Header Ads
Showing 54001 words to 57000 words out of 58708 words

Chapter 19 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

na tashi na ce, "mu fara gyara gidan sai muyi wanka muyi sallah mu nemi abincin da zamuci ko? ".




Dariya ya yi yace, "nima hakan naga zai fi".




Ai kuwa a take muka hau gyaran gidan har ɗaku nan na ƙasa da sama, da kichin da bayi duk sai da muka tsab tace komai, san nan, na haɗa masa ruwan wanka ya shiga ni kuma na dawo falon na kunna kalli sai da ya fito ya saka kayan shan iska, nima na shiga nayo wankan na fito ke nan, naga ya a jiye mani kayan da zan saka na shan iska ina ɗaukar rigar da guntun wandon, na ajiye na ce, "kam lallai ma, taya zan iya saka wannan yan iskan kayan na fito falo, na zauna? Ni kam ba zan iya ba, haba kamar wata yar iska dai! ? ".






Hijab na saka, gashi towel ɗin ƙarami ne, baya rufe mani cinya ta, ai kuwa na soma faɗar "Daddyn Shuraim! Daddy Shuraim..! Kazo Allah ni ba zan yarda ba, haka kawai a ce, na rasa kayan da zan saka sai wannan kayan haba ɗan Allah, kuma kace naje na zauna kamar wata marar kunya? "




Ido rufe nake ta masifa, shi kuwa ya shiga cikin ɗakin ya harɗe hannayen sa, yana bina da ido, ganin ba zan dai na masifar bane, kuma ba zan buɗe idon bane, ya saka shi yin wani makirin murmushi, ya matso dab dani, ya fisgen hijab ɗin, ya riƙe a hannun sa, ya zuba mani ido kallona ya keyi tun daga sama har ƙasa, ko ƙyafta ido ba yayi.




Ni kuwa mutuwar tsaye nayi, cikin fir gici na, buɗe ido na zaro su waje, ganin abunda ban shirya ba, a kuwa da gudu na juya zan faɗa toilet na rufe kawai, taku biyu yayi ta tare ƙofar shiga bayin na faɗa jikin sa, ai ban san lokacin da na kwatsa masa wank uban ihu ba, sai da ya rufe mani baki da hannun sa.




Ya ce, "wallahi idan baki saka wannan kayan ba, yau sai dai ki zauna da wannan towel ɗin kuma ba zaki saka wannan hijab ɗin ba, ke nama fasa kada ki saka wasu kayan kiyi zaman ki a hakan kin fi ma burge ni, wallahi ".




Ai tun da naji yayi rantsuwa kuma dai naga ya ɗaure fuska kawai, na ce, "dan Allah Daddyn Shuraim kayi hakuri Allah zan saka kaga bama zanyi sallar ba, kaje kayi sallar kawai ni na yarda in dan wannan kayan ne Allah ".




Dariya ya yi, ya ce, wato dai aboki na ne ya zo, ashe dai nan da wata tara zaki sake haifo mani yan biyu, ko ƙuratul aini? ".




Jin nakeyi kamar na nutse saboda tsabar kunya amman Daddyn Shuraim ya sauya mani lokacin ƙan ƙani, kwata_kwata, ya ajiye kunya a gefe, sai zuba mani fitsara yakeyi.




Kuka na fara harda hawaye, ya ce, "ashe ko dai zan cire wannan towel ɗin yan zun sai naga yan da ake kukan shagwaɓa".




Ai haɗiye kukan nayi, na ce, "nifa kukan yunwa ne nakeyi ba wani kukan ba".




Dariya yayi yace, "haba dai ƙurratul aini, ai nasan halin basajar ki, yan zun jeki ki saka kayan bara na kawo maki pad da fant, na tausaya wa yar yarinyar nan, kai na gode wa Allah fa, na Auri yar shekara sha shidda gani da ɗa kusan shekara biyar kuma ita matar yan zun zata cika shekara ishirin kai nikam ɗan baiwa ne, yan zun take zama cikak kiyar mace, wayo Allah na....!, kai ƙurciya zallar ta ".




Rasa bakin magana nayi, daman tsokana ta ce, yakeyi kuma tsokanar ta samu shiga, dan hawaye naci gaba dayi".




Da dariya ya mai dani gefe, ya je ya ɗauko kayan ya bani ya fita yana dariyar keta gashi da hijab ɗin ya fita, hawayen na shiga sharewa, shigo wa ya sake yi ya bani leda ya fita yana, lasar baki yana shafa sajen sa, da harara na bisa har yaja ƙofar.




Haka na shiga na shirya, na saka kayan rigar mai haɗe, da gidan bra, kuma hannun bra ne da ita, iyaka cibiya, ta tsaya, sai wandon iya karsa, cinya, kasa fito wa nayi, nayi zama na a cikin bayin gajiya yayi da jira na, yazo ya buɗe bayin ya shigo yaja hannu na muka fito waje bai bari muka haɗa ido dashi ba, muka dawo cikin falon ya zauna akan kujerar ya zaunar dani akan ƙafafuwan sa, ya janyo abincin da yayi order aka kawo masa, ya buɗe ya soma bani, a baki, ganin bai ma damu yanda nake shigewa cikin jiki na ba saboda kunya, sai da ya tabbar da na ƙoshi ya bani ruwa, sannan ya soma ci, har ya ƙoshi.




Ya ce, "to ki tashi kije ki shirya sai ki dawo muyi fira kuma idan baki dawo ba, da kaina zan je kin dai san sauran ". ya kanne ido ɗaya.




Tashi nayi jiki babu lakka na nufi cikin ɗakin, naje nayi sha, fa mai na fesa turare da humra nayi, sai yar powder da jan baki, na tashi gashi ina jin kunyar sa, haka na fito na samesa yana kallon labarai, naje na zauna a kusa dashi yasa hannun sa, ya dawo dani sosai a jikin sa, mukaci gaba, da kallon a tare, har naji bacci, a jikin sa na kwata ya gyara mani kwanciya, a take nayi bacci.




Shi kuwa koda ya gama kallon ya kashe kayan kallon, ya ɗauke ni, ya kaini, ɗaki ya kwantad dani shima ya shiya ya kwanta yayi muna addu'a, nikam saboda tsabar gajiya bacci sosai nasha, sai a suba na falka, ina buɗe ido kawai na tsinci kaina, kwance a jikin mutum da sauri na yuƙura zan gudu ya janyo ni nadawo ya ce, "gudun na miye madam? Bayan duk kin bi kun shure ni da ƙafafuwan ki, kin zubo mani yayun bacci "




Nikam ban san lokacin da na ce, "wallahi ban yarda ba, ina da ja ni bani da nauyin bacci kuma bana saleɓa, kai sai dai idan kaine kake yi, ni rabu dani, naje na gyara jiki na, malam, haka kawai kazo kana yi mani cin kashin kaji? ".




Dariya ya yi, daman burin sa ke nan yaga ina masifa, kuma iyakar gaskiya ta na keyi, tashi nayi nace, "ka bani kayan da zan sauya ni kam, wallahi ko kuma ka nuna mani inda suke kaji? ".




Ya ce, "aa malama zo ki doke ni, ki ɗauki kayan kin ji...? Matar Salman? Uwar ya'yan Salman yar yarinyar Salman, mai ƙuruciya, shagwaɓaɓbiya t.... Maman Shuraim ƙurratul aini, nikam yau dai da kai na zan yo maki wankan nan fa bari na tashi dai na cire maki wannan kayan ".




Ai at 3√6o na faɗa jikin sa, na rufe ido na shige jikin sa, sai dariya yakeyi, ganin ya samu abunda ya keso naji, kunya, sannan ya ce, "ni tashi mani a jiki kada ki karya ni, kin ga kayan ki can a wan can seat ɗorowar, kuma sau ran kan yan suna a ɗaya dorowar, maza jeki ki fito kizo muyi baccin safe".




Kayan naje na ɗauka, na ce, "halan kayi sallar ne da zaka sake yin baccin? ".




Ya ce, "kina can kwance kiji fata mai laushi a baki sanin na tashi ko ban tashi ba, amman zan rama nikam dan ba zan yarda ba ".




Kyalesa nayi na shiga ciki bayin nayo wanka, da brush na shirya na fito, koda na fito yayi bacci, nadawo na kwanta a gefen sa, na kwanta sai bacci.




Sai sha biyu muka fito muka nemi abunda zamuci, bayan mun ci, muka fito muka nufi falo, ya ce, "muje ki sauya kayan nan mu fita ki gano gari".




Cike fa farin ciki muka dawo cikin ɗakin ya ɗauko mani sweater da dogon wando, da gyale nayi rolling ɗin gyalen, shima irin shigar mu ɗaya, har ta kalmi, muka fito, hannu na a cikin nasa hannun, muka fita yawon shaƙatawa, kai nikam sai dai na ce Alhamdulillah.




Birnin london kam mun zaga shi sosai nida Salman tattali da soyayya da kulawa duk ina samu, a gurin Salman, ga tsokana kamar miye? Wata rana har sai taga ina kuka yake dawowa yayi lallashi, babu abunda na nema ba rasa a gurin Salman, gidan su Mom munje ya kai sau nawa, a gurin su ma nida Shuraim gata suke nuna muna, har gurin dan gin Mom ya kaimu, a masarautar su Mom kuwa kwana biyu ne kawai muke tsallakewa.






Zaune muke nida Daddyn Shuraim ina sha masa ƙamshi shi kuma sai famar dariya yakeyi, ya ce, "ke kuwa wannan haɗe ran fa ba zai hana anjima na sake yi maki wani wa'azin ba, keda naga harda su kabbara kikeyi mani, saboda tsabar ɗaukar wa'azi, ai my love, kin iya bada hankali gurin ɗaukar wa'azin Mr Salman Daddyn su Shuraim da 'yan uwan sa ".






Filo na jefa masa ya ci, gaba da dariya, yana tsokana ta, na ce, "yau ma nawa ga wata ne? "


Ya ce, "oh zaki fara lissafin cikin wata nawa ne? Yau dai kwana ɗay... "


Da sauri na haye saman jikin sa, muka shiga ko kawa, dashi ina son rufe masa, baki, shi kuma yana son ƙasawa, sai da muka gaji muka baje a gurin.




Haka dai rayuwar mu, taci gaba tafiya cikin kulawa, da tattali da ƙaunar juna muna kiyaye duk wani abun da zai bamu matsala a zaman mu dashi, cikin ikon Allah watan mu biyar a ƙasar, wata ranar labara na tashi da ciwon ciki mai tsanani, a ruɗe ya ɗauke ni, ya kaini asibiti gwajin farko, aka sami kyakykyawan result, Allah ya bamu ƙaruwar cikin wata, ukku, da sati biyu, murna a gurin mu ba a faɗa, su Mom ya kira ya sanar dasu, ai kuwa koda muka dawo gida a nan muka same su harda Muhseen Mom Dad Shuraim,




dan Salma ta daɗe da komawa Nigeria, sai tambaya ta sukeyi miye zan ci, ko miye nake so, kuma sun ce, kada ya yarda ya cika matsa mani da takura mani, duk abunda nake so, yayi mani ko a kira su a sanar dasu Shuraim kuma ya ce, ba zai koma ba, a nan zai zauna ai kuwa korar sa, Salman ya yi, wai kada ya takura mani ya riƙa saka ni yawan magana, nikam dariya suke bani, kuma da yaga Shuraim yayi fushi sai ya fasa barin a tafi dashi, dole aka bar sa, daman sun san ba zai bari a tafi dashi ba, dan mun sha zuwa ɗauko ana hana mu.






Haka dai akaci gaba da tarairayya, ta, har Allah yasa cikin ya kai watan haihuwar sa, har kwakin haihuwar da aka bamu ya wuce, zama daket tashi da ket, Shuraim wata rana har kuka yakeyi, idan yaga ina son tashi tsaye na kasa, Salman kuma jin yakeyi kamar cikin ya dawo a jikin sa, wata rana shi da kansa yake ɗauka ta ya tayar dani tsaye mu fara tafiya saboda motsa jiki.




Yau kam tun da na tashi nake jin ba dai dai ba, ciwo_ciwo sama_sama, tun ina jin kamar da wasa har na kasa hakuri, nace, "Shuraim kira wo mani Daddyn ka, wash...! "





Ai da gudu suka iso baiyi wata_wata ba, yazo ya ɗauke ni, Shuraim ya buɗe muna motar muka shiga, sai asibiti ai da sauri muka ƙarasa, yana yin parking, ya fito ya ɗauko ni, abu da ƙasar waje kawai sai ga ma'aikatan asibitin sun zo da gadon ɗaukar masu ciki, suka bar su a nan baya aka shiga dani, aka hana su shiga sai go and come sukeyi tare da addu'a Shuraim kuka kawai yakeyi.




Cikin ikon Allah ko a awa ba'ayi ba Allah ya sauke ni lafiya, aka sami yan biyu namiji da mace ai kuwa zo kuga irin yanda su Salman suke tsalle da hamdala, ɗakin da aka kaini futu suka shiga, idon su, a kaina, sai da suka tabbar da lafiya ta lau sannan suka ɗauki yaran sai dariya sukeyi, sai alokacin ya kira Mom yake sanar da ita, ya kira Dad da Muhseen da Salma sai ya kira Yaya Auwal dasu Jafar, kai Salman kusan sai nace, zaucewa yaso yi sai da na anshe wayar dan photo yake ɗaukar yaran iri daban_daban yana posting ɗin sa.






Mom na zuwa ita dasu Dad kowa guri na ya fara zuwa sai da sukaji lafiya ta, sannan suka ɗauki yaran wanda Muhseen da Shuraim suka kan kane gurin sun hana kowa ɗauka, Mom ce ta anshe yaran ta kore su, awar mu shidda aka bamu sallama bayan a duba lafiya ta da lafiyar yaran, muka dawo gida ai kuwa sai shirye_shiryen zuwa gida Nigeria akeyi wanda Mai martaba ya bada umarni, sake shirya wa mukayi, dan Muhseen ya tafi da Shuraim airport mune kawai ake jira, haka muka fito cikin farin ciki muka nufi airport ɗin, bamu wani jima ba jirgin mu ya ɗaga sai Nigeria.




Da misalin ƙarfe biyu na dare muka iso, ai kuwa motocin Mai martaba ne suka ɗauke mu sai fada, muna isa bakin kofar faɗar kamar rana haka muka sami gurin cike da mutane, fulani ce da kanta ta janyo hannu na, muka shiga cikin gidan wani ɗakin ta nufa dani, muna shiga tace, "ki kwanta kiyi bacci ki futa har zuwa da safe kinji jika ta? ".




Murmushi na sakar mata tare da gyaɗa mata kai na, ta juya ta fita ni kuma baccin gajiya ne ya ɗauke ni akan wannan gadon na alfarma, ban falka ba, sai gurin ƙarfe takwas na safiya, ina falkawa sai a idon fulani ai kuwa da kanta ta kaini bayi, tayo mani wankan da ba zan taɓa manta irin saba, a rayuwa ta, muna fitowa ta shirya ni da kanta, aka kawo yaran duk an gyara su, sai uban ƙamshi suke zuba wa, harda Shuraim a biye dasu, shayar dasu nayi, aka fara jero mani abun kari nama rasa wane zan ci wane zan bari, Mom ce ta shigo cikin ɗakin da kanta ta soma ciyar dani har sai da na ƙoshi.




Anan ne Fulani da Mom suke sanar dani cewar, Mai martaba ya ce, zamu zauna ne a fara yin walima sannan mu tafi gurin su Umma na, dan za'a haɗa ne da bikin naɗin sabon sarki.




Na ce, "babu damuwa duk yan da kuka tsara mu masu biyayya ne".




Ai kuwa sun ji ɗaɗin wannan maganar tawa, har sai da suka nuna farin cikin su.






Tun daga wannan ranar fulani da Mom sune suke kulawa dani har zuwa yau da mukayi kwana shidda kuma yau ne walimar, walima ce, wadda ta tara manyan malamai sarakai masu mulki da masu muƙamai talakawa da masu kuɗi, samari da yam mata, yara da manya, tsoho da tsohuwa, su Salma da su Humaira dasu Amrah tun daga lokacin da suka zo jiya basu futa ba, sai kai komo suke yi, anyi walimar lafiya an watse lafiya.




Sai shirye_shiryen zuwa gida kawai mukeyi, muna gamawa, aka ɗauke mu cikin motoci na alfarma muka nufi garin Yola domin ƙarasa wannan gagarumin bikin, cike da ɗoki nake son na buɗe ido na, naga irin farin cikin da Umma na zata nuna mani da na cika mata burin ta, su Hindu da Salma sai tsokana ta, sukeyi, ina share su.




Saboda tafiyar Asubanci ce mukayi kuma bamu tsaya ko ina ba, zuwa ƙarfe goma muka iso, ƙofar gidan mu, muna sauka da sauri nabar yaran hannun su Amrah nayi cikin gidan da gudu ina kiran Umma..! Inno...! Yaya....! Gani nazo na ganku".




Dariya suka sakar mani cike da farin ciki, Mama ta rungume ni, ta ce, tunda ni badani ba, a cikin mutanen da kike kira ni na fara tarbon ki.




Da sauri na rufe ido alamar naji kunya nace, "Afuwan Mama duk cikin mararin ganin kune".




Inno ce, tace, "munyi farin ciki da ganin ki, amman ki daina gudu ba kyau".




Dariya nayi na faɗa jikin Inno, haka su Amrah suka same mu, Yaya ma rungume ni tayi, yan gidan kuwa, gurin ɗaukar yaran suka nufa idan wannan ya ɗauka sai wannan ya ɗauka, nikam hayewa sama nayi, na nufi cikin ɗakin Umma, ai kuwa tare da mutane na sameta, suna jin sallama ta, duk suka taryeni tare da yi mani barka, duk suka fita, aka barni nida Umma sai Mama Luba, jikin Umma na faɗa ina dariya ta fara shafa mani kaina, tana murmushi, Baban da ya shigo cikin ɗakin ya ce, "wa nake gani kamar Narjeesah na? ".




Ai da sauri nayi kansa na faɗa jikin sa ina dariya sosai mukayi farin ciki a cikin ɗakin Mama Luba ce, ta ce, "Narjeesah Ashe ansami ƙaruwa Allah ya raya, am sai kuma gashi kin sameni a cikin gidan ku, dan Allah ki yafe ni laifin da nayi maku na cin mutumci ta korar wula'kanci sai gashi kuna barin garin komai nawa ya lalace hayar ma dana ke biya na kasa biya, ke daga ƙarshe ma na rasa komai nawa sai bara nadawo ina yi a rin wannan rayuwar ne, Allah ya kawo mani Umman ku, ita ce ta zo dani har ta bani kuɗin ɗaukar wani gidan hayar, tare da kuɗin siyen kayan ɗaki da sutura, haƙiƙa gaskiyar magana na yarda hassada ga mai rabo taki ce, ku yafe ni ".




Murmushi nayi, na ce, "nikam na yafe maki bana iya riƙe kowa a zuciya ta, Allah ya yafemuna baki ɗaya ".


Kowa ya ce, "Amin".


Cikin falon muka dawo Baban mu kuma ya fita, muka soma fira da su Amrah har nake tambayar ta sauye_sauyen da nagani, ta ce, "duk aikin Yaya Salman ne, dan dashi da Shuraim duk ƙarshen wata, suna zuwa su kwana biyu, shine ya baiwa Umma dasu Inno jarin miliyan biyu_biyu, su Yayan mu kuwa, aiki ya nema masu, mukam dubu ɗari biyar_biyar ya baiwa mata mu dogora da kan mu, yara dubu hamsin_hamsin,






Sai kuma provision ɗin da buɗawa Baban mu, sannan ya baiwa duk su Yaya mota, harda Baban mu ai kin ga gidan cike da motoci, sannan wan

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads