Header Ads
Showing 45001 words to 48000 words out of 58708 words

Chapter 16 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

mu, mukayi parking, duk muka furta "Alhamdulillah",




Bamu fito ba muna daga cikin motar, kusan mintina biyar, idon mutane, yana akan mu, Yaya Auwal ne ya fito daga cikin gidan yana kallon motocin, a kuwa nida Amrah da gudu muka buɗe ƙofar motar muka fita da gudu muka faɗa jikin sa, muna hawaye, cike da mamaki da farin ciki ya ce, "Alhamdulillah Alhamdulillah Amrah Narjeesah kune nake gani da ido na? Ina Umma ina Auta Nusaiba ina yaron nan Shuraim? ".




Yaya Aliyu ya ce, "to taya zasu iya amsa maka duk wannan tambayar lokaci ɗaya, ka bari ku shiga daga ciki ku zauna mana ".




Dariya Yaya Shuraim ne ya ƙaso gurin yana faɗar "Mommy waye ya dakeku kuke kuka, na kira Daddy na, nasar dashi yazo da Bindigar sa ya rama maku? ". kamar zaiyi kukan shima






Da sauri Yaya Auwal ya janye mu daga jikin sa, ya matsa, ya ɗauki Shuraim yana dariya yayi cikin gidan dashi, mutane kuwa tuni labarin zuwan mu ya riski kowa.




Inno ce ta fito tana gyara ɗaurin zanen ta, ta ce, "dama nadan duk daren daɗewa zaku dawo, toni yan ban zanga kuzo na rungume ku mana".




Ai da gudu mukayi kanta har da Auta da ƙaraso gurin mu, rungume ta mukayi, kuka ta fashe dashi taja hannun mu kukayi cikin gidan, kallon gidan mukayi duk an sauya masa tsari icce dalbejiyar mu yana nan, amman ɗakin Umma babu shi kwata_kwata wasu ɗakuna ne akayi daga baya, a tsakiyar gidan cikin inuwar icce inno ta saka akayi muna shimfiɗa muka zazzauna, Shuraim ne suke fira shida Yaya Auwal yana bashi labarin Daddy sa, suna dariya Inno kallon mu takeyi ta kalli Shuraim.




Ta ce, "wai nikam Amrah yaron nan ne yayi wannan wayon haka? "




Dariya mukayi Yaya Aliyu ne ya ce, zan je nadawo Shuraim kayi mani rakiya mani"




Da sauri ya tashi yana murna, Inno ta ce, "kuce ɗan naku swai_swai ne jirgin yawo to ayo muna tsara dai".


Dariya mukeyi Shuraim ya ce, "zanyo maki tsaraba mai yauwa ko Uncle? "


Dariya yayi masa ya shafa kansa, Inno ta ce, to da kuɗin waye zakayi mani wannan tsabar mai yauwa, dan nasan kai dai ba kuɗi ne da kai ba, baka da ko naira". Tana yi masa dariya




Fuska ya ɗaure ya ce, "Uncle Daddy na yanada kuɗi masu yawa ko? Kuma shine zai bani kuɗi nayo maki tsarabaaa".


Dariya akeyi masa antaru a gurin harda maƙota da yan gidan wanda bamu sani ba, baƙin fuska, Humaira da Yaya Jafar suka shigo da sallama da sauri Shuraim ya nufesu yana yi masu oyo kuma sai dawo "mun riga ku, wallahi"


Ɗaukar sa Yaya Jafar yayi ya shillashi sama, suna dariya.


Humaira a kusa da Inno ta zauna tana gaisawa da ita, ta ce, "wash Allah na gaji, Inno a bani filo na kwata naɗan futa".




Cike da mamaki Inno ta kalle ta ta ce, "da alama jiki na ne yake wahalar mani da 'yata ".




Dariya muka shiga yiwa Humaira Inno tayi mata tonon silili, rufe ido tayi, kawai aka kawo mata fillon ta ce, "to malama Narjeesh matar shugaba Salman ".




Duka na kai mata, Inno ta tare, tare da faɗar "kada ki kusa dukan ta a gaban idona, Allah zan saɓa maki".




Baki na turo na tashi daga gurin nace, "ai inda Yaya tana nan da sai ta shigar mani, nima".




Dariya suka saka mani, ina hara rar su, harda kyabci nakeyi masu.


Su Yaya Aliyu kam tafiya sukayi, sai ga Yaya ta shigo tana faɗar "Inno da gaske dai sune suka zo"




Da gudu mukayi kanta mu ukku run gume ta, muna dariya, itama kukan ta saka tana faɗar, "miyasa kuka daɗe baku wai waye muba, ne duk kun tafi kun bar mu da tunanin rasa sanin inda kuka shiga, munyi nema munyi cigiya gashi Allah ya dawo muna daku cikin ƙoshin lafiya, ina Umman Nusaiba, ina fatan tana lafiya naga anfito da yaro ƙarami baƙi nakuwa san cewar shine yaron da kuka tafi dashi yana jin jiri"






Dariya muka shiga yi, hannun mu taja muka ƙarasa muka zauna sai tambayar mu take "kuna lafiya ya bayan rabuwa, Narjeesah duk kun sauya muna kamar ba ku ba"




Humaira ta ce, "Yaya ai ita Narjeesah Daddy Shuraim ne yayi mata wannan gatan bakiga irin yanda suke zuba soyayya ba, ke da zamu zo harda kukan rabuwa sukayi harda cewa tayi wai ita ba zata zo ba, sai dai mu muje ita ba iya barin mijin ta, ya zauna shi ɗaya".




Ido na zaro waje na ce, "ke Humaira Allah Yaya kada ku yarda da uwar sharrin nan, Allah ƙarya takeyi maku! "




Hindu ta ce, "Inno da gaske ne bata son mu faɗa ne kawai amman ko yan zun hankalin ta yana gurin gurin sa da kuka suka rabu dashi ".




Tagumi na zuba ina kallon su, Anty Basira ce da Shamsiyya da Hanan Haule, Hannatu Yaya Halilu Yaya Hamza, Yaya Mudarsir Anty Asma duk sune suka shigo cikin gidan kamar wanda aka koro su, zuwa can kafin su zauna sai ga goggo da Kawu Bala har yan cin tun tube da babbar rigar sa, kamar zai kife, Mama ce, ta fito tana ɗir gisa ƙafa duk tayi baƙi ta fita hayyacin ta.




Su Humaira duk sai suka maida hankalin su akan wannan mutanen dake ta shigo wa, mu kuwa kallon kowa mukeyi ɗaya bayan ɗaya.




Kawu Bala ne ya ce, "kamar dai naji ance, wai su Nusaiba ne suka dawo kodai mutane basa gani da kyau ne kuma basu dai ji abunda ake faɗa da kyau ba, har kasuwa akaje aka sheda mani, ɗan achaɓa ne ya kawo ni gidan nan".




Duk a daburce yake magana, Hanan ce tayi dariya ta ce, "wallahi sune suka dawo Narjeesh Amrah Nusaiba kun dawo kamar wasu "ya'yan turawa" tana dariya tayo kan mu ta zauna a kusa damu tana cike da farin ciki ta ce, "ina Umma da Shuraim? ".




Humaira ta ce, "ko bamu tambaya ba nasan wannan ita ce Hanan".




Dariya mukayi tashi Hanan tayi, ta ƙarasa gurin su, aikuwa sai fira kamar sun daɗe da sanin juna.




Kallon Inno nayi batare da na kula da kowa ba a gurin na ce, "Inno tare muke da Umma da kuma wani babban al'amarin daya shafe mu baki ɗaya".




Cike da mamaki kowa yake kallon mu, suna mamakin wane babban al'amari ne da yashafi kowa a zuri,ar mu?




Kawu Bala ne ya ce, "badai wani cikin ki sake yowa ba, ko wannan ce ma tsaurin idon tayo shi, to ba a gidan ba, dan kun san baku da gado a cikin sa".


Da sauri Hindu ta ce, "gado kam ai ya tashi tunda mamalkin gidan da ransa bai mutu ba, nifa wallahi ba zan iya jurar abunda su Narjeesah suka jura ba, ehe! ".




Humaira ta cafe tace, "waifa gado ina ma wani gadon yake ne, malamai bari kuji, ita fa Narjeesar nan da kuke gani zaune a gaban ku, ku kiyaye sakin duk maganar da tazo a bakin ku, saboda idan masu tsaron lafiyar ta, sukaji zasu iya datse wa mutum halshe dan haka mutum ya kiyaye, kawu Bala kaida goggo da Mama kubi a sannu dai ehe! "




Kowa kallon su Hindu yakeyi cike da mamaki, goggo ta ce, "to da alama dai ankai maku ƙarar mune dan naji kuna furta Sunan mu kamar a bakin ku aka zana shi ki? ".




Amrah tayi dariya ta ce, "wato dai mu bamu da aiki sai tara "yaya kun maida mu fasiƙai, to Alhamdulillah duk cikin mu babu wanda ya taɓa zubar da cikin shege kuma, yan zun da mutum yasan wace ce Anty Narjeesh da ɗan mu Shuraim da zufa tayi ta zubo masa! "




Ni kuwa nayi saurin faɗar ku ce, dasu da sun san abunda muka zo masu dashi da wasu sun kusa sumewa, marasa gaskiya kuwa za suyi ta kan su, Inno da Yaya duk abunda kuka gani kada ku firgita kuyi aiki da hankalin ku, komai a zahirin gaskiya yake tafiya kuma, mutuwa bata ɗauka sai lokaci yayi, haka zalika ko wane bawa da irin tasa ƙaddarar wasu suyi imani da ita ƙaddarar wasu kuwa suyi biyu babu, Nusaiba jeki kice da Umma kowa ya hallara a gidan nan! "




Ai kuwa da gudu Nusaiba ta tashi ta fita, kowa yana jiran dawowar ta, Inno ta kasa haƙuri ta ce, "kodai masu neman Auren kune? "


kawu ya ce, "ashe dai kun ƙaro fitsara eh lallai kam na fahimci komai ".




Goggo ta ce, "wato rashin kunya kuka dawo kuyi muna ku nuna muna baku shiryu ba kuma duniya bata hora kuba ko su kuwa wan can fitararrin daga ina kuka samosu ko suma abokan fitsarar taku ne? "




Sai a lokacin Mama tace, "sune ma dan wannan rawar kan nasu yayi yawa, ai kuwa abunda kika aikata zasuji babu wani rufin asiri".




Yaya tace, "ai dai masu goyon shegun suna da yawa, dan haka baki da bakin yiwa Narjeesah gori dan kema kin goya shegu, ga kuma wani cikin nan wanda bamu san uban saba, a gurin yarki, kin ga kuwa dama can mun sanar dake mai ɗa goye baya cewa ɗan wani shege bai sani ba ko ya haifa, ashe kuwa ya baki ya boka, kin haifa shegen ke nan".




Tsit kaji bakin Mama tayi ƙasa da kanta.


Dariya Amrah da Humaira da Hindu sukeyi harda tafawa.


Sallamar Umma ce ta katse masu tattaunawa suka maida idon su, akan Umma cike da mamaki suke kallon yanda Umma ta sauya ta zama wata Hajiyar da ita, sakin baki sukayi wasu ma murza ido sukeyi.




Inno ta ce, "Allahu akbar kabira, Umman yara kece kika dawo haka ikon Allah to lale maraba da zuwa, sannu da zuwa sannu da zuwa " cike da farin ciki suka rungume juna.




Ita kuwa Yaya hannun Umma ta riƙe tana kallon ta, tana godiya a gurin Allah subhanahu wata'ala.


Umma tayi murmushi tace tare muke da baƙi fa, dan Allah ku zazzauna hannun Inno da Yaya ta kama suka nufi gurin su Humaira suka zauna,




Nusaiba ce tare da Baban mu suna riƙe da hannun juna suka shigo Yaya Jafar Yaya Aliyu suna biye dashi.




Hailala da salati gurin ya ɗauka sai murza ido sukeyi ai kuwa da gudu Yaya Auwal ya matsa yana taɓa jikin Baba sai da ya tabbar shine ba mafalki bane yakeyi ai kuwa ya rungume shi, ai sai ga Hanan itama ta faɗa jikin sa, sai kuka yadawo sabo.




Kawu Bala ne ya ce, "wannan ai ba gaskiya bane waye ya taɓa mutuwa kuma ya dawo sai dai ko fatalwa ne eh lallai kuwa ni ban yarda da wannan lamarin ba! "




Goggo ta kasa tsayuwa ta zube a gurin bata numfashi haka Mama faɗuwa gurin tayi, su Yaya Halilu kuwa suman zaune sukayi hada su Anty Asma.






Hamdala Inno tayi tace, "ikon Allah tabbas wannan Malam Isah Musa, dan naji a jiki na, mai gidan mu ne ya dawo ran sa, Allah mun gode maka".




Yaya tace, "hakane Inno wannan uban "yayan mune Allah ya dawo muna shi, yara kun tashi daga marayu kun dawo masu uba, mu kuma mun dawo matan Aure Allah da ikon sa yake".




Tashi nayi natako nazo nace, "muje ka zauna Baban mu ka futa sai ka bamu labarin abunda ya faru a shekarun baya"




Hannu na ya riƙe muka je muka zauna muka saka shi a tsakiyar mu, duk kowa yayi shiru muna jiran muji daga garesa, harda maƙota masu kallon Ikon Allah, duk suna a gurin.




Wayar Yaya Jafar ce tayi ƙara, da sauri ya kalli Baban ya ce, "sun neman izinin shigowa"


Murmushi Baban yayi ya maida idon sa akan Yaya Mudarsir ya ce, "kaje ku shigo da baƙi".




Tashi yayi ya fita, sai gashi sun shigo tare zaro ido waje nayi, na buɗe baki zanyi masifa, da sauri Humaira tayi wa Inno da Yaya raɗa a kunne da sauri suka ce, "A hir ɗinki Narjeesah Allah kikayi wata magana a gurin zamu swaɓa maki ".




Zuɓurar baki nakeyi gaba, ina ɗaure fuska, Shuraim kuwa ƙafata, yazo ya haye Salman a kusa da Yaya Jafar ya zauna, Muhseen kuwa a kusa da inda muke zaune ya zauna ya ce, "Anty Narjeesh bakiyi maraba da zuwan mu ba ne? ".




Gir giza masa kai nayi nace, "kai nayi maraba da zuwan ka amman banda wan can mutumen ka duba yanda yake harara ta"




Ɗaga ido sukayi shida Amrah ai kuwa harar ta, suka kamasa yana yi dariya sukeyi ƙasa_ƙasa.




Gyaran murya Baban yayi yace, "To Alhamdulillah Allah shine mai tsara yanda yaso a duk lokacin da yaso, to gashi Allah yayi dawo wata a cikin iyalai na, kuma gashi nasami sauye_sauye da dama kuma abubuwa duk sun birkice, motar da muke ciki ce, tayi hatsari ba tare da mun san miye musabba bin ba, amman kuma ni a cikin jeji aka jefa ni, motar ta kama da wuta, kaina ya bugu da icce nikam ban sake sanin inda kaina yake ba, na dai falka ne na sami kaina a asibiti kuma na manta kaina da Sunana kawai dai na rasa Yaya zanyi na tuna inda na fito, koda aka sallame ni daga asibiti wannan yaron ne na gani a kaina, kuma shine ya ɗauke ni ya kaini gidan sa, naci gaba da jinya ta har nasami sauƙi amman kuma, hal zuwa lokacin bana iya tuna waye ni, ganin haka ne ya mai dani asibiti aka ce, idan naga abunda nafi ƙauna zan iya tunawa, gidan su muka dawo ya bani aiki wanda na nema duk da kuwa cewar gidan sa cike yake da ma'aikatan kaki da marasa kaki ya bani gadin get ɗin ƙuryar gidan sa, kasan cewar get huɗu a gidan nasa".




Kallon Salman sukeyi wanda idon sa yake a watar sa kamar baya gurin.


Baban ya ce, "sai shekaran jiya ne Allah ya kawo mani Narjeesah da Amrah, muka haɗa ido dasu ne, a lokacin ne, nafaɗi ƙasa, kaina na juya mani, a take na some a gurin, ina farkawa na fahimci cewar nawo cikin hayyaci na".




to kunji abunda ya faru.


Zufa su kawu suke gogewa, kallon Baban Inno tayi tace, "Alhamdulillah barka da dawowa Malam, sai kuma abunda ya faru bayan baka nan" a take Inno ta labarta masa komai.


Ai kuwa kallon kowa yakeyi a gurin yana gir giza kai, ya ce, "wato koda mutuwar ce, haka zakuyi wa iyali na, wula'kanci, Narjeesah! Narjeesah!! Narjeesah!!! Kuna nufin ita ƙaddara bata isa ta faɗa a kan ta bane ko miye kuke nufi? Ai ada na ɗauka, koda a ce da gaske cikin jikin Narjeesah da gan ganci ta same sa irin yanda kukafi kowa sanin ina son ta, to kuma zaku sota kuma zaku janyo ta a jikin ku, a hankali kuna nuna mata, laifin ta,






To yan dai bari kuji waye wannan Shuraim ɗin yaron Narjeesah wanda kuka tsana kuka kureta ida da 'yan uwan ta, harda mahaifiyar ta, suka rasa matsu gunni, kuka basu wasu 'yan kuɗi, wai gadon da suka samu ke nan, to kun ga wannan yaron Shuraim? "




Ya janyo hannun Shuraim ya zaunar dashi a jikin sa ya ce, masu "yaron nan ɗan halak ne kuma wannan yaron da kuke gani Narjeesah ta hanyar sunna suka sami cikin sa, kuma, shi jika ne, a gurin sarakai kafin nan Aliyu ku sanar dasu waye mahaifin Shuraim"






Gyara zaman Yaya Aliyu yayi yace, "Shuraim" labarin komai ya basu har sace sa zuwa yan zun, san nan ya sake kallon su, ya ce, "kun ga wannan"




Ya nuna Shuraim yace, "ga Salman nan shine uban Shuraim halak malak".




Dukan su mamaki sukeyi wai a ce Shuraim ɗan gata gaba da baya, sukayi muna wannan walaƙancin haka?.


Salman kuwa haushin su yakeji, Inno ce da YAya da su Yaya Auwal Hanan da wasu daga cikin yan uwa na kawai yaji baya jin haushin su, tashi kawai yayi ya bar gurin yayi waje kamar wani kubu buwa.




Da sauri su Yaya Aliyu da Jafar suka mara masa, baya.




Inno ce ta ce, "Malam Shamsiyya da Atika ciki biyu sunayin kuma suna haifewa, ita Shamsiyya wannan cikin na jikin ta shine na ukku, duk da anso zubar dashi amman abun ya faskara".




Cike da mamaki Baban ya ce, cikin fushi, wato........








*Comment And share*



*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹




💐💐 *NARJEESAH* 💐💐




*Rubutawa*
*NANA KHADEEJATU*
*_UMMU IHSAN_*


*ELEGANT ONLINE WRITERS*


_*Bismillahir Rahmanin Rahim*_


5⃣1⃣⏭5⃣5⃣

➿➿➿➿➿➿➿➿➿ "wato sune "ya'yanso ko? Basa laifi, ai ni a ganina duk yara na ɗaya suke a gurin ku kamar yanda nake ji a zuciya ta, Bala kai da ƙanwata da ke Larai kun cutar dani kun raba mani kan "ya"yana manya basa tausayin naƙasa dasu, ni kuma ba haka nabar ku ba, amman babu komai kunyi son ranku, duniya ce, gashi nan tun yanzun kun fara gani!".


Kawu Bala yace, "kayi hakuri ɗan uwana sharrin sheɗan ne hakan ba zata sake faruwa ba "




Goggo ta ce, "haba ɗan uwana ai wallahi mu bamu da niyar watsaye maka zaman lafiyar da ka ɗora iyalan ka, shi yasa ma bamu siyar da gidan ba".


Tsaki Muhseen Humaira da Hindu sukayi, ni kuma na ce, "andai ji kunya wallahi, a ce ya'yan ɗan uwan ka, kayi mugun tsana to taya ma zan yarda in saki jiki daku, kudai kawai a daiyi zumunci".




Baban murmushi yayi, ya ce, "ba kuda bakin kariyar kan ku amman ina mai jin takaicin abunda kuka aikata mani, domin ni kuka to zarta ba wani ba, ke kuma Larai kin girbi abunda kika shuka ko? Nafi kowa sanin irin yanda kike ƙin Narjeesah amman na ɗauka ko da bayan rai nane zaki iya renin duk nin abunda na bari a baya na, amman ba bu komai a ga su Shamsiyya nan sun bar maki darasi, Narjeesah ƙarama ce, akan su Shamsiyya amman

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads