Header Ads
Showing 9001 words to 12000 words out of 58708 words

Chapter 4 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

wani abun daban gwara ke kiyi hakuri kiyi wannan sana'ar".




Shiru Umma tayi tana, tunani zuwa can tace, "babu komai na yarda zanyi nasan duk abunda kika sani wanda zai sa naci gaba shi kike bani shawara akai baki taɓa bani mummunar shawara ba, dan haka na yarda ɗari bisa ɗari".




Mukam duk jikin mu yayi sanyi bare ma lokacin da muka gano wurin ranar da Umma ta fara yin abinci a gurin, gidan muka dawo muka saka kuka, kamar wanda akayi wa mutuwa, a ranar koda suka dawo gida sam basu gane kan mu ba.




Babu wanda yabi takan mu dan sun fahimci komai, Umma ce naji tana faɗar Alhamdulillah kasuwa tayi kyau , sai farin ciki sukeyi.




Da haka dai har muka saba itama Umma ta saba, cikin ikon Allah Umma da tayi abinci nan da nan ya ƙare, sai Mama Larai ta baiwa Umma shawarar itama ta kama gidan haya dan itama haya takeyi Umma bata kawo komai ba, takuwa yarda, a haka har Umma ta samar muna gidan haya, amman nesa da unguwar da Mama Luba take.




Umma kam, sai sam barka a da kuɗin abincin ta mukeci muke sha, kuma muke biyan haya hankali kwance.




Cikin ikon Allah har muka shekara biyu a garin shuraim na daɗe da yaye sa, shegen wayau ne dashi shekarun sa, biyu da wata shidda a yanzun amman idan ka ganshi zaka ɗauka ya shekara ukku a duniya sai uban surutu.




Umma ce mu kaga kwana biyu bata dafa abinci ba, shine muka kasa hakuri tunda munga lafiya lau take, amman da alama tanada damuwa gashi ni ban isa in san damuwar ta ba, zaune muke da Amrah da Nusaiba na ce, "Amrah miye yasaka ba zaki tun kari Umma ba kiji damuwar ta, tunda kin san nice babba amman bani da wannan ikon dan Allah kije ki tambayar muna ita ".




Tashi Amrah tayi ta sami Umma zaune ta doka uban tagumi shi kuwa shuraim yana zaune a ƙafar ta na wasa da motar da ta siya mashi, da remote a hannun sa.




Amrah tace, "Umma dan Allah mike damun kine? Kuma kwana biyu bakiyi abinci ba lafiya dai? ".




Ajiye zuciya Umma ta sauke tace, "Luba ta hana ni ɗan makulli tace, itama abincin ta dawo wa saboda ɗikin da takeyi babu kasuwa amman taga siyar da abinci akwai kasuwa harda riba, kuma tace kada mu sake zuwa inda take gashi na kashe kuɗi na, nayo cefane, yan zun ya ya zamuyi ne, gashi wannan lokacin ne zan nemi kuɗin hayar gidan nan! "




Zaro ido waje mukayi nida Nusaiba uwa uba Amrah da take zaune ta kafe Umma da ido.


Fitowa nayi inda muke ɓoye nida Nusaiba na ce, "Umma ni zan......








*Comment and share*




*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹




💐💐 *NARJEESAH* 💐💐






_*Rubutawa daga alkhalamin*_🖊
*NANA KHADEEJATU* *_UMMU IHSAN_* *SADAUKAR GA DUK KANNIN MASOYANA NA*




*ELEGANT ONLINE WRITERS*




*7&8*


➿➿➿➿➿➿➿➿➿ Umma ni zan iya fitar maki dashi a bakin titi ko ƙofar gida, tunda kema kina iya bakin ƙoƙarin ki na ganin kin ciyar damu da halak, dan haka ki bani wannan damar dan Allah Umma".




Shiru tayi duk muka zuba mata ido Amrah ta ce, "Umma ki yarda damu zamu iya wannan aikin dan Allah, mudai kawai ki bamu dama yan zun mu soma aiki kawai".




Nusaiba ta ce, "Umma ya kamata ki fahimci cewar baki da masoya na gaskiya idan ba muba, baki da wani ɗan uwan da zai so ganin ci gaban ki sai mu, kuma baki da wani abokin shawara wanda ya kai mu, mune kawai yafi chan chanta ki baiwa yarda da amana ɗari bisa ɗari".




Umma kuwa ta ce, "kuje ku ɗaura girkin ni zan iya fitar da abuna kawai ni dai fatana ku koma makaranta dan ku sami ilimi domin ilimi shine farkon abunda ya kamata na koyar daku nema ba kuɗi ba".




Sanin halin Umma magana ɗaya takeyi ne yasaka muka fita muka fara haramar ɗaura girkin kowa da abunda ya keyi, nike wanke kayan miya, Amrah ta ɗaura dafuwar shinkafa, Nusaiba ke dafuwar wake da taliya, ina gama wanke kayan miyan Nusaiba taja hannun Shuraim suka nufi gurin markaɗen kayan miyan ni kuma naci gaba da aikin da takeyi, koda ta dawo na komawa aiki na itama taci gaba da yin nata, kudi Umma ta fito dasu tace, "waye zai je sayen nama dan na kira mai naman nace ya ajiye muna na dubu ukku, sai aje a anso daga nan asiyo kayan lambu a yanka shi daga can ayi sauri a dawo".




Kallon Umma mukeyi, Amrah ta ce, "Umma nikam yau duk a har gitse nake ba zan iya fita ƙofar gida haka ba, sai dai ko Nusaiba "




Nusaiba ta ce,"Umma kin san bana shiri da mai naman nan saboda ce mani yake nice matar sa, har mutane yake nunawa cewar Umma ta bashi ni, kuɗin Aure na kawai zai kai dan haka ni kam ba zan iya zuwa ba".




Dariya muka saka wa Nusaiba muna zolayar ta, "aa Nusaiba kice zamuci nama sosai a gidan ki, tunda kin zama matar mai nama"




Ture baki tayi, na tashi ina dariya na wanko hannu na, na ashi kuɗin na ɗauko mayafi na, zan fita, shuraim yafasa uban ihu da sauri kowa yake kallon sa ana faɗar lafiya? Umma ta ce, "wannan yaron anyi ja irin yaro, nan mu da kake gani halan ba mutane bane ko cin yeka zamuyi ne? Da sha shancin banza".




Sai a lokacin ne muka fahimci son yakeyi ya biyo ni.


Dariya su Amrah keyi, Nusaiba ta ce, "jirgin yawo abun nema ya samu, to tashi ku tafi kasan halin Anty zata iya tafiyar ta, tunda kana yi mata kukan banza".




Dariya ya saki da gudu ya ƙaraso inda nake wai kuma sai na ɗauke sa, dariya nayi na ce, "ashe dai baka shirya tafiya ba, yaro nikam da kake gani na a nan ba zan iya ɗaukar ka ba, yaro sai dai kayi zaman ka"






Tunda yaga na juya zan tafiya ta, da sauri yazo ya kama hannu na ya riƙe muka fita yana yi masu bye_bye, aikuwa duk inda muka wuce, sai an bimu da ido, har na fara tsar guwa, a kusuwar kuwa Mai naman ne yaƙi shanye raɗa yake tambaya ta, ina matar sa, ni kuwa na share sa saboda ni kwata_kwata yanzun maza na ajiye su guri ɗaya azzalumai ne kawai.


Ya yi ta magana yaji shiru, da yake mun saba zuwa nida Amrah da Nusaiba wata rana nida Amrah kawai wani lokacin kuma ni ɗaya shi yasa yasan hali na, dan haka bai damu ba, da share san da nake yi.


Yana bani naman hannun shuraim naja muka nufi gurin mai sai da cucumber carrots cabbage na soya harda green beans da dai sauran su, ya wake ya yanko mani, ya zubo mani a Leda mai zane, ya zubawa shuraim lemo da ayaba da abarba yanka ɗaya_ɗaya godiya nayi masa muka fito ka suwar muka dawo gida abinci dai aka gama komai, Umma ta fita dashi cikin ikon Allah har ana nema.




Tun daga wannan ranar ne Umma a gidan ta abincin yake ƙarewa.


Mama Luba ce, tazo gidan mu cike da masifa wai Umma ta muna fuce ta, duk ta janye mata customer, wallahi tayi alkawarin sai Umma ta zubar da hawayen ta indai har tana cikin garin nan kuma tana siyar da abinci ".




Kallon ta mukayi bamu ce dasu uffan ba dan ko Umma murmushi tayi bata ce da ita komai ba,har ta ƙarasa zazzaga masifar ta, zata fita Umma ta ce, "Luba saboda ke nazo garin nan kuma ke ce kika bani shawarar yin wannan abincin, banso yiba sai da kika roƙeni, kece kika bani gurin fara wannan aikin daga baya kuma kika zo kika hanani kika ce na baki shagon ki, na baki abun ki, shine kika zo yan zun har gidan mu kike futa mani irin wannan muya gun kalaman, to naji Luba ki bani nan da kwana biyu, kizo unguwar nan kuma ki bin cika a garin nan idan har kin tsinci takalmin da na bari a garin nan kije kiyi abunda kika ga dama dashi! ".




Fuuuuu taja iska ta fita kallon Umma mukeyi cikin mugun tashin hankali, nace, Ummmma... Kina... Nufin. Zamu.. Zamu bar.. Garin.... Garin nan ne to muje ina!?.




Amrah ta ce, "Umma kina nufin cewar tsoron ta zamuji ne, to muje ina wai, ko zamu koma garin mune inda ake farau tar rayuwar mu!? "




Kallon mu Umma tayi ta ce, "tabbas mutun abun tsoro ne, kuma zuciya mugun nama ce, hassada mummunar abuce, kada ku yau dari zuciyar ku, saboda idan kun lura da yanda take wannan maganar sam bataji bata gani huɗubar shaiɗan ce kawai keyi mata yawo a jinin jikin ta".




Nusaiba ta ce, "to Umma ina zamu a yanzun zun nan shike nan mu kullum cikin gudun hijira muke? ".




dariya Umma wadda tafi kuka ciwo tace, "Yaro yarone tabbas duk ku yara ne, kuje ku fara shiri zan zo da dillalai su saye kayan mu saboda tafiyar nan bata yuyuwa da kayan nan namu".






Hannun shuraim taja suka fita mukam duk jikin mu a sanyaye yake, yanda Umma ta ce, muyi hakan mukayi, koda dillalai suka zo suka siya kayan har tukunyar da muke abinci dasu da katifu, suka bita kuɗin suka kwashe kayan ya ge daga mu sai suturar mu da wasu tarkace ba masu yawa ba, gurin wanda take ansar kayan abincin taje ta biya su, cike da alhini suka rabu, ta biya kuɗin da ake biyar nu na haya, ta dawo da sauran kuɗin.




Da dare sai dai muka shimfiɗa tabarma mukayi shimfiɗa muka, kwanta duk muka kasa yin bacci sai juye_juye mukeyi, har Asubahi, muka tashi mukayi sallah, mu ka fito neman abinci, tea muka dafa muka sha muka wanke kayan muka kwashe komai muka ɗaure a buhu, muka fito da komai a tsakiyar gida duk kowa ka duba zaka fahimci yana cikin damuwa in banda shuraim dake ta haukar sa ko ince shirmen sa, daɗi Kawai yake ji yau zai hau mota.




Sallama mukayi da maƙota muka baiwa mai gidan makullin sa, muka hau mota sai tasha, garuruwa ake faɗa mudai Umma muke bi rasa motar da zamu shiga mukayi, wani mutum ne yazo ya ishe mu da surutu, "Hajiya wallahi motar Yola bata da wata matsala dan daga ganin ku, ku mutanen Yola ne, Allah Hajiya wallahi maganar gaskiya wannan drivar ya iya tuƙi yasan takan aikin sa, dafe goshi Umma tayi ta ce, "muje malam haba! ".





Dariya mukayi duk da irin halin da muke ciki, ai kuwa da gudun sa yake ɗauke buhu huwan har da akwatin mu, mu kam sai bin sa mukeyi da ido, sai da ya kwashe komai muka bisa a baya muka shiga cikin motar, kamar mune kawai ake jira, muna shiga motar na tashi, shuraim kuwa a ƙafar Nusaiba yake zaune sai surutu sukeyi, ni kuma tunda muka shiga cikin motar nan nake jin gaba na na dukan ukku_ukku, addu'a kawai nakeyi duk na zama wata irin ta daban, Amrah ce ta dubeni ta dafa ni na ɗago ido na kalle ta.




Ta ce, "Anty lafiya dai duk naga kin sauya mani kala ba kamar yanda muka fito daga gida ba yan zun kin fi shiga cikin damuwa".




kallon ta nayi na gir_giza mata kai alamar babu komai na rufe ido na.


Tafiya mukeyi ina ƙara shiga cikin damuwa, sai na kauda kaina gefe na fashe da kuka, wanda ni kaina ban san dalilin yin sa ba, kawai naji muryar Amrah ta ce, "Anty na sani kuka kikeyi ni ba zaki iya ɓoye mani komai ba, amman kuma na fahimta sosai kukan zuwar maki yayi, dan Allah ki daure ki daina kukan nan haka, kafin Umma ta san halin da kike ciki ko Shuraim".




Ɗaga mata kai nayi ba tare da na juyo ba, tafiya kawai muke yi, har muka isa garin yola koda muka sauka a tasha bamu san inda zamu ba, wata motar kawai muka shiga aka sauke mu a cikin garin.




Goya Shuraim nayi saboda ya gaji kuma yunwa yakeji guri muka samu ajikin wata bushiyar mangwaro muka zauna a kusa da wata hanyar manya_manyan gidaje, shimfiɗa mukayi, mukayi sallar ƙasaru, daga nan muka buɗe abinci muka fara ci amman ni sam hankali na yana gurin wata hanyar da wata motar ta fito a can gaban mu, ba wannan hanyar da muke kusa da ita ba.




Tashi nayi na ce, "Umma" zan je wan can gurin na gani.




Amrah ce ta ce, "muje na taka maki, nima nagano abunda kika tsare da ido tun ɗazun".


Murmushi nayi, nace, "Amrah "kedai kice gudu kikeyi na ɓata kije nema na baki san inda zaki same ni ba.




Dariya mukayi zamu tafi Shuraim ya taso ya riƙe mani hannu nace wallahi rigimar ka yawa ne da ita, nida zani gurin can ba wani nesa ba.




Dariya Amrah tayi, ta riƙe hannun sa ɗaya muka tafi, hanyar nake bi da ido duk da marece ne, wata bushiyar lemon tsami na kafe da ido a take gaba na ya faɗi, da sauri hawaye suka soma zubo mani, babu tsayawa, cikin tsananin tashin hankali Amrah take gir_gizani tana tambayar miye na gani, kuka na fashe dashi matsanan cin kuka na fashe dashi, na durkusa, ƙasa ina kuka, tambayar duniyar nan Amrah tayi mani amman na kasa bata amsa shima Shuraim ganin kukan da nakeyi ne ya saka shi fashewa da kukan ya rungume ni ta baya.






Da sauri Amrah taje ta kira Umma da Nusaiba suka kwaso kayan mu suka sameni a yan da Amrah ta barni.


Nusaiba ma cikin kukan take tambayar mike faruwa amman duk na kasa basu amsa Umma kuwa juya muna baya tayi, har sai da su Amrah sukace idan ba zan dai na kukan ba, suma ba zasu daina ba, dan dole tasa na goge hawayen duk da basa barin zubar, na ce, "Amrah kuzo muje ba zamu kwana a nan gurin ba, duk da ban taɓa tsammani haka ba ko mafalkin hakan ba, kuma ina roƙon ku da ku zuba mani ido kawai".




Sukam duk basu fahimci inda maganar tawa ta dosa ba, goya Shuraim nayi ina takawa a hankali kamar wadda ƙwai ya fashe wa a ciki tafe muke ta gefen hanyar muna ta wuce manyan gida jen dake unguwar, bayan wani ƙaton gidan wanda irin su basu wuce biyar ba, amman kam unguwar akwai gida je masu kyau kuma unguwar ta tsaru, ta jikin wata "yar ƙaramar hanya mukabi ta bayan wannan gidan, muka iso gaban gidan.




Nusaiba ta ce, "kai Anty Narjeesah uban waye zai iya bamu gurin aiki idan ya kalli shigar mu da kayan mu, kuma wannan gidan ai sai masu yanka kan yara dan Allah mu rufawa kanmu asiri! ".




Kyaleta nayi, na matsa a jikin get ɗin na durkusa, ƙasa na tona wani rami wanda yake da dutse a gurin na janye dutse, wani ɗan akwatin ƙarfe na ɗauko wanda yake rufe a cikin wata 'yar jaka, na buɗe makullai ne a cikin gurin sai da na duba da kyau na ɗauki ɗaya, naje na ɗorawa Amrah akwatin wadda ta saki baki da hanci tana kallona ko ƙyaftawa babu, a hannun ta, na juya naje na saka ma kullin na buɗe ƙofar sai da na rufe ido na, a lokacin da gidan ya buɗe, tsaye nayi a gurin duk jikina a sanyaye yake, Nusaiba ce ta dafa ni na jiyo na buɗe ido na na kalleta zata magana nace, "Nusaiba" bana son tambaya a halin yan zun dan haka ki ɗauko kayan mu mu shiga daga ciki.




Sanin halina da yanda nayi mata magana ne ya sakata aikata abunda na faɗa, da tsoro_tsoro suka shiga cikin gidan harda Umma ni kuwa sai da na daɗe a gurin da addu'a na ɗaga ƙafata na shiga cikin gidan tare da zubar da hawaye, rufe ƙofar nayi da makulai na ƙara gyara get ɗin gidan, motoci ne guda biyu a harabar gidan duk a lullube suke, abun duk yayi datti bana wasa ba, shuke_shuke ma wasu duk sun bushe wasu sun fito ciyayi duk ko ina in banda cikin barandar gidan.




Wuce su Umma nayi, na dake zuciya ta, naje na buɗe ƙofar da ɗaya makulin na tura ƙofar na jiyo nace "Bismillah Amrah".




Nice na fara shiga ina shiga na kunna wutar gidan a take gidan ya ɗauki haske ta ko ina gashi gidan babba ne kuma a cikin babban falon gidan duk kujeru ne ta ko ina ga kayan more rayuwa.




Kowa ni yake kallo tare da neman ƙarin bayani, ni kuwa na share na ce, kuzo mu gyara gurin da zamu zauna kafin zuwa safiya kowa ya kama nasa ɗakin duk da nasan Nusaiba da Amrah ɗaki ɗaya zaku ɗauka Umma ɗaki ɗaya, ni kuma ɗaki ɗaya nida Shuraim.




Amrah ta ce, "ok Anty Narjeesah Allah ya taimake mu baki ɗaya ".


Kowa ya ce, "amin"


Makuli ɗaya nasake amsa gurin Amrah naje na buɗe wata ƙofar wanda gurin yake kichin ne da gurin ajiye kayan share_share da goge_goge, ɗaukowa nayi nazo na basu muka fara gyara ko ina, A cikin falon sai da muka gyara Umma da Shuraim suka zauna, a kujera, lokacin sallah ne yayi nazo muka fita gurin fanfo mukayo alwala mukayi sallah nadade ina addu'a har sai da nayi sallar isha'i natashi gurin abinci muka ci kowa da abunda ya ke saƙawa, bayan mun gam.




Amrah ta ce, "dan Allah Anty Narjeesah yaushe ne kika taɓa zuwa garin nan kuma har kika san wannan gidan dan duk abunda kika aikata a tun daga ɗauko makullin gidan nan da buɗe sa da shigowar ki da da yanda kike komai hankali kwance da sanin ma'ajin komai haƙiƙa babu ko shakka kin san abunda mu bamu sani ba"




Nusaiba ta ce, "tabbas Anty Narjeesah akwai abunda kike ɓoyewa wanda mu bamu sani ba dan Allah ki sanar damu dan muna cikin duhu, ki fitar damu haske ".




Amrah ta ce,

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads