Header Ads
Showing 24001 words to 27000 words out of 58708 words

Chapter 9 - NARJEESAH Book Complete Document By Nana Khadijatu .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

Salma da Muhseen suka zubawa ƙofar ido.


Ƙarasowa yayi inda suke ba tare da yace dasu uffan ba kawai yaja hannun su ya ƙarasa fita dasu a cikin wata mota aka ɓude masa ya saka su a ciki shima ya shiga daga ciki aka rufe, yaye mayafin fuskar sa yayi, atake suka haɗa baki gurin faɗar, "grandpa!! ".


Murmushi kawai yayi masu ya bada umarnin tafiya, aka ja motar, sai tafiya sukeyi, cikin wata unguwar da wasu mutane duk a waje suke kwana, saboda gida jen su duk sun rishe, wasu zane ne suka ɗaura suka killace, parking akayi a hankali ya sauka daga cikin motar ya fara jawo hannun Salma da take ita ce a kusa dashi, sai kuma yaja hannun Salman da Muhseen, duk suka fito suna dube_dube gashi dare ne unguwar sai ɗoyin kwata ke tashi, bayan motar aka buɗe aka riƙa sauke kwalayen taliya indomie shinkafa irin buhun nan masu ɗaukar kwano huɗu, ƙanan jarkar manja man gyaɗa magi gishi, sai amblant, layi Mai martaba yake bi yana ajiye masu kayan a gaban su tare da amblant ɗin, su Salman kuwa cike suke da mamaki, wata mata ce ana ajiye mata kayan zasu tashi da sauri ta riƙewa Mai martaba ƙafa, ta fashe da kuka, Mai ne ya ɗuƙa yace, "mike faruwa ne daga ganin wannan kukan kin daɗe kina yin sa"


Tashi zaune tayi tace, "dan muna talakawa shine aka maida mu bayi babu mai kulawa da halin da muke ciki, maru nd gareni mata biyu dan rashin imani anzo an ɗauke mani su duka duk anyo masu ciki, ɗayar gurin haihuwa ta haɗu da lalurar yoyon fitsari kuma, mutanen ya ce, ba zai iya ɗaukar nera ya bamu ba mu nema mata magani ba, kuma bamuda wanda ya isa ya kamasa da laifin cikin da yayi mata kuma ya saka ɗan sa ya ɗauke ƙaramar itama yan zun haka tana ɗauke da cikin ɗan sa, munje police, an koro mu, to shine "yar tawa tace zata kashe kanta, nikuma na hane ta da aikata hakan shine suka gudu suka barni, wai basu kashe ni da baƙin cikin suba! ".


A take jikin kowa yayi sanyi a gurin, Salman ya ce, baku da human right ne a ƙasar nan? ".


Shiru Mai martaba ya yi kukan tsohowar na damun su, Salma tace, "yaran naki kin san inda suka tafi ne?".


Kai ta gyaɗa masu ta ce, "ance mani an gansu, amman na kasa zuwa inda suke gudun kada su bar gurin ".


Salman ya ce, "zamu zo da safe amman kiyi shiru da bakin ki".
Tashi sukayi suka ƙara sa gaba, haka sukayi ta cin karo da masu matsala, matsalar wani dattijo ta ƙara sanyaya masu gwiwa, saboda yaran sa ukku biyu maza ɗaya mace, ne gobe za'a yanke masu hukuncin kisa, saboda sun sace wa Mai gidan da suke yiwa aiki maƙudan kuɗade, a take hankali kowa ya tash.


Muhseen ne ya ce, kuma an tabbar da sune suka aikata hakan? "


Dattijon ya ce, "harda shedu suna su wanda suka ce, sun gane su da idon su suna aikata hakan, kunga kuwa ni babu abunda zan iya faɗa duk wanda mukaje gurin sa ya taimaka muna sai ya ce, shi sam baya iyawa, wani mane yace, zai taimaka muna amman sai mun bashi miliyan ɗaya, ni kuwa ko abincin da zamuci wahala yake yi muna nida mata ta da ƙana nan yara na, wani kuma ya ce,zai taimaka muna ashe ƙarya yakeyi, wannan mutanen ya turo shi, muna zuwa kotu, yace shi ba lauyan mu bane lauyan mutumen ne! ".


Tashi tsaye sukayi Salman ya ce, "zamu zo da safe insha Allah ".
Gida suka koma har ɗakin da suka baro Mai martaba ya raka su,suna shiga suka rufe ƙofar, suka kunna glub, duk suka zazzauna a ranar basuyi bacci ba, tun da asuba Salman da Muhseen suka nufi masallacin gidan kowa ya gan su a wannan nan lokacin sai yayi mamakin hakan amman su basa kula kowa har akayi sallah sai da safe suka fito bayan sunyi azkar".


Darect gurin Mai martaba suka nufa a cikin falon gidan inda kowa yake kawo masa gaisuwa, kowa ka gani cike yake da mamakin ganin Salman da Muhseen, Mai martaba suka nufa suka rungume sa, suka sumbace shi, zasu juya ne ya janyo su jikin sa, shima yayi masu yanda sukayi masa, yace, "Allah ya yi maku albarka ".


Amin kowa ya ce cike da farin ciki, Salma ce ta fito itama da shagar ta ta ƙananan kaya amman wannan da ɗan damar su, ta zo ta rungumi Mai martaba ta sumbace shi, shima ya ce, "Allah ya yi maki albarka ".


Ta dawo gurin su Salman suka rungume juna, suka sum baci juna, ta koma jikin fulani ta sumbace tayi kwance a jikin ta, zama su Salman sukayi ƙasa a kusa da ƙafar Mai martaba, bayan sun zauna ne, ƙanen mahaifin su wata, shattima ya ce, "Alhamdulillah abu ya yi kyau sannu a hankali komai zai tafi dai_dai ".


Duk sukayi dariya, abinci aka kawo kowa da abunda ya ke ci, Salman da Muhseen Salma suka tsare kowa da ido cike da burgewa, sai da fulani ta ce, "ku ba zakuci komai bane? ".


Salma ta ce, "yau fa duk azumi mukeyi yau Thursday kasan cewar Dad da Mom sunayi shi yasa duk mun saba a kowa ne Monday da Thursday ".


Jin jina kai Mai martaba ya yi haka fulani da murmushi ɗauke a fuskar ta, wata budurwa wadda suke sa'a ɗaya da Salma ta ce, "shike nan ma kuwa daman naji labarin Uncle duk abunda ya keyi yana kaman ce ceniya da Mai martaba, gashi kuwa yau mun fara sani muma dan haka fulani ba zaku sake yin wannan azumin bada ni ba ".


Dariya akayi masu, Salman da Muhseen Salma ne suka tashi suka shiga ɗakin su, kowa ya fito a gyare Salman da Muhseen duk sun yo shigar su irin ta cikakken turawa, sunyi stoking, sai duk suka burge kowa Salma kuwa doguwar riga ta saka har ƙasa amman ta sako gashin kanta a ƙafaɗar ta, babu ɗan kwali sai fula facing cap, da haka a hannun ta, irin ta ma aikata, haka su Salman suke, kallon su kawai akeyi.




Mai martaba ne ya tashi ya ce, "kuzo muje daga ciki".


Murmushi kowa keyi da mamakin taya akayi Mai martaba ya shawo kan, wannan yan rigimar nasa, koda yake Mai martaba Allah ya yi masa baiwa wadda ba kowa ne yasan da hakan ba.


Ɗakin Mai martaba suka shiga anan ne shima ya shirya ya kira waya, ya yi magana sannan suka fito yana gaba suna biye dashi, fadar suka nufa, sai gaisuwa ake kwasa, kowa ya kalli, su Salman sai ya sake kallon su, motoci aka fito dasu, aka jera shiga sukayi su Mai martaba da tawa gar sa, su Salman suka shiga wata motar ta daban, suka ɗauki hanya, motocin Mai martaba hanyar su, daban suka ɗauka, haka su Salman, wani ƙayataccen gida suka nufa, suna yin parking suka zauna direban ne ya fito shida wani bafade da suke tare suka shiga, basu wani daɗe ba, suka fito sukayi masu iso.




Wannan dattijon ne da wannan tsohowar da wasu mutane su ukku a zaune saman kujera, hannu suka baiwa Salman da Muhseen Salma kuwa hannu ta ɗaga masu ta ce, "Hi".




Gurin zama aka basu suka tattauna tare da sake yiwa wannan dattijon tambayoyi yana amsa masu, haka wannan tsohowar, magana suka sakeyi da wannan mutanen, sukayi basu hannu sukayi masu sallama suka fita daga cikin gidan mota suka shiga suka nufi wani gurin basu daɗe ba, suka ɗauki hanya sai wata unguwar, a bakin wani gidan suka faka motar, bafaden ne ya fito yayi sallama aka amsa mashi mai gidan ne ya fito bayani yayi masa tare yake da baƙi mutumen ya ce, "nasan da zuwan su kace dasu si shigo".




Tare suka fito suka shiga cikin gidan iso mai gidan ya yi masu har cikin ɗakin sa, wannan tsohowar ce, da wasu matasan mata zaune sai kuka suke wata mata tana gefen su, zama su Salman sukayi, suka fara yi masu tambayoyi suna amsawa, daga nan suka fito suka ɗauki hanya sai wata babbar kotu, suna isowa yayi dai_dai da mai shari'a yana yanke hukunci kamar haka:-ni alƙali Muktar na kotun mages tree na yanke wa wannan yaran Haruna Nuhu Musa Nuhu Saude Nuhu hukuncin.. Da sauri, Salman ya ce, "ya mai girma mai shari'a ayi hakuri da zuwan mu a makare suna na Salman Yunus muhammad, loya ne ni mai zaman kan sa, ina tare ne da loyan Human right daga hukumar human right ta duniya, mune wanda zamu Kate wannan mutanen da ake ƙara, takardu ya baiwa wani maga takardar kotu, a take ya ansa ya baiwa wasu suka duba aka baiwa alƙali ya duba, umarni ya basu da su ƙaraso ciki su zauna, zama sukayi si biyu, shi kuma Muhseen ya samu guri ya zauna.




Lauyoyin gurin duk haushin shigowar su Salman sukaji, mutumen da yake ƙarar su, jin yakeyi kamar ya tashi ya kashe su Salman, su kuwa bayin Allah kuka ne kawai sukeyi, mutane kuma masu kallo gyara zama sukayi dan kowa son yakeyi yau ayita ta ƙare, bayan Salman ya zauna shida Salma, alƙali ne ya baiwa Salman damar fara aikin sa, aikuwa Salman ya tashi tsaya, rigar lauyoyi ce ya saka, yaje gaban su Haruna ya kafe su da ido ya yi murmushi san nan ya ce, "Sunan ka muke son sani ".




Kallon Baban su da innar su sukayi ganin sukayi suna hawaye suna ɗaga masu kai, aikuwa ya ce, "Haruna Nuhu" kowa gurin cike yake da mamaki dan tun da aka fara shari'a dasu wannan zaman shine na biyar sai yau suka taɓa magana shi kanshi alƙalin sai da ya jin jina.


Salman ya ce, "shakurun ka da aikin ka please".


Amsa masa ya yi shekaru na ishirin da shida, ina yin wanko da guga ne a gidan Alhaji Ƙasimu, shekara ta ukku a gidan sa ina aiki".




Murmushi Salman ya yi ya dawo gurin ɗaya ya tambayi sunan sa, sai ya ce, "Musa Nuhu shekara ta ishirin da ukku, ina aiki ne a gidan Alhaji Ƙasimu, nine wanda yake yi masa gyara da kula da fulawar sa, shekara ta biyu ina wannan aikin".




Itama Saude ta amsa masa amman ita abinci ne kawai take dafa masu, shekara ta ishirin dai_dai".


Salman ya duba alƙali da mutane ya ce, "ya mai girma mai shari'a ina son kotu ta bani dama nayi magana da Alhaji Ƙasim"




"Kotu ta baka dama" fitowa yayi yana tafe yana hura hanci ga uwar zufar dake zubar masa ta ko ina, yana tsayawa, Salman ya kafe sa da ido, ai kuwa duk ya daburce, murmushi Salman ya yi ya ce, "koto zata so sanin Sunan ka"




Kallon Salman ya yi, ya fara gyara babbar rigar sa, ya ce, "ba kotu ke ce ke son sanin sunana ba, kai ne kake son sanin suna na kaida ba ɗan nageria ba, su yan nageria ai sun san ko waye Alhaji Ƙasimu a ci dukiya! ".




Tun kafin Salman ya yi magana alƙali ya ce, "ina mai horon ka da ka guji kaucewa umarnin kotu nan kotu ce, ba gidan ka ba, dan haka dolene kayi biyayya ka yi duk abunda aka umurce ka idan ba haka ba akwai hukunci mai tsana nin da zai iya hawa kanka".


Salman ya ce, "nagode ya mai girma mai shari'a" kallon sa ya mai da aka Alhaji Ƙasimu.
Shiru ya yi ya sharce zufa ya ce, Sunana Alhaji Ƙasimu aci dukiya shahararren mutum wanda ya tara dumbin duk... ".




Salman ya ce, "dakata malam iya Sunan ka kawai muke son ji, kuma munji shin da gaske ne kamar yanda suka faɗa shekarun da suka ɗauka a gidan ka, haka ne? ".




Cikin gadara ya ce, hakane kuma tun lokacin basu taɓa shiga can cikin gida na ba, saboda bana son sa ido, ehe!".


Dariya mutane suka fara a ɓoye lauyoyin sane da sauri ɗaya ya tashi ya ce, " ya mai girma mai shari'a taya lauyan wanda yake kare wanda ake ƙara yake daburta mai ƙara? "


Salman ya kafe sa da ido shima a take ya tsuke bakin sa, ya koma ya zauna yana goge zufa, alƙali ya ce, ai ba matsa masa akayi ba, kuma ba tukura masa akayi ba, tambaya ce yake amsawa dan haka ƙorafi bai ƙarbu ba, sai a ki yaye loya, Salman ya duba yace, ci gaba "




Murmushi Salman ya yi, ya ce, "nagode ya mai girma mai shari'a ".


Salman ya ce, "kace basa shiga cikin gidan ka, amman duk shekarun da sukayi a gidan ka antaɓa kamasu da wani laifin ne makaman cin sata? ".


A a yace, kuma ni har ma mantawa nakeyi dasu a gidan, sai da akayi mani wannan satar ne, nagane ashe su ɓarayi ne kuma ni ina da shedun da suka ga lokacin da suka fito da kuɗin suka gudu".


Salman ya ce, "wato dai kai baka ga lokacin da suka fito da wannan maƙudan kuɗaden naka ba".


Ya ce, "eh kai nifa nagaji da wannan tambayoyin naka ne shi yasa nake sanar da kai gaski, kuma lauyoyin dana ɗauka duk sun kasa bani taimako, to gaskiya tunda ba lahira muke ba, zan sanar dakai wanda suka gan su da idon su, Mai gadi na Lado sai yara na maza guda biyu Ashir da Yasir, sune suka sanar dani a lokacin da nake haukar neman kuɗin nawa".




Kiran su aka ba Salman damar yi ya kuwa kira su, kallo ɗaya Salman ya yi masu, a take ya fahimci basu da gaskiya, Salman ya ce,"mai gadi kaine cikin ma'akatan gidan kaga lokacin da suka fita da kuɗin ko? ".






Tsuru_tsuru sukayi mai gadi sai soshe_soshe yakeyi, kowa ya kafesa da ido kawai ya fashe da kuka yace, "nidai ban ga lokacin da suka fita da kuɗin ba, kuma nima kashedi akayi mani akan nace sune, idan ban ce sune ba, kashe ni zasuyi, shine nazo nabada sheda suka bani kuɗi nera dubu hamsin ne suka bani, kuma wannan da muke tare sune suka fito da jakar kuɗin cikin dare kasan cewar ni ne mai gadin gidan dan haka ne, nima na gan su! "


Kuka yake, su kuwa tsuru_tsuru sukayi sai zarar ido sukayi, tambayar farko suka bada tabbacin sune suka saci kuɗin suka sayi mota suka ɓoye sauran kuɗin kuma sun kashe wasu, sun ɓoye wasu".




Hamdala kowa yakeyi shi kuma Alhaji Ƙasimu aci dukiya mutuwar tsaye ya yi jin cewar yaran sane ɓarayin ba yaran wasu ba, dan haka mai ɗa goye baya cewa ɗan wani shege, sai yan zun yasan fassarar wannan karin maganar.




Salman ne ya kalli mai shari'a ya ce, ya Mai girma mai shari'a ina son kotu tayi dubo da aikin da wannan bayin Allah sukeyi a gidan wannan mutanen kamar yanda suka faɗa da yanda mai gidan ya faɗa da yanda shedu suka faɗa, duk da kasan cewar sheɗun sune suka aikata hakan, da wannan nake son kotu ta wanke bayin Allah nan nagode ya mai girma mai shari'a ".




Yana zama alƙali yayi rubuce_rubuce ya ce, ko akwai wani mai magana daga cikin lauyoyin ne? "
. shiru sukayi Salma ce ta tashi tsaye ta ce, "Suna na Salma Yunus muhammad nice lauyan da human right ta turo akan wannan ƙarar kasan cewar duk wani haƙƙi na ɗan adam muna da alƙa dashi, muna neman haƙƙin wannan bayin Allah da aka zalun ta, aka yi masu ƙazafi aka kai su gidan yari suka sha kunun gidan yari, da duka idan aka dubi yanda suka dawo ga tabon duka nan ta ko ina da wannan ne muke jan haƙƙin su a gurin mutanen da ya kawo su, wanda shine sanadiyar komai, nagode ya mai girma mai shari'a "


Zama Salma tayi kowa mamakin yakeyi yanda akayi su ba hausawa ba, amman suke jin hausa kamar mi sai dai hausar tasu bata hau bakin su ba, da kyau, dan suna yin magana zaka gane turawa ne, su.




A take alƙalu ya yanke hukunci ya ɗaure su, ya wanke bayin Allah nan ya nemeni haƙƙin su akan Alhaji Ƙasimu aci dukiya saboda shine ya ɗaure su, kuɗi akace ya basu kowa ɗubu ɗari da hamsin dubu ɗari huɗu da hamsin ke nan.




a take ya ce su bishi gida su ansa hannu da hannu.


Kotu ce ta tashi da sauri Salman yaje ya yanki wani sammacin aka baiwa yaron alƙali yaje ya kai, ya tafi, fito wa sukayi shida Salma suna riƙe da hannu juna, gurin Muhseen suka nufa da sauri ya rungume su yana yi masu barka da samun nasara akan wannan shari'ar, jikin motar su suka nufa anan ne lauyoyin suka zo suka basu hannu Salman ne kawai ya amsa Salma kuwa kai ta ɗage, fadawa ne suka zo kiran su, cike da mamaki kowa yake kallon yanda fadawa suke duƙawa suna gaishe su, tafiya sukayi gurin da mai martaba yake tare da tawa gar sa da wannan dattijon da iyalan sa, suna yi masa godiya duk wannan lauyoyin suna biye dasu, su Salman na zuwa aka basu guri kawai suka je suka rungume kakan nasu tare da sumbatar sa, nuna masu yayi masu godiya kawai Muhseen ya ce, "mu bama buƙatar godiyar ku kuje kuyi ta muna addu'a ita ce kawai muke buƙata".


Hannu su Salman suka ɗaga masa, aikuwa sun sha addu'a haka suka tashi suka rafi, ɗan saƙon ne ya dawo tare da mutanen da akaje nema suna zuwa suka shiga chamber, anan ne aka sa santa suka ce sun yarda da cikin sune suka ɗauki nayin memawa ɗayar lafiyar ta, da kula da abunda ta haifa, itama ɗayar zasu kula da lafiyar ta da cikin ta har ta haihu tayi yaye dasa hannun kotu, kowa abun yayi masa, da daɗi, godiya da addu'a sun shata sosai.




Gida suka koma tun daga wannan ranar ne kullum cikin dare sai sunbi Mai martaba sun jiyo koken jama'a suna

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads