Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 46909 words

Chapter 2 - BAKAR IZAYA Complete Book by Ansholy .txt

Ads the beginning of article before Image

Ansholly   

01 Jul 2024

799

Ads at the middle of Article

muka bari dare yayi kana muka tafi


domin masu sa ido cikin ikon Allah da mukaje ba asamu wata matsalaba yasaya yabamu kudinmu


nawane ma alhaji hamza yace milyan 40 yauwa damuka amso munyi niyar mudawo gida aranar amma alhaji hamza yace saimun kwana to da daddare nida mlm sule mukai shawar gwara asai wani abu da kudin


A aje zaifi da ace kudin xamu taho dasu kana in ansaya saimuba alhaji hamza ajiya to da haka muka kwanta


Da safe muka samu alhaji hamza da maganar shima ya amince da hakan amma yace bazai amshi ajiyar ba


daqel muka shawo kanshi yayadda zai amsa amma saida yakira mai dakinshi yafada mata da yaranshi dan shekara goma


mai dakinshice tabamu shawarar gwara musai diamond haka mukaje muka sayo diamond din milyan 39 akabarman milyan 1 ahannuna


shine damuka dawo mukace zamu taho yace saiya biyomu dan asamu sheda muma awurinmu


yana zuwa nan yai shiru saida najima shiru domin ina ganin wannan kasace




Hakanan daganin mutum saika yadda dashi harka bashi ajiyar milyan 39








*Ansholly*😘
[3/8, 1:05 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭9








😘Ansholly😘










Wannan gangancine amma saina bar abin azuciyata nafara mgn to mlm amadu


Miyasa kasaida raqumanka nibaka fadaman ba saida yayi jim kamar bazai fada manba kana yafara mgn




abinda yasa nasai dasu shine kasan ni yata daya dije kana yanxu ta Allah takasance


kaina nasan yan uwana bazasu ba dije gadoba koda sunbata ba wani mai yawa zasu bataba


shiyasa nayanke shawar tunkamin ta Allah takasance agareni gwara nayi kyauta da dukiyar


saida sarkin yaqara gyara xama kana yace to dijar kaima kyauta da dukiyar taka indai har ita kaba


to kaima kasan kayi rarguwar dubara dan kana mutuwa yan uwanka saisun amsa




a,a ba ita nababa dan daxata haifa naba ko yarda zata haifa nabasu halak malak



to shikenan Allah yara basu da abinda ke cikinta lfy aka amsa da Amin mlm sule ne yace ya kamata akira dangin mlm amadu asanar dasu


haka aka aika kiransu amma saida mukacema alhaji hamza yatafi domin inhar sukazo suka iskeshi to zasu iya bigeshi su amshi diamond din




Kana mlm amadu yace kadda yasake ya qara zuwa rugarnan sai bayan shekara shabiyar lokacin komine ne dija tahaifa ya girma yana tafiya bada jima waba saiga yan uwan mlm amadu




koda nagama fada masu abinda yafaru karkiso kiga yadda suka rikice tamkar dukiyarsuce aka saida kanan baffanshi harda daukeshi da mari danjin haushin abinda yai




harda cewa indai harbaije yadawo da wannan dukiyarba to babasu bashi




shidai shiru yai yaqalesu baice uffanba har suka gama zage zagensu saka tafi da amshe raquminshi daya dayarage


Allah yaso basuji cewa yanada milyan daya ahannunshi ba dan bankai ga fada masuba suka fars zage zage




nasan da har ita saisun amshe nandai nabashi haquri da abinda yan uwanshi sukaimai


yace bakomi ai abinda yasa yasaida raquman bawai dan dije na diyar shi daya ba jiyai suna shawarar xasu kasheshi inya fita kiwo


shiyasa yai maza yaje yasayar naji tausayinshi sosai sukatashi suka tafi suma hakadai




rayuwa taita tafiya yayinda cikin dije yakai wata tara haihuwa yau ko gobe
[3/8, 1:05 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 10








😘Ansholly😘












ranar asabar da asuba dije tasauka ta haifi kyaikyauwar yarta wace hatta unguwar xoman data wanketa saida yarinyarnan tabata tsoro


dan kyan yarinyar yayi yawa amma datai wani tunani taga daga uwar har uban kyawawane shiyasa yarinyar tazama maikyau haka




da akaba iro karkiso kiga murnar dayayi yana godiya ga Allah dan kyan yarinyar firgitashi yayi


To aqa idar garinnan inhar matar mutum tahaihu dole yaje masallaci yafada haka yai alwalla yatafi masallaci cikin farin ciki


bayan angama sallah yace matarshi ta haihu tahaifi diya mace kamin yagama rife baki




Wani yace kace annoba tafito duniya wadda in akace uwarta nada ciki mutum yanayin asara ina ace anhaifeta


shima kamin yarife baki wani yaro yashigo massalacin dagudu yace adamu babanka ya mutu kamin yaran ya ida magnar nan adamu ya fece daga




Masallacin da gudu kamin mi wani yinquri wasu yaran suka kaqara zowa suka fadamana mutuwar mutum ukku hadda kakanki
mlm amadu


da gananfa mutane suka fara tsanar dije da iro haka akakai matattu har hudu gidansu na gaskiya yayinda mahaifiyarki dije har suma tai




hakadai akaita zaman gaisuwa yayinda mutane ko kallanki basuyi daga dije sai iro saikuma kakaninki matake daukarki wani abin mamaki tunda


aka haifeki baki taba koda rintse idankiba koda cikin dare idanki abude suke ranar da su mlm amadu suka cika sati guda aranar


tun cikin dare kike bacci kema aranar satinki guda aduniya abin yayima dije dadi dataga kina bacci danda duk atuna nunsu kobaki lfy


har anfara neman maki magani shiyasa duk yan rugarnan suka sani tunda aka haifeki kwana shidda baki taba bacci ba


wanda ansan jariri da bacci


to aqa idar rugarnan inhar mutum ya mutu to ranar daya cika kwana bakwai aranar zakiga


anata abin ciccika kamar anayin biki kuma har yanxu


ba adaina ba haka mata dayawa suketa kai abincin gidan mlm amadu




wani fura wani tuwo wani nono hakadai mutane keta shiga da qwarya an aje da anyi sallah la asar za ai addu,a lokacin bai ida karasawa ba




mukaji wuta takama agidan mlm amadu ga mata dayawa aciki dan aqalla matan dake ciki zasukai ashirin


muka tashi dankai dauki amma da mutum yatin kari wutar zakaga kamar ta biyushi haka munaji muna gani wutarnan tacinye mutanan ciki kaf ciki harda mahaifiyarki da matar mlm sule da matar marigayi mlm amadu da matar liman


saida mangariba tai kana wutarnan tatsaya batare da ankasheta ba gurin yayi sanyi qalau kamar bawurin akai gobara ba




haka mutane sukaita shiga cikin gidan amma inba tukaba ba abinda kake gani


Kakanki mlm sule sumewa yayi dan tashin hankali daman ga mutuwar amininshi bata sake shiba yanzu gashi matarshi


ta mutu wani abun mamaki ke kina kwance ba abinda yasa meki dan wasanki kawai kike da hannu wanki




*Ansholly*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 11








😘Ansholly😘




sadaukarwa g limsy🌺 ina godiya da addu,arki






haka mutane sukaita magan ganu akanki wasu suna cewa keba mutum bace qilan diyar aljannuce domin kuta kyanki aka duba ansanke ba diyar mutane bane




haka dai mutane suketa magan ganunsu wani mai zafin zuciya abbashe dan gidan jamo shiya daukeki ya samu karmami ya kunna wuta




yaje zai sakaki ciki alokacin muna chan wajan qokarin ibu tokar mutanan da suka qune ihun mutum kawai mukaji muduka da sauri muka fito daga inda muke


Abbashe ne muka gani cikin wutar yanata ihu wuta tana cinshi muduka kamar anriqe mana qafa muka kasa zuwa inda yake harsai da yacinye wutar tamutu


kana muka iya zuwa wurin yadda muka ganki acikin gida kina gefe haka yanzuma muka sameki sai wasa kike da hannunki


tan bayar mutane mukai cewa miya kawoki anan kida keki cikin gida nansuka fara bamu lbr abbashe ne yadauko ki zai sakaki awuta yazo dai dai wutar




sai yayi kamar anjefashi ciki muza musama harda yarinyar taqone hakadai muka sallaci tuka muka tai muka rife aka dawo da wata saban xaman




ke kuma babanki iro yadauke ki yatafi dake gida domin duk dacewa mutum ukku ya mutu agurinsu to ba wanda yakoma qofar gidan anadawo wa




daga maqabartar kowa yakama hanyar gidanshi dan atunanin mutane yanxu kuma maza xa akashe tunda bida bine abun andauki maza sai kuma aka dauki mata to




Insuka qara zama suza aqara dauka shiyasa da aka dawo maqabarta mlm sule yagaba wanda yabiyo su saiyaja iro cikin gida




yafaramai nasiha domin yaga yafara yadda da abinda mutane kecewa akanki shin iro ka yarda diyarka yar aljannuce kamar yadda mutane ke fada




iro saida yaqara sinkuyar da kai domin jiyake shima kamarya hadi zuciya ya mutu dan rasa matarshi dayayi da mahaifiyarshi


kana yafara magana to baffa zata iya kasan cewa haka domin daga yadda mutane sukace ba ataba




haifar mai kyantaba duk rugarnan ni kaina yanzu tsoranta nake




dan kyanta kanshi abin tsorone ballantana yadda kuma taxa mamma mutane annoba ciki hardani dan nima nayarda annobace aka haifa man kawai yasa kuka








*Ansholly*




*08136195038*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 12








😘Ansholly😘












Mlm sule zubama iro ido kawai yayi yana kallanshi saida yayi mai isarshi kana yaishiru




kana mlm sule yafara mgn iro kaban mamaki dahar dakai ake cema diyar daka haifa annoba kuma wai yar aljannu to inajin jinina ajikin yarka kuma nasan wannan


yarinya yarkace domin jini baya qarya da yarka bace da baxanji jininta ajikina ba kawai dai nasan da abinda Allah yabuye akan wannan yarinya




hakadai mlm sule yaitaima iro nasiha ta dai dai iliminshi cikin ikon Allah iro yasa duda yayda dake yarshice danda


da gaske kallan yar aljannu yake maki nan suka samaki suna hainan dan ba asa maki sunaba kuma yasan yanxu inyace atara mutane asa maki suna ba wanda zai iya


zuwa mlm sule ne yace iro ya dauko shanuwa guda cikin shanunshi ukku yanka maki na sunanki dan alqawari yai indai dija ta haihu saniya zai yanka mata dan haka kuda bata da rai bazai fasa wannan al qawarin daya dauka ba saida aka gama yankan shanuwar




kana suka kama tunanin waye xai soya mlm sule ne yace iro yaje gida zai bada akawo mashi shi yasamu wadda zaya turo tasuya




yana tafiya ahanya yagamu da uwale ita uwale ba yar rugarmu bace rugarsu nagaba datamu


uwartace ke aure anan shine tatahu da ita agolanci to uwale tunda taga iro taji tana sanshi amma shi alokacin baya takanta domin




dijen shice abun sanshi gaisawa sukai kana taimai gaisuwa yaji dadin gaisuwar da taimai domin tunda akaimai mutuwar ba
wanda yaimai gaisuwa




wasuma harararshi kawai suke yai mata godiya harzata wuce yatsaida ta


dan Allah uwale wani tai mako nakesan kiman


to Allah yasa zan iya dama baffane ya yankama hainan shanuwa to narasa wanda


zai suya man yancikin koxaki iya taima kaman ki suya man kamin gobe nasamu mai suyaman gangar jikin




saida tara zana dataji ance saniya aka yanka maki domin koni aka haihu gidana tumakai nake yankawa dan kinsan fullatani da shaninshi gwara




yaga tafadi ta mutu da ace anyankata uwale cikin saurin murya tace ta amince amma saitaje ta gayama innarta


bakomi saikin dawo dannasan lokacin har ankawo naman


kuda taje tagayama mahaifiyarta bata hanata ba itama dauko gyaletai tabiyo yar tata domin sunada san banza sosai


koda yaran da mlm sule ya aiko kawo naman yazo sai iro yace yafa dama mlm sule yasamu mai mashi soyen


haka uwale da mahaifiyarta sukaxo suka kama soye bayan angama sallah magarib iro yafadi


ansa maki suna hainan ba wanda yace mashi ko uffan


hakasu uwale suka gama soyansu suka tafi da alqarin gobema zasu dawo su ida sauran


haka kowa yake jininshi bisa akaifa har kika kai sati daya lokacin satin mahaifiyarki daya bata raye


kekuma satinki biyu aduniya amma tun bayan baccin dakikai kina sati daya aduniya baki kuma wni baccin ba




😘Ansholly😘
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 13








😘Ansholly😘












To abinda yasa mutane suka saki jiki shine da sukaga harkinyi wata ukku ba abinda yaqara faruwa


yayinda uwale tashi gema iro sosai tunyana shareta har yake yafara kulata domin yadda take kula dake


yanxu kuma yafara jin saukin yan rugar dan sun fara rage tsanar da suke mashi shida yarshi


haka baffanshi yaje ya neman mashi auran uwale ba asa bikin da nisaba domin uwale ta jima gida dan xata kai shekara 20


dan duk rugarnan ba tsaranta danmu yarinya nada shekara 13 muke aurar da ita


ansha biki lfy ankawo uwale gidan mijinta


ya yinda kike da wata tara kina tafiyarki ko ina


alokacin uwale tadaina kula dake saiki kashinki harya bushe ajikinki bata wanke ba har sai iro yadawo shi zaya wanke maki


ranar dazaki ciki shekara daya aranar kikai bacci


hankalin iro yatashi dan gani yake kamar abinda yafaru abaya zai kuma faruwa da assuba yatashi yai alwalla yatafi masallaci


dan sadda yaje ko liman bai samuba haka yatsaya har liman yazo iro lfy naganka haka cikin tashin hankali


bai iya boyewa limanba yafada mashi abinda ke faruwa


wanda yaci ace ya boye wannan abun acikin xuciyarshi danda bai fadaba ba wanda xaice




dan kincika shekara daya wani bala,i yafada mashi hakadai aka kira sallah


bayan angama sallah liman yatashi yafara gayama mutane abinda iro yafada mai


kana yace nafada makune dan kusan da zanchan dan kar abar mutane cikin duhu


nan akaita surutu kamar ba masallaci akeba wani cayake wallahi inhar tasake tataba mani wani nawa aradun Allah saina bajeta


hakadai iro yatashi yatafi gida jikinshi duk ba dadi domin saiyanxu yake dana sanin fadar dayai


yana zuwa gida bai daddara ba yaqara fadama uwale kamin tace wani abu taji sallama kobata fadaba tasan qananta ne tafito da sauri Audi


lfy nangaka tunda asuba gashi sai kuka kake
saida yaqarasa wani kukan


kana cikin kuka yace uwale inna ta mutu ihu tasaki wanda


saida yasa iro yaji tsoro yafito daki da sauri lfy uwale ita bata masan


miyake cewaba dan hanyar dakinshi kawai tai saidai kanantane kefada mai abinda yafaru ihun


hainan sukaji amma ko motsawa iro baiyiba dan yana ganin haka uwale kadai zatai tahuce abinda takeji


dan shima jiyake kamar yaje yai mata dan banxan duka saida uwale taga kinsuma kana taqyaleki domin duka tai maki bana wasaba


kamar tasamu wata abiyarta hakata dakeki ko tausayinki batajiba


alokacin data fito lokacin kuma wani yaro yashigo yafa dama iro mutuwar baffanshi


dagudu iro yafito daga gidan yai gidan baffanshi ita kuma uwale komawa tai dakin iro tadaukoki


suka tafi itada kananta saida sukazo dai dai wannan rafin da kuke ibar ruwa kana tasakeki ciki suka juya suka tafi


suka barki sbd tasan dole ki mutu koba kumi ke yarinyace baki iya ruwaba kuma tasan ba mai taimakonki


iro yaji mutuwar mahaifinsa wannan lokacin mutum biyar ne yamutu ciki harda dan liman hakadai muka kaisu makwancinsu


nikaina abin yafara bani tsoro hakadai nabar abin azuciyata


iro yaje yima uwale gaisuwa nan yake gaya mata yayanke shawarar kaiki bakin ruwa yadda aljanun zasu dauki abinsu


nan uwale ke fadamai aitun da akai mutuwar taje tasaki arafi bai wani damuba domin shi harga Allah


yadauka ke diyar aljannuce haka yai mata sallama yatafi zuciyarshi sawai dan jiyake yarabu dake dagashi har uwalan basu koma gida ba


sai bayan da akai sarakar bakwai kana iro yabi yama uwale suka tafi gida


uwale natura qofar dakinta tai arba dake kwance kina mata dariya




*Ansholly*




*08136195038*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 14








😘Ansholly😘












Da gudu uwale tafito daga dakin tare da fasa wata irin qara nabani mlm wallahi aljana adakina


tanata kerma wanda har fitsari tasaki batare da tasani ba


Iro da sauri yafito daga cikin dakinshi lfy uwale kijifa yadda kika saki fitsari daga tsaye


bata masan miyake cewaba dakinta kawai take nunamai tanace wa wallahi mlm


aljanace cikin dakinnan da dai yaga bata cikin hankalinta sai yashige dakinta


dasauri yajawo qofar dakin yace uwale kikace kin yadda hainan rafi amma miyasa naganta ada kinki


cikin rawar murya uwale tace wallahi mlm nakaita rafi har saida nagata nutse kana nabaru rafin




shi kanshi qafafuwanshi karma suke dan ya tsora yana tunanin ko uwale bata kaiki rafiba yaci ace kin mutu


Koda baki mutuba kinji gata domin ko babbane aka bari da yunwa natsayin sati daya dole yajigata ballantana yarinya


yajuyo yakalli uwale yace uwale aradun Allah hainan ba diyata bace aradu diyar aljannuce


kamin uwale tai wata magana kika bude kofa kika fito ai daga iron har uwalan waje sukai da gudu


suna naiman taimako karo sukaci da yalwa qawar uwale tace lfy mlm iro daga kai har uwalan naganku haka


kedai bari yalwa lokacin da kikazo man gaisuwa bana fada maki najefa hainan rafiba to wai yanxu muna dawo wa


na isketa ada kina itama tadan razana amma dayake yar duniyace saita nuna bata tsorata ba dan ita har burni tana shiga


haba mlm iro karkaban kunya mana kamarba namiji ba yanxu dai mushiga ciki


haka suka bita suka koma ciki amma atsorace suke


haryanxu tsaye take inda suka barta yalwa taje ta daukeki kana tajuyo takallesu


tace uwale nasan da gaske kinsa hainan arafi amma baki tunanin ko wani yaje yacireta




Sadda zaki sata ke dawa kikaje nida audi kanena kuma nasanshi da tausayi


shima ne yaje yacirota dan shika daine yaga lokacin dana sata


mlm iro shiru kawai yai dominshi bai yadda ba in ance audine yaci rota to wake kawo mata abincin daza taci waya budema audi dakin uwale


maganar dayaji yalwa nayi ita tadawo dashi daga tunanin daya tafi


Mizai hana mudau hainan mukaita chan kusa da rigar innarki uwale kinga acan ba wanda




ya sanmu bare mu ajeta wani ya biyomu da ita saida uwale tai jim kana tafara magana


tace yalwa shawarki tayi amma karki mantafa chan aka haifeni taya xakice basu sanni ba


aibacane mutafi tare dakeba tare da mlm iro zamu tafi


to hakanma yayi yanxu kuimaxa kutafi kamin ai magriba tunda ankusa




haka suka fito suka tafi saida suka kusan xuwa rugarsu uwale kana suka ajeki amma saida sukaga ba kowa kana


sai ana sallah isha,e kana suka dawo duk wanda yagansu ya tambayesu daga ina suke sai yalwa tafada masu dan dama surutu gareta




Aikin santa ko kai kawai tadaga domin kuka kawai take


kana yaci gaba haka suka dawo ma da uwale albishir taji dadi sosai


dan tana ganin sunrabu dake kenan iro tashiyai yatafi yaje yai sallah su kuma


Suka aza zancen duniya dan daga yalwar har uwalan sallah bata damesu ba


yalwa batabar gidanba saida dare yayi sosai kana tai masu salama tatafi


domin mijinta yajima da mutuwa gashi batada ya


tunda asussuba mlm iro yaji bugun qofar gida da sauri shida uwale suka fito dan bugun bana wasa bane


suna budewa sukaga yalwa tsaye duk jikinta shatin bulala


da sauri uwale tace lfy yalwa naga jikinki duk shatin bulala saida yalwa ta qara fashewa da kuka tace wallahi mlm iro


Aljanaka haifa


kuyi haquri fans am busy wallahi amma next insha Allah xanyi mai yawa




*Ansholly*
[3/8, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: 😭BAQAR IZAYA😭 18

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads