Showing 6001 words to 9000 words out of 58708 words
Chapter 3 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt
*Comment And share*
*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
💐💐 *NARJEESAH* 💐💐
_*RUBUTAWA *_ 🖊
*NANA KHADEEJATU*
*_UMMU IHSAN CE_*
*YA ALLAH KAJIKAN IYAYE NA KAYI MASU RAHMA KA KYAUTATA MAKWANCIN SU KA SANYA SU DAGA CIKIN DAUSAYIN ALJANNA SU DA DUK KANNIN MUSULMI BAKI ƊAYA AMIN YA ALLAH*
*_BISMILLAHIR RAHMANIN RAHIM_*
*5&6*
➿➿➿➿➿➿➿➿➿➿
Umma ta ce, "kada ku yarda naji wata magana ta fito daga cikin bakin ku har sai idan naso hakan, wannan umarni na ne! " kawai ta shige cikin ɗakin ta, ta saki labule.
Tunda mukaji umarnin Umma sai duk jikin mu yayi sanyi babu wanda ya sake cewa komai tashi nayi nima kashige cikin ɗakin mu na kwata, ina nazari, tabbas duk abunda ya saka Umma kuka baƙara min abu bane, amman kuma Umma ta hana nasan ko miye wannan abun, kai koma miye babu shakka duk abunda ya faru nice sanadiyar komai ya Allah kadube mu.
Duk yinin ranar bamu da wata walwala kowa a cikin damuwa yake har aka kwana biyu, yau muna zaune muna fira ni dasu Amrah Nusaiba na goye da yaron yana bacci, sallamar su Inno ce ta katse mu, cikin farin ciki muka tarbe su Inno da Yaya da Mariya, Umma ce ta fito cikin ɗakin ta, tazo ta, tarye su da farin ciki, tabarma aka shimfiɗa masu suka zauna na kawo masu ruwa Amrah taje maƙota ta siyo masu zuɓo ta kawo masu, bayan sun sha aka gai da tambayar ya akaji da hidimar biki suka ce Alhamdulillah angama lafiya taro ya tashi sai dai abunda ya faru ne wanda basu ji daɗin saba.
Umma tace, "ai komai ya wuce".
Da sauri nace, Inno dan Allah miye ya faru a ranar dan Umma ta hana kowa ya sanar dani, sun barni cikin duhu da tunanin miye yake faruwa, bana bacci ina cikin damuwa, duk da nasan da cewar ba kowa bane ya janyo wannan matsalar ba sai ni.
Inno ta ce, "ai koni ma ba zan iya sanar dake komai ba, da kuma wanda sukayi abun kasan cewar nafi kowa sanin halin ki Narjeesah idan kika san ko su waye da abunda akayi ba zaki ɗauka ba, kasan cewar ki mafaɗa ciya, daman cikin da kike dashi ne yasaka ki yin sanyi amman yanzun nasan zaki iya fafatawa da kowa".
Yaya ta ce, "tabbas hakane Narjeesah zaki san wani abun amman banda wani abun, ranar a unguwar mu anyi faɗa sosai har makarantar islamiyar ku inda akace malan Abbakar shine ya yi maki ciki kasan cewar sa yana sonki tun kina ƙaramar ki, kuma Baban ku ya sani amman yace, sai in kinyi hankali kin ce kina son sa, to ganin irin yanda idan baki zo makaranta ba yake zuwa ya sakaki a gaba kije makarantar shine aka ce shine ya yi maki cikin yaron nan, shi kuma ya ƙaryara rigima har aka koresa a makarantar duk da kuwa kasan cewar mahaifin sa shike da makarantar".
Hawaye naji suna zubo mani nace wallahi Inno bashi ne yayi wannan cikin ba kuma wallahi ko kalmar kebewa a wani gurin, ko a makarantar bai taɓa furta mani ba.
Inno tace, "ana cikin wannan rigimar ne, wani mai mota yazo daga ganin sa anga dan shaye_shaye to shine ya ɗauki hankalin kowa inda ya ce, shine wanda ya yi maki cikin yaron nan kuma yazo ya anshi abun sa ne, saboda duk lokacin da ku ka tafi makarantar boko shike zuwa yana ɗaukar ki yana zuwa gidan sa dake har sai da kika ɗauki cikin sa, kuna tare shine ma yace ki zauna ki raini cikin zai Aure ki, to yan zun ya fasa Auren ki yaron kawai yake so ko kiba shi yaron da arziƙi ko kuma yazo da "yan sara suka sai dai su kashe ki da duk wanda yake tare dake su ɗauki yaron! ".
Da sauri na tashi tsaye na fara ja da baya ina zubar da hawaye nace wallahi Inno da Yaya, wannan ba shine uban yaron nan ba, wallahi ba zan bada shi ba! .
Inno da Yaya suma suka tashi tsaye suka haɗa baki gurin fad'ar, "to waye uban yaron nan tunda kin ce wannan bashi bane!? Kuma kina nufin kin san inda uban yaron yake ke nan! ".
Nace wallahi wannan ƙarya yake yi maku bani da wata alaƙa dashi, mutum nan ɓarawon yara ne kada ku yarda dashi.
To wane ne uban yaron nan tunda kin san shi kuma a ina yake kuma ya ya sunan sa? "Inno ce" ta jero mani wannan tambayoyin da suka riki tar dani a take na dabur buce na rasa ma wace irin amsa ce zani bata, gashi duk ankafe ni da ido.
Sai da na haɗiye yawu masu ɗaci ga uwar zufar da take , zubo mani ta kowane saƙo na jiki na nace, a gaskiya duk bani da amsar da zan baku daga cikin wannan tambayoyin amman gaskiyar zance "wannan mutanen ban taɓa sanin sa ba! "
Inno tace, to ya zama wajibi tsakanin yau ko gobe ki sanar damu Baban yaron nan, ko kuma kubar garin nan, sati ɗaya mutumen ya bada zai dawo kuma dawowar sa ba abu bane mai sauƙi dan da alama zai iya aikata duk abunda ya faɗa saboda a tare yazo da maso shaye_shaye harda takubban su"
Daɓas na zauna a ƙasa na fashe da kuka kamar raina zai fita, suma su Amrah kukan ne sukeyi sosai, Umma dai bata ce uffan ba, har su Inno suka dawo a kusa dani suna lallashin mu, kallon Inno nayi nace, "Inno dan Allah ku anshi adireshin sa da number sa ku ajiye mani ita har na tsayin wani lokacin".
Insha Allah suka faɗa, Inno ce ta kawar da wannan kukan ta ce, yo ni wannan iyayen na daban kuke kuna nufin ba zaku bani maigidan ba na ɗauke sa, ba har sai na roƙa ko? ".
Dariya mukayi, nidai shiru nayi Nusaiba ta sauke shi ta bata shi tace, "gashi nan Inno bama rowar ɗan baiwa".
Dariya sukayi Yaya tace, "ni kuwa wane suna ne kuka sakawa angon namu dan naji har yanzun baku faɗa ba, kodai sunan bai da daɗi ne ace yaro wata biyar bamu san sunan shi ba? "
Dariya mukayi, "Nusaiba tace suna kam mai daɗin gaske sunan hafizai".
Inno tace, "um kaji iyayen "ya"ya da kauɗin tsiya, wane suna ne wannan? ".
Amrah tace, "Shuraim ke nan Inno yaro hafizi ga daɗin murya".
suka haɗa baki gurin fad'ar, "kai masha Allah, Allah ya raya muna Shuraim yaro mai suffar larabawa da sunan larabawa abu ya yi kyau".
Mariya ce ta anshe sa, tana kallon sa, tace, "kai Inno wallahi wannan bai kama da wannan ƙaton mutumen mai ƙaton hanci kuma gashi baƙin sa ya yi yawa kawai dai ɓarawon yara ne, a gaskiya a gudu da yaron nan daga garin nan ma baki ɗaya, saboda naji ana raɗe_raɗin cewar cikin dare za'a nuna masu gidan nan ni wallahi yaron nan tausayin sa, nakeji! "
Kallon_kallo muka shiga yi nida su Amrah cikin damuwa Amrah tace, "Insha Allah babu maiyi sai Allah, burin wasu ba zai cika ba"
Sai marece su Inno suka tafi, Umma ce taja Nusaiba suka fita, Amrah ta sameni a cikin ɗaki kwance ina tunani ta dafani, na ɗaga ido na kalleta na tashi zaune tace, "Anty nifa a tsorace nake da maganar da naji su Mariya na faɗa nifa ina ganin zan baiwa Umma shawara, ne yau mu nemi gidan da zamu je mu ɓuya a can".
Kallon ta nayi, nace "Amrah "duk nice na janyo maku shiga cikin wannan hatsarin nifa ina ganin zan ɗauke yaron nan nabar garin nan gudun kada azo kashe ni a haɗa daku duka na bani, nayi sanadiyar mutuwar mahaifiyar mu daku kan ku, kuma aje a maida yaron nan wani irin mugun mutum".
Rufe mani baki Amrah tayi ta ce, "Anty dan Allah hankalin ki ya dawo jikin ki, ai duk inda kika saka ƙafar ki muna sai mun saka dan haka zamu gudu tare mu tsira tare".
Koda Umma ta dawo, ita da Amrah har mun gama abincin dare mu gyara ko ina, sannu da zuwa mukayi masu.
Da dare bayan munci abinci muka rufe gidan tare dayin Addu'oi sosai muka ɗauro alwalar kwanciya muka rufe ɗakin mu nida Amrah, Umma da Nusaiba suka kwanta ɗakin Inno suka rufe, addu'a sosai mukayi, kafin mu kwanta na shafe Shuraim da addu'a wanda shi tuni yayi bacci.
Can cikin dare muka fara jiyo, motsin ana shirin cire muna ƙofa ta shigowa cikin gidan, ai kuwa duk muka tashi zaune a tsorace addu'a muka somayi, ai kuwa dukan ƙofar akeyi da ƙarfin gaske kuma da makamai ake dukan ƙofar da sau muka diro ƙasa, nasa hannu, na ɗauke Shuraim na goye shi nasa wani zane na taresa dashi, sai muka lallaba, a hankali muka buɗe ƙofar ɗakin mu muka fito anan ita Umma suka fito sai jikin mu ke rawa, addu'a duk wadda tazo bakin mu ita muke yi.
Gashi har ƙofar ta fara alamar da kuwa, ta maƙotan mune aka saƙo tsani, da sauri muka ja da baya dan mun riga da mun san tamu tazo ƙarshe, hannun Amrah naja da niyar mu koma cikin ɗaki mu rufe amman kuma idan mun gudu su Umma fa, duk mun ruɗe dawowa gurin Umma mukayi nace, Umma dan Allah ki yarda mu koma cikin ɗaki ɗaya, mu ruf... Ban kai ga ƙarasa wabane, wasu maza guda biyu ne suka diro ta inda aka saƙo tsanin.
Zaro ido mukayi waje da sauri suka nufo mu mukam mun sadaƙar, har gaban mu suka tsaya cikin rawar jiki suna yi suna kallon ƙofar mutumen ya ce, "kuzo dan Allah mu taimakeku, kafin su shigo ciki dan sunada hatsarin gaske, akwai wanda zasu tarye ku a waje! "
Da gudu muka nufi gurin dan Amrah ta gane mutumen, naji tace, " to Baban Ahmad"
Abu ga tso wai mune da hawan tsani wanda ko amafalki ban taɓa tsammani haka ba, Umma aka fara ɗorawa kamar walkiya ta haye saman katangar gidan wasu suka taryeta sai, su Amrah suka turani, ni kuwa ina cewa ku fara fita, mutane suka ga zamu saka har a samemu kawai wannan ɗaya mutumen ya ɗagani sama ya taka matattakar tsani nin ya fitar dani, aka anshe ni sai Nusaiba sai Amrah sai mutanen suka ɗauke tsanin suka diro mukuwa tsuru_tsuru a cikin gidan kawai suka bud'e muna wata ƙofar muka faɗa wani gidan inda matan gidan suka maza suka tura mu wani ɗakin suka rufe, Shuraim ne na sauke da sauri gashi ta ko ina jikina rawa yakeyi.
Fitila aka kunna, Allah sarki bawan Allah idon sa biyu yana kallo na, zama nayi a gefen matar dake cikin ɗakin na bashi mama, ya fara sha, matar tace, "Allah ya ƙara tsare gaba ".
Mukace amin, anan muka zauna sai da asubahi aka buɗe kofar ɗakin muka fito, mukayi alwala mukayi sallah tare da godiyar Allah da ya tseratar damu dan wannan ikon Allah ne.
Sai garin Allah ya waye sannan muka fito gidan muta yi masu godiya wadda bamu san irin ta ba, a ƙofar gidan muka riski su Baban Ahmad mukayi masu godiya, suka ce babu komai ai yiwa kaine, wallahi wannan mutanen miyagune, suka bamu shawarar ya kamata mubar gidan.
Tun a ƙofar gidan ne zaka fahinci cewar da sun same mu a gidan nan da sunga bayan mu dan ƙofar sai an sauya wata.
Cikin gidan duk sun har gitse muna kaya amman basu ɗauki komai dan babu abun ɗauka a gidan.
Umma kam fita kawai itada Nusaiba kamar jiya, mu kuma muka gyara gidan da ɓarnar da akayi muna, muka ɗora abun karyawa koda muka gama Umma bata dawo ba zama mukayi muna ta jimamin abunda ya faru a daren jiya.
Umma ce ta shigo tare da wasu mata suka shiga cikin ɗakin ta suka fito, suka dawo cikin d'akin mu suka fita Umma ce ta dawo da kuɗi a hannun ta masu yawa, kallon ta mukeyi nida Amrah, sanin cewar idan nayi magana Umma ba zata bani amsa bane ya saka na ƙyafaci Amrah, da sauri Amrah tace, "Umma kuɗin miye haka? ".
Bata kuɗin Umma tayi Amrah amsa, Umma ta ce, "na sayar kayan ɗakin mune harda katifu kuma kwanonin sai a zuba su a buhuwa, yau nake son mubar garin nan saboda hankali na bai kwanta da wannan mutanen ba dan nasan zasu iya sake dawowa, yauma Allah ne ya kawo muna ɗauk, kuma kunji mutane sun bamu shawarar mubar gidan nan da wuri, gudun samun matsala, gashi ana ta sanar damu cewar yau kada mu kwana a gidan nan, shine ni kuma na ce abunda zamuyi kawai shine yau bar garin nan".
Ajiyar zuciya muka sauke a take muka hau shiri, Amrah na goye da Shuraim har muka gama komai muka rufe gidan muka baiwa maƙota makullin saboda wanda zasu ɗauke kayan su idan suka kwashe idan ansamu wanda zasu zauna sai basu su ƙarasa wata bakwai wanda ba muyi ba.
Ƙarfe biyar na marece muka isa tasha, mudai Umma muke bi duk inda ta dosa, motar kaduna muka hau ta biya kuɗin sai da Umma tayo muna siyayya muka ɗauki hanya, kasan cewar duk bamu san gurin waye zamu je b, amman bana jin zafin wannan tafiyar, har su Amrah fuskar su a sake take, Shuraim ya hannu na, yana bacci saboda su Amrah a matse suke, shi yasa na anshe sa.
A gaskiya tafiyar dare babu daɗi ko kaɗan, zafi ne ya dami Shuraim ya saka muna kuka na rasa ya zanyi masa, Amrah ta amsa Umma ta ansa Nusaiba ta ansa adawo mani dashi, ni kuma na rasa miye zanyi masa ma wanda zai daina wannan rigimar.
Wani bawan Allah ne da yake a jikin glass ɗin motar yace, "baiwar Allah kodai zafi ne ke damun sa,na buɗe maku glass ɗin kaɗan gudun kada mura ta kama shi? ".
Godiya nayi masa ai kuwa yana buɗe windon tuni ya koma baccin sa, ajiyar zuciya muka sauke, sai da naji iskan yayi yawa nace ya rufe muna mun gode.
Biredi da lemo muka sha da tsire,tafiya mukeyi tun daga jigawa dutse zuwa kaduna, jigawa dutse ma a Kauyen gumil dake cikin garin jigawa.
A tasha muka sauka muka da misalin ƙarfe shidda da rabi na safiya.
Wata unguwar mukaji ana faɗa unguwar kawo, a can muka sauka, Umma ta tsayar damu taje tayo tambaya aka yo mata kwatance, tayi godiya tazo tace, muje, cikin ikon Allah, bamu wani sha wahala ba, muka isa gidan da Umma ke nema, da sallama muka shiga gidan matar ta amsa ta fito, tana ganin Umma ta washe baki tana faɗar lale_lale maraba da zuwan ku haba, Aysha yau kam kin wanke tarin laifin ki a gurina, maraba ku ƙaraso daga ciki mana".
Cikin falon ta muka sauka kayan mu muka baro su a tsakar gidan, Allah yasa da nefa duk sai muka baje a saman ledar tsakar ɗakin muna futuwa, a take taje ta kawo muna abinci da nasha, nida su Amrah ne mukaci muka ƙoshi, ba mayi wani baƙunta ba, Umma ma haka, dan ma ina zaune a gurin bata wani saki jikin ta ba Shuraim ne ya motsa ya fara kuka, Nusaiba ta sauke shi ta bani, matar ta kafe ni da ido musamman ma da taga na fara shayar da yaron riƙe baki tayi ta kafeni da ido.
Ganin hakan ne ya saka Umma tambayar ta buta zatayi alwala, da sauri matar ta, tashi ta kawai wa Umma ruwan wanka tace, ta fara yo wanka tukun na.
Murmushi Umma tayi taje gurin wankan matar ta ce, "Narjeesah wai ku kuwa har yanzun baku daina yin Aure da wuri haka ba? Kuma fa naga mahaifin ku baya da wannan ɗabi'ar kodan anga baya raye ne shine akayi maki Auren wuri? ".
Kallon_kallo muka shiga yi mu ukku, Amrah ce, "eh ke dai bari kin gafa da ƙurciyar ta anyi mata Auren wuri shine fa mijin yaje ya shawo iskan sa, yazo ciki wata biyar ya sake ta a gaban mu harda su Inno kuma saki ukku, shine ta reni cikin gidan mu, wai yan zun da yaga yaron ya fara wayau wai shi sam bai san lokacin da yayi sakin ba, ina mai baki labari zarya kullum da safe da rana da dare, shine wai kowa sai ta koma ko kuma tabashi ɗan sa".
Wani uban ashariya matar ta saki, tace, halan ce masu akayi bata da gata ne, kodan sunga Aysha tana share tane, ai Aysha dama ita kunya ne da ita da kawaici ai kuwa tunda kuka baro masu garin nan ba zaku koma ba wallahi bari uwar taku tazo, to wai ma ke da nasani uwar masifa da surutu ya ya akayi kika dawo haka? ".
Dukan mu ta bamu dariya, sai da muka dara nace, "Mama ni wallahi sai yanzun ne na gane ki ashe wai gidan ki muka sauka".
Dariya tayi tace, "ja'irar yarinya, idan mai gidan nawa ya ƙoshi bani shi".
Shuraim ɗin na bata, Umma kuwa tun lokacin da Amrah take, sheƙa ƙarya ta fito riƙe baki tayi tana mamakin a ina Amrah ta iyo ƙarya haka, shigowa cikin ɗakin tayi, nima naje nayo wankan su Amrah ma duk sunyi wankan muka ranka sallolin da bamuyi ba, mamar ce tayiwa shuraim ɗin wanka, mukam bacci muka ranka har shuraim ɗin, Umma kam babin firar yaushe rabo suka dasa.
A gaskiya zaman gidan Mama Luba akwai farin ciki dan ɗaki biyu ta bamu Umma ɗaya mu ɗaya, satin mu biyu a gidan ta baiwa Umma shawarar mufara kasuwan ci, to wace sa'na arce zamu fara?.
Tace da Umma "ko abinci ne ki fara sai dawa inada shago a kusa da shagon da nake ɗinki, mai sai da abincin tayi Abuja ne dan haka ke zaki iya, dan Allah Aysha kada kice ba zaki iya ba, saboda yaran ki matane, da suje su siyar da abinci ko