Header Ads
Showing 42001 words to 45000 words out of 58708 words

Chapter 15 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

cikin hatsari, kuma kun san irin matsanan ciyar damuwar da nake ciki,? A gaskiya kun ɓata mani rai ku tashi muje gurin su Mai martaba dan duk abunda ake faɗa tun daga farko har ƙarshe munji komai! ".




Haka muka doshi ɗakin Mai martaba duk da kuwa yawan mutanen biki da suka cika ko ina na cikin gidan, a can ne, Mai martaba yayi muna faɗa sosai shida Dad shine muka shirya zuwa Abuja kuma Alhamdulillah mun iso da wuri, bamu san lokacin da Bro ya baro mu ba, amman ya kiramu yace, na kira Anty Narjeesh akan cewar duk abunda sukeyi su isa ɗakin Mai gadi, a cikin daren, to kunji abunda ya faru".




Murmushi nayi nace, "Allah sarki sannun ku da ƙoƙari" anan ne Daddyn Shuraim ya ce, "a lokacin dana zo gidan, sai na shigo cikin sanɗa batare da kowa ya ganni ba in, banda yara na, masu, kare lafiya ta, shine na shiga cikin gidan na zubawa Haulart maganin bacci a cikin ruwan lemon da ta a jiye ta shiga toilet, ina kallon ta ta jikin labule har ta shanye duka anan ne bacci ya ɗauke ta, ni kuma na baro ɗakin naje ɗakin mai gadi dan jiran zuwan su, ai kuwa suna zuwa na ɓude masu ƙofar na ɓuya, kasan cewar yasan da zuwan nasu tun kafin nazo, to anan ne, suka gane cewar mahaifin su ne, kuma shima ya ƙarasa dawowa cikin hayyacin sa"


A Nan ne yaci gaba da basu labarin har zuwa yan zun da komai yake faruwa a gaban kow.




Cikin sauri Miss Naseer ta nufi gurin Miss Yaseer da niyar dukan ta, cikin tsawa mijin ta ya ce, "haba dai tun kafin kiji naki saka makon, to tun da kin so jin naki tarihin bari kiji".




Turus tayi tana kallon mijin nata, kamar wata hauka sabon kamu,


Ya ce, "to duk abunda kika ji Salma ta faɗa nine wanda take magana a kai kuma nine na basu information a kan ku, kuma nine na basu tarihin ku, da halayyar ku, kuma Yaseer da Nazeer dani kai na duk kowa ya bada gudu muwar sa, a cikin wannan aikin, kuma Salma da kike gani ita ce nayi niyar Aure ita ce muka haɗu da ita a shari'ar da sukayi ta farko wadda na bata, rigata, ta rufe jikin ta, saboda kallo ɗaya nayi mata, a lokacin suna baƙin zuwa wannan ƙasar, kuma ni ban san ya ya, akayi ba kika shigo rayuwa ta, har na Aure ki, dan haka yan zun ina yi maki albishir da cewar, an ɗaura Aure na nida Salma yan zun haka, ita a matsayin mata ta, take".






Wani irin uban ihu tayi ta zube a ƙasa sai ihu take zubawa tana ba zai yuyu ba.


Kukan mutum ukku da ihun su kawai kake jin yana tashi a gidan dan duk sun cika wa mutane kunne, ihu Nazeer ya ce, "Shin yan zun guguwar ta zo ne ko da sauran ta? ".




Da sauri Miss Nazeer ta ce, "aa kada ka ce komai a gurin nan na roƙeka da ka tausaya mani! " sai gir giza kai takeyi.




Wata uwar tsawa ya daka mata ya ce, "yan da kika rabi da iyaye na, mata ta da yarana da kowa sukaji baƙin ciki kema sai kinji fiye da hakan shegiya muna fuka azzaluma! ".




Mai martaba ne yayi gyaran murya ya buɗe taron da addu'a, bayan ya ƙarasa ne, ya ce, "tabbas Allah shine mai iko akan komai, gashi Allah ya baku aron dama kunyi watsi da ita, to bari kuji Salman da wannan yarinyar Narjeesah ni ne, na saka aka ɗaura masu, Aure tun lokacin da tsafi gaskiyar mai yin sa, ya saka, aka sato yar mutane da niyar cin zalin ta, na riga su, a gurin domin nine na saka aka bar hotel ɗin da aka yada su, kuma wannan yaron da ake rigima a kan sa, ɗan halak ne gaba da baya" anan ne Mai martaba ya basu labrin komai har zuwa yau ɗin nan.




Ham dala kowa keyi duk da ni da su Yaya Jafar dasu Amrah dasu Humaira da su Salma mun san da wannan zan cen wanda basu sani bane kawai suke cike farin ciki, saɓanin mutum ukku, wato Haulart da wanda a tare suka wani ƙurma uban ihu suka bushe da dari suka fara yaga kayan jikin su, sukayi waje da gudu suna ihu, duk abunda suka gani sai sun daka, cige gashin kan su sukeyi, wata irin uwar guguwa ce ta taso, ta tur nuƙesu tayi sama dasu.




Mutane kuwa kowa yayi ta kan sa da gudu.




Nan nauyar ajiyar zuciya kowa ya sauke, Mai martaba ne ya ce, "to kun dai ga ƙarshen masu shirka, duk wanda yace, tukunyar wani ba zata tafasa ba, to shi tasa tukunyar ko zafi ba zatayi ba, dan haka muji tsoron Allah a duk inda muke, ku kuma Allah ya saka maku da alkhari, gabaki ɗayan ku, Salman kuna sakaci da addu'a duk da nasan ka da ƙoƙari, kuma ita ƙaddarar mutum duk inda yake sai abun nan ya shafesa, sai dai saboda addu,oi abun ya zowa mutum da sauƙi, Allah ya ƙara bamu kariyar sa baki ɗaya ".






Amin, duk aka amsa Mai martaba ya sake cewar, ku tashi kowa yaje ya shirya yau zamu bar garin nan, kema Salma bikin da ya rage sai kuje ku ƙarasa, Narjeesah da mahaifin su, a maida su gidan su, dan hankalin Umman su ya kwanta".




Kowa ya amsa da "Insha Allah".


Dad ne yakewa Shuraim wasa, yana faɗar, "abokina zaka bimu ko? ".


Ai kuwa da sauri ya tashi ya gudo ya haye jikin Amrah ya ce, "gurin Umma zani, ita ne mai yi mani wasa, tana siya mani kayan wasa kuma tana sakani nayi bacci na mai daɗi... "




Ai kuwa dariya aka saka masa, tashi mukayi, cikin farin ciki nida Nusaiba mukayi waje, Amrah tana riƙe da hannun Shuraim sukaje suka janyo trolley ɗin mu, suka fito shima Baban mu, ya ɗauko kayan sa, duk kowa yayo waje, motoci aka shiga, nida, Humaira Hindu Amrah Nusaiba Shuraim mota ɗaya Yaya Jafar Aliyu Baban mu mota ɗaya, Salman Salma Muhseen Dad Mom motar su ɗaya, Mai martaba mota ɗaya Naseer Yaseer Nazeer Miss Yaseer motar su, ɗaya.






Haka muka ɗauki hanya sai gidan su Ummey muka ɗauko kayan mu, mukayi mata, sallama muka rabu cikin jimamin juna, tana tsokanar Shuraim, haka muka nufi airport, jirgi muka hau dukan mu, yan yola, cikin ikon Allah muka sauka lafiya, yaron Yaya Jafar ne yazo da motoci muka shiga sai ƙofar gidan mu, ai kuwa Shuraim da Nusaiba da gudu sukayi cikin gidan, mu kuwa dariya mukeyi masu, muka mara masu baya.






Umma ce zaune tana famar kiran wayar mu amman shuru, duk hankalin ta, ya tashi kamar daga sama taji muryar Shuraim yana kiran Umma..... Umma...., ai kuwa da sauri ta buɗe idon ta ganin Shuraim ya shigo da gudun sa, ƙofar falon ma da ƙarfin sa, ya turo yayo kan Umma cike da farin ciki ta cafe sa, ta rungume tana dariya Nusaiba ba ce, ta shigo itama ta rungume Umma tana dariya, ahaka muka same su.






Hindu ta ce, "kai Umma sune kawai kike yiwa oyo amman banda mu".


Sai a lokacin ne Umma ta ɗago idon ta, ta kallemu taga kowa ya zauna yana murmshi, ta ce, "to bayan kun nemo muna wannan mai saka mutane kuka ya hana su cin abinci? ".




Dariya mukayi Humaira ta ce, "ai dole ne muyi kuka Umma, kema fa kawai kinyi dauriya ne, amman fa abun babu dama".




Dariya Umma tayi tace, "Humaira ungo wannan na ce gidan ku".




Dariya muka shiga yi, a dai dai lokacin da su Yaya Jafar da Yaya Aliyu da Baban mu suka shigo bakin su ɗauke da sallama, amsawa Umma tayi ai tana ɗaga ido, kawai sukayi ido biyu da Baban mu, cikin wata irin zabura Umma ta tashi tsaye, ta zaro ido tana murza idon ta ta gani ko mafalki ta keyi ne, da sauri muka ƙarasa inda take muka riƙe ta, sai jikin ta, ke rawa bakin ta sai mur_mar yakeyi ta kasa furta kalma ɗaya.




Nusaiba ta ce, "Umma a zahiri ne ba a mafalki bane , Baban mune da kan sa, wanda kowa aka sanar dashi mutuwar sa, ashe yana a raye wasu ne dai suka mutu".




Zaunar da Umma mukeyi Amrah tace, "a gidan Daddyn Shuraim muka samesa a lokacin baya cikin hayyacin sa, sai da idon sa ya sauka akan Anty Narjeesh san nan yadawo daga cikin hayyacin sa".




Kuka Umma ta fashe dashi, shima Baban kukan yakeyi ganin hakan ne ya saka Yaya Aliyu ya ce, "dan Allah ku dai na kukan nan haka, kada ku saka kowa ya kama kukan, tun da Allah yasa Baban yana a raye kuma an samesa ai sai godiyar Allah ".




Share hawayen su, sukayi, kowa yayi shiru sai Shuraim ne ke wasa a jikin Umma yana jan jelar gashin Umma, yana dariya.




Tashi Umma tayi tace ku tashi Amrah keda Nusaiba ku kawo abinci muje na nuna maku, komai".




Abincin aka kawo bayan anci ansha ne, Amrah ta labar tawa Baban komai wan da yayi kuka sosai, shi kuma ya ce, sai sun koma gida zai basu labarin abunda ya sani game da hatsarin, kowa yayi na'am da hakan.




An ajiye maganar tafiya gobe laraba da safe, ai kuwa su Yaya jafar sukace duk tare za'ayi wannan tafiyar dasu, dan haka sukayi sallama suka tafi tare da matan su, mu kuwa cikin farin ciki muka kwana ga Shuraim a jikina.




Yau tun da mukayi sallar Asubahi, bamu kwanta ba, muka shiga haɗa kayan tafiya, Umma kuwa suna kichin ita da Auta da Shuraim.




Bayan mun gama shirin mu, mun ci abinci su Humaira suka zo daga baya su Hindu suka zo, muka shiga fitar da kayan mu, motar Yaya Jafar muka shiga muka ɗauki hanya.....






*Comment and share*




*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹




💐💐 *NARJEESAH* 💐💐




*Rubutawa*
*NANA KHADEEJATU*
*_UMMU IHSAN_*


*ELEGANT ONLINE WRITERS*


_*Bismillahir Rahmanin Rahim*_




*Hahhhh😂🤣 Narjeesah team kun fa sakani dariya, a page biyu, 36/40 41/45, haba dai har kun manta cewar mutuniyar taku, irin gidan da ta fito gidan mata huɗu gidan makirci? Tafa san ta kan kishi da iya zaman da mutane, kuma, cikin Shuraim shine ya saka ta, ta dawo wata irin shiru_shiru da ita, amman kowa yasan Narjeesah bata dama, haka Amrah, dan haka nasan yan zun kun gane dalilin da yasa, sukayi, acting ta maida Sunan ta NARSAL*




*Ina godiya sosai da Comment ɗin ku da sharhin ku, kuma ina ƙara godiya da addu'ar ku, sosai*


4️⃣6️⃣⏯️5️⃣0️⃣




➿➿➿➿➿➿➿➿➿ Tafe muke a cikin motar Yaya Aliyu Hindu na gefen sa, nida Amrah da Shuraim muna a baya, kowa ka kalli fuskar sa, a cikin farin ciki yake.


Yaya Jafar kuma shine ke driving Humaira tana gefen sa, Baban mu da Umma da Nusaiba suna baya, kowa yana cike da farin ciki idan ka kalli fuskar sa, amman Baban mu ba zaka gane wane yanayin yake a ciki ba.


Shuraim sai surutu yakeyi, yana faɗar, "yeeee! Mun hau mota zamuje yawo, Uncle ka siya mani giwa da zaki inyi wasa dasu, mu shiga ta cikin wannan jejin muyi ta faɗa, da... Da... Dami ma ake ce masa Anty? "


Dariya mukeyi, Yaya Aliyu ya ce, "nikam ba zan iya siya maka giwa da zaki ba, amman inda kace, na siya maka doki ka hau zan iya kayi ta su guda" da dariya ya ƙarasa zancen.


Haɗe rai Shuraim yayi Hindu ta, juyo tana dariya tana kallon Shuraim ta ce, "kada kayi fushi nawan bari na anshi wayar sa na kira maka Daddyn ka, nasan shi zai siya maka su, ko? ".


Kwallar idon sa ya goge ya gyaɗa mata kai, Yaya Aliyu ya ce, "kai my boy badai kuka kake yi ba, to yi hakuri da wasa nakeyi maka, zan siya maka duk abunda kake so, kaji yaro na? ".


Maƙe kafaɗar sa yayi, mukam dariya mukeyi masu, Hindu ce, ta ɗauki wayar Yaya Aliyu ta kira number Daddyn Shuraim, ai kuwa ringing biyu, ya ɗaga suka gai sa, take sanar dashi Shuraim ke magana, ya ce, da ita "bashi wayar ki saka mashi Hans free".


Hans free ta saka mashi, ta bashi wayar, shi kuwa ya amsa, yayi kwanciyar sa, a jiki na, ya fara faɗar, "Daddy ina kwana? " dariya ya yi yace, "lafiya lau my lovely son, ka tashi lafiya ya Umma na, dafatan ta tashi lafiya da Baban mu da su Amrah da waye ma? ".




Dariya Shuraim yayi yace, "lafiya lau Daddy baka ce, da Mommy na ba, kuma muna cikin mota zamuje wani gurin, kana zuwa muzo mu tafi da kai ko? ".




Shima dariyar yayi, ya ce, "Shuraim ai Mommyn ka bata son tafiya fani, kaga bata sanar dani ba, ko? Amman zan zo yaro na dami kake son na zo maka dashi ne? "




Cikin sauri Shuraim ya ce, "Daddy zaki da giwa, da doki mai tashi sama"




Ai kuwa kowa ya saka masa dariya shi kuwa Salman ɗin ya ce, "to kai kuwa yaro na a ina ne, zaka ɗaure giwa da zakin ka kuwa san Mommyn ka tsoron su takeji ko? Kuma gashi har doki mai tashi sama, ina fatan dai zaka hau dokin".




Cike da jin haushin su, na ce, "ai da yake shi mutum baya tsoron zakin dolene a cikawa mutane baki, kuma kada a sake sakoni a cikin shirmen ku ehe! ".




Dariya yakeyi ta cikin wayar, haka su Amrah, Shuraim ne ya ce, "Daddy ka kawo mani mage ƙarama mai kyau ".




Da sauri na ɓalla masa harara, na ce, ki nemi gidan uban da zai kai maka ita, ku ajiye, kai wallahi kun fa fara cika ni, zan baku mamaki, idan baku fita hanya taba".




Yaya Aliyu ne, ya ce, "to ke Narjeesh wannan faɗan kuwa, kamar yana a gaban ki, firar suce sukeyi a tsanin ɗa da mahaifin sa, sai kuma kiji haushin su? "




Ni kuwa na ce, "to baka jin sune suke sako suna na a cikin zan cen su? To kayi masu magana mana su dai sakani a harkar su, ehe! "




Dariya sukayi shi kam firar shirmen su sukeyi kuma duk abunda nake faɗa, a kunnen sa, ne yaƙi magana sai ma cewa yayi, "Shuraim ka kirani da wayar Mommy ka yan zun sai muyi firar mu ko? Ka baiwa Uncle wayar sa kaji yaron kirki? ".




Dariya yayi ya baiwa Hindu wayar ta kashe suna dariya, kallona ya keyi yana son na bashi wayar amman na ɗaure fuska, kuka ya saka, na kallesa, na daka masa tsawa, "rufe mani baki daga nan ko yan zun nayi maganin wannan rashin kunyar, anƙi a baka wayar, tunda da kuɗin ku na siya, ko kuma ta mutum ce, na ɗauka dole sakani abunda banyi niyar aikata wa ba, kuma ba zaka kira shi da wannan wayar ba, sai dai ku zauna kurame ni babu ruwa na, a ciki" ina zare masa ido.




Ai kuwa cikin jikin Amrah ya faɗa ya saki kuka yana kiran "Dadd... Daddy", share sa nayi kamar bana a kusa.




Amrah ce ta shiga lallashin sa, da taga yaƙi yin shirun ne, ta rasa ya zatayi, zuwa can tayi kamar zatayi kuka, ta ce, "Anty Narjeesh dan Allah ki aro muna wayar taki, mu kira masa Daddyn nasa, tunda ba kece zakiyi maganar ba, kinji Anty Narjeesh wallahi har jikin sa ya fara zafi".




Shareta nayi, itama tayi shiru Hindu ta ce, "shima dai Salman yaso ya haɗa wannan rigimar ne, yasani sarai, Narjeesh ba zata bada wayar ta ba, amman ya saka Shuraim a ciki dan ya fahimci rigimar sa, ke kuma dan Allah ki basu aron wayar tunda ba cinye wa za suyi ba".




Kamar nayi kuka na zaro wayar a jaka ta na bashi, ai sai kukan ya dawo dariya idon sa da hawaye amman dariya yakeyi.




Suma ajiyar zuciya suka sauke suna dariyar, Hindu ce ta anshi wayar ta saka number ta kira, ta saka murya ta bashi da farin ciki ya amsa, ya fara magana amman bayaji saboda munzo gurin da service yake rawa, dole ya haƙura, zuwa can yayi bacci, sai a lokacin ne Yaya Aliyu ya ce, "Narjeesah wai miye ya saka kika saka yaron nan kuka kuma ba zaki lallaba sa ba, kodai irin yanda Umma takeyi maki zaki yi masa ne? ".




Na ce, "to ya zanyi masa, ai dai kasan ni bana son lambar wayar wani ta shiga cikin waya ta, sabo bana buƙatar ya takura ni, tunda ba shine ya siya mani wayar ba".




Ya ce, "amman kin san zai iya siya maki wadda tafi wannan ko? "


Na ce, "aa ni ban sani ba dan ban buƙata ba, kuma ban roƙa ba".




Hindu ta ce, "hahh wata rana zaki buƙata Miss Salman Allah dai ya ƙara danƙon soyayya dan wannan zazzafar soyayyar tana tafiyar dani ne fa".




Tsaki kawai na sakar masu ban sake bin ta kan su ba, tafiya kawai mukeyi , amman mun tsaya a hanya munyi sallah munci abinci mun riƙo wani, na guzuri sai gab da magriba muka iso garin namu, ham dala muka shiga yi mun shigo garin dutse, a wani hotel muka sauka, muka kwana, tun da safe muka ɗauki hanyar shiga garin gumel, mun iso cikin garin gumel lafiya muka ɗauki hanyar shiga ƙauyen mu.






Tafe muke wasu zafafan hawaye ne, suka shiga zubo mani, ina tuna irin fitowar da mukayi a lokacin, kallon Amrah nayi naga tana wani makirin murmushi, ta ce, "Alhamdulillah Allah mun bar garin nan da far gaba da tashin hankali da tunanin makomar gurin da zamu sake sabuwar rayuwa, sai gashi yanzun zamu shiga garin nan da ƙarfin mu, kuma cike da farin ciki, da tarin nasa rori".




Kwatan ce hanyar da zasu bi Amrah takeyi, har muka iso ƙofar gidan

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads