alakar dake tsakanin su ba, har sai kusan ɓatan Shuraim da kusan wata ɗaya koma fiye, tun lokacin da bro ya sanar dani komai, kuma ya tabbar mani da cewar ya ɗauki Shuraim a ranar kuma a ranar aka nemesa aka rasa, to kawai na fahimci cewar aikin Haulart ne, shi yasa na nemi shawarar wanda zan Aura a lokacin, shine ya taimaka mani, haka, Muhseen shima ya bada tashi gudumawar, a gurin wanda zan Aura ne nasami photon su da bayan su cikin sauƙi ba tare da nasha wata wahalar ba, amman kuma ma sauki da direbobin da ke zirga_zirga da ku da gidan da kuke zaune ba aiki na bane, aikin Muhseen ne, Muhseen kai muke saurare".
Gyaran murya Muhseen yayi yace, "a lokacin da na fahimci miye Sister Salma take shirya wa ita da Narjeesh, shine na, sanar da direba na ya ɗauko su a hanya ya kaisu airport, kuma a hannun Salma na anshi photon su Anty Narjeesh naje, gurin abokin karatuna a airport domin ina son yayi masu komai a cikin sauri kuma Alhamdulillah nasami yanda nake so, haka na kira abokina kuma amini na, Al'amin akan buƙatar su Anty Narjeesh su zauna a gurin Ummeyn su, kuma yayiwa abokan mu bayani sune zasu riƙa kaisu duk gurin da na kira na faɗa ina bukatar aikaisu, ai kuwa haka, suke bin umarnin na, sun bamu haɗin kai ɗari bisa ɗari, harda su sauya suna akan sunayen "yan kauye wannan ke nan".
Salma taci gaba da faɗar, "tun daga lokacin muka fahimci su Anty Narjeesh sun sami nasarar shiga a gurin su Haulart muke neman yanda zamuyi, su sami ɗaukar Shuraim, gashi mun sami labarin tafiyar dare ne, duk hankalin mu a tashe yake, mun rasa mafita, gashi duk mun haɗu a guri ɗaya nida Muhseen da Yaya Jafar da Yaya Aliyu da ita Anty Narjeesh da Amrah da muke waya, dasu, suna sanar damu halin da ake ciki, na tabbar da cewar Shuraim yana gidan kamar yanda Miss Yaseer ta sanar da ita, gaskiyar lamarin, ai kuwa kamar daga sama, Bro ya fisge wayar ya kashe idon sa yayi mugun ja saboda ɓacin rai, duk sai da muka tashi tsaye, muna zarar ido, cikin ɓacin rai yace, "haba taya zaku riƙa ɓoye mani halin da ake ciki bayan mata ta da ɗana da "yar uwar ta suna