Showing 21001 words to 24000 words out of 46909 words
Chapter 8 - BAKAR IZAYA Complete Book by Ansholy .txt
tadago kanta bokanya wata bakwai yayi yawa nida nakeso yanzu dana koma gidata mutu
tsawarda bokanya tayice yasa dan uwale firgita yasa kuka
Ansholly😘
ðŸ˜BAKAR IZAYAðŸ˜
48_49
😘Ansholly😘
*wannan pagen sadaukarwace ga dukkan masoya bakar ixaya ngd d kaunard kuke nunama littafina*
*garin abuja*
hannu yasa yadafe zuciyarshi danjiyai tana wani irin bugu amma yana ganin tamkar arba dayi da abinda yaji nantake yanaso ne domin yana ganin tunda yake baitaba san wataba sama dawannan baiwar Allah wace ko sunanta baisani ba
nafi tasowa tayi daga wurin datake zaune dan tanasan yaji kamshin turaran da boka yabata sosai taba kafadarshi tayi firgigit yadawo daga tunanin daya tafi
ido takashe mai yadai my haisham kodai ban makaba ne
haisham da tunda yashaqi kamshin Nafi ya ida birkicewa yafara magna cikin voice dinshi mai saka yan mata surude irinsu halima Lol
tunda nake bantaba samun macen danaji tashiga zuciyata irinki inajinma yanxu dana fita daga nan kd zani dan inaso ayi auran nan cikin kankanin lokaci dan baxan iya jure rashinkiba akusa dani
dadin danafi taji Allah kadai yasani dan jitai tamkar tazuba ruwa akasa tasha amma tayi alkawari da haisham yatafi zata hada wani qwarya qwaryar party
kallanta haisham yayi yaga tatafi tunani tabata yayi lfy naganki cikin tunani
murmushi taimai kana tafara mgn ina tunanin Sa ar da Allah yabani nasamun qwarxan namiji irinka haisham ina sanka tunda naganka naji narasa sukuni harsai yau daka firta man kallamar so
kallanta yayi cikin murmushin shi dama kintaba sanina ne baby
sai yanxu tagane katobarar datasoyi girgixa kanta tayi a,a kasan dai inso yana azabar da mutum baima san miyake fitowa daga bakinshi ba
fira sukaci gaba dayi tamkar sunkai shekara yayinda haisham ma yamanta yana dauke da wata cuta mai suna aids yana ganin tamkar yanxu zaifara
aure kuma auran saurayi da budurwa
saida akayi sallah azahar kana yai shirin miqewa
baby nah baqo zaiyi halinsa zantafi badan nagaji dake ba saida i haquri ne domin inda xani danna sameki ne amma dazaki yarda kibini mutafi tare dana tafi dake saidai nasan baxaki iyaba
cikin kisisina irintasu ta yan bariki tafara mgn nima haka nakeji my haisham jinake tamkar karmu rabu amma yaxanyi tunda tafiyar taka takasance wacce xamu xama abu dayane saidai kawai naimaka addu,a
shafo fuskarta yayi baby kintafar man da xuciyata gabaki dayanta inama ganan gaba
amma kinman laifi m kallanshitai alamar firgici afuskarta laifin minai ma my haisham
murmushi yayi kwantar da hankalinki baby bawani laifi kikaiman mai yawaba
sunanki ne baki fadaman kinaso naje gida dad dina yatambaye ni nakasa fada dakuma garinku kifada man komi
sunana nafisa mubiyu ne wajan iyayenmu nida yar uwata sadi mahaifina Allah yaimashi rasuwa shekara goma data gabata wani hawayan muna firci tashare daga fuskarta
ayya sry Nafisa Allah yajikan baba
amin tace kana tafara mgn sunan qyauyan mu sulaja
mahaifina kamin yarasu yanada rifin asirin shi amma tunda ya mutu yan uwanshi
suka kwace mana komi yazam mana abincin dazamuci yana gagararmu to lokacin Dr bashir yaje qyauyanmu domin duba asibitin cikin qyauyan ko wa inda aka turo suna aiki yadda yakama to anan yaga yayata yace yanasan ta
kamin takara mgn wayar haisham tadauki qara da sauri yadauki wayar assalama alaikum chan dayan bangaran akace
wa alaikumussalam dad ina wuni lfy dama cemaka xanyi inbaka samo matarba toni nasamo ma yarinyar mutinci diyar alhaji Ahmad aikasan irin tarbiyar dayake ba yaranshi ko
murmushi yayi dad karka damu nasamu wata yarinya mai tarbiya gani nanma wurinta tace nagaida ka duk mgnr dayake idanshi nakan Nafi
shima alhaji hamxan fadada fara,arshi yayi to ina amsawa yaushe xakazo gidan dan xaman dakake ba mata yana damuna
dad yau ina nan tafe to saikazo kashe wayar yayi yakalli Nafi to nidai xan tafi baby inajin sai gobe xandawo inna dawo xaki idaban lbrn
dariya tayi tace saidai muhadu asilaja dan gobe muma zamu tafi dan afada masu dawuri to xanm sameku achan din kiran orderly dinshi yayi da waya kakawo man 2milyan yanxu ok sir
ai Nafi mutuwar tsaye tayi 2 milyan to itaxaiba koko tsaye kawai take amma xuciyarta taruga wani wuri zata iyacewa duk karuwancinta bata taba rike koda 1milyan ba amma yau gata harda 2
ba afi 3mnt ba yashigo dauke da kudin ahannunshi amsar jikar haisham yayi gashi baby kiyi manaiji kamin nadawo inkuma bakisan wannan kinfisan kifiddo da kanki to kifada man
girgixa Kai tashigayi uwa kadan garu murmushi yayi mata kana yajuya yatafi dan yaga tamkar batasan inda take ba
itakuma tayi shirune domin tasan inhar tabude baki to ihu zata saki dan tsananin murna to bataso tabada kantane
Ansholly
ðŸ˜BAKAR IZAYAðŸ˜
53_54
😘Ansholly😘
*wannan page nakini Aisha*
kd
haisham ne xaune shida mahaifiyarshi kasha hanya dan nan dayake baka safe take fadin sunanshi ba
murmushi yayi haba hajiya wace hanya ga mutuman da yaxo ajirgi
duk da hakanan akwai gajiya yanzu katashi kaje kadan watsa ruwa kana kaci abincin
to yace mata dan yanasan hajiyar tashi ganin yadda take tattalinshi tamkar karamin yaro dayazo wurinta jiyake duk wata damuwarshi takau
yana shiga bedroom din wani kamshi yadakeshi yasan aikin hajiyarshi ne wani tausayinta yaji tabbas inba uwaba bawanda zaima haka dan yasan ita tagyara dakin dakanta tunda tasan bayasan na house girl
cire kayanshi yayi yafada bathroom
Nafi tanajin qarar fitar motarsu haisham tabuga wani irin ihu nafarin ciki da gudu Dr bashir suka shigo palon dama suna kusa da wurin dan tunda sukaji alamar haisham yatafi suka fito daga cikin gidan
tana ganinsu tarungume Dr bashir yayana mafarkina ya kusa zama gaske kaduba kaga irin kyautar da haisham yayi man alokaci daya to inama ga abu yayi nisa
nandai sukaita murna Nafi ce tai mgn aiyau akwai party dan dolene achashe
dole kudi suyi kuka sadi taba hannu suka tafa
shidai Dr bashir yana xaune yana kallansu yayana yanaga kai shuru ina tunanin wani abune Nafi
bai kamata ataba kudin nanba gwara kitashi mubi hanyar kauyanku yanxu dan mugaya gidanku yake kinsan tunda bawani gidan kirki bane ko qyaure babu ballantana yyanxu
wannan kudin chan yakamata suyi kuka banan ba kinsan matsayin haisham kodashi baiga aibun gidanba tunda yana sanki wasufa zasu gani yakamata muje mugaya gidan yake kana
amma inkinga shawar batayiba shikenan
tashi tayi da sauri haba yayana wanama irin shawararka batayiba tabbas kakawo shawara mai amfani kawai tashi muje
bawani bata lokaci suka dauki hanya bayan tayi amfani da mgnin da boka yabata
muntoci kadanne yakaisu cikin kauyan dan bawani nisa daga cikin gari zuwa kauyan
yadda gidan yake haka yake saima kara lalacewar dayayi
shiga cikin gidan sukai itada sadi sai wani irin warinne ketashi tamkar ba mutane aciki sadice takalli Nafi anya nafi akwai mutane cikin gidan nan jibafa kiga gidan duk kazanta aini wallahi ko yawo bana iya hadawa
Nafi tajuyo zatai mata mgn sbd tadanji haushin abinda sadi tace kamin tace wani abu wata mata tafito daga cikin wani daki wanda yake bara xanar xubewa koda yaushe
kuyi haquri yarannan ina sallah ne shiyasa kukajini shiro kushigo maraba banku
wani kallan tsana nafi takebin matar dashi wai yanxunan wannan itace mahaifiyarta
ya yinda ita kuma taga yan burni sai washe baki take wata yalolowar tabarma tadauko tashim fida masu ga dukkan alamu bata gane kosuwaye ba
kallanta Nafi tayi cikin tsana dan tanaganin tabada ita gaban qawarta yadda sadi take bata girma duk da ta girmeta amma tasan yau girman yazube dan taga yadda takema gidan kallan raini
wai Abu baki gane niba ne sai wata qerma kike dan haka take kiranta tunda da sauri wadda aka kirada Abu tajuyo danko da cikin bacci taji murya Nafisa dole taganeta tasan yanxuma abinda yasa bata gane taba farin dataga tayi mata
baccin tasan diyarta bakace Nafisa kece kika koma haka tamkar baturiya zo kuzauna nabaku ruwa kusha
a'a Abu bazamu iya shan ruwa acikin wannan gidanba kidauko hijabinki kizo mutafi gidan kawu kema bazaki kara shigowa ba harsai angyara gidan
to kawai tace domin wata irin shakkar nafin taji tanaji
koda sukaje gidan kawunta ba wanda yachanxa mata fuska ko yanuna abinda tai bata kyautaba murna ma suke nantake cemasu mgnr auranta ne yataso kana take gaya masu matsayin wanda zata aura
karkuso kuga yanda kawu habu kewashe baki shida matansh
ita kanta tasan wannan nasarar tata tana daga cikin aikin boka
shi kuma Dr bashir yakoma cikin gari dan dauko wa inda xasu fara ginin gidan
*Ansholly*
ðŸ˜BAKAR IZAYAðŸ˜
55_56
😘Ansholly😘
*page nakune duniyar hausa novels*
tsawarda bokanya tasace yasa dan uwale kuka wata tsawar takuma dakawa kutashi kuban wuri konasa ya'yan aljannu sutsotse ma yarannan jini da gudu uwale tafito daga bukkar
ya yinda yalwa tatsaya bata haquri daqyal tasamu tasauko domin da tace baxatayi aikin ba
sai chan yalwa tafito daga cikin bukkar da sauri uwale tayi wurinta yalwa yaya tayarda kotace tafasa aikin
hmm nasamu daqyal ta amince kema uwale kincika sauri tunda kikaji tace haka aikinsan akwai abinda tahango
muje gida saina fada maki abinda tace to kawai uwale tace dan jikinta haryanxu rawa yake
suna isa gidan yalwa uwale tasunce goyan mai kudi inajinki yalwa dan nazaqu najimi bokanya tace maki
kallan uwale tayi kedai aradu kincika azabarbiri naji nidai kifada man
ke uwale Ashe hainan dinnan dakike gani mai kudice
hade fuska tayi wani irin maikudi haba yalwa banasan wasa fa mitake sayarwa dazata samu kudin
hmm uwale ke kinada Matsala baki iya cin ribar zance ba mutum yana cikin mgn zaki katseshi
kiyi haquri kawata aimaganarce najita wata iri
kinsan da duk rugarnan ba wanda yakai mlm amadu yawan rakumma sadda yana raye
gyada kai uwale tayi dan batasu tayi mgn yalwa tace takatseta duk da tamanta waye mlm amadun
to lokacin dayaji yan uwanshi na maganar zasu kasheshi to lakacin ne nandai tacigaba daba uwale lbrn abinda yafaru
kana tace abinkichan da bokanya tayi kagano wannan mutine da mlm amadu yaba kudin yana gab daxuwa rugar nan kuma yanxu kudin sun ninka nada sauba adadi dan da abashi juyasu yaitayi
shiyasa tayanke nanda wata bakwai xa akashe hainan dan lokacin yayi daidai da xuwan mutuman kinga dole yaba ubanta kudin yaqara gaba
tafawa sukai kana uwale tatashi tana rawa kai Allah ngd ma kice nakusa zama hajiya uwale da gaske dai yarona saiya xama mai kudin dana keso
kallan banza yalwa tayi mata uwale kenan dake sai danki kikasani koki tunada yalwa
haba aminiyar arziki taya zan manta dake dukfa inda kikaji uwale to dole kiji yalwa nandai taitayi mata dadin baki harta sauko
amma ita uwale axuciyarta tayi alqawarin indai harta samu kudinnan tagama abuta da yalwa ai ita sai matan ardo suma saita daddaga masu kai
nandai suka zauna sunata lbrn yadda zata kasance in kudin sunzo
hainance kwance tsakar gidansu sai murkuso sowa takeyi tadafe cikinta tunda tagama aikin datake ciwan ciki keda munta jitake tamkar zata mutu tagala baita sosai
wata kyaikyawar mata naga tashigo cikin gidan sallama tayi daqyal hainan tadago kanta ta amsa
gani tayi matar tayo kants da sauri tatashi zaune duk da yadda cikin natake mata ciwo gaiyar da ita tayi cikin siriri yar muryarta
kana tace innar bata nan murmushi matar tayi mata ina innar taki tajene kamin tabata amsa cikinta yawani murda dafe cikintayi da sauri
matar ta matso kusa da ita mike damunki da hannu tanuna mata cikinta bata tsaya wani bata lokaci ba tadauki hainan din tamkar tadauki baby takaita bayi
hainan dai kallanta kawai take dan takasa mata mgn abun mamaki suna shiga bayin hainan taga ruwa ajiye ga dukan alamu yanxu aka ajiyesu towa yakawo su itada tasan
bakowa cikin gidan ita kadaice kallan matar tayi ita kuma taimata murmushi
kana tafara cire mata kaya cire wandanki bata musa mataba domin jitake matar tayi mata kwarjini
jinin data gani ajikin wandan nata yasata dagowa araxane takalli matar
nima arazane naqara leka pant din badai hainan anxama manya ba Anty mamie cetace bata isabane shekara12 ace bata isa tafara on ba Lol
tam fans komi uwale xatace intaji Hainan angirma ba mashin shini
Ansholly
ðŸ˜BAKAR IZAYAðŸ˜
59_60
*this page is for member of ansholly novels I love y all*😘
😘ANSHOLLY😘
kuka tasa ya yinda matar batace mata komiba ta ammashi pant din gefe daya ta ajeshi kana taci gaba dayi mata wankan volum din kukanta taqara
dan ita gani take kawai takusa mutu tunda har jini yake zubo mata tanan tasan jininta ne zaiqare shikenan tamutu
wani kukan tasa matar tadago takalleta mikikema kuka hainan ko wankan ne bakiso girgixa kanta tayi alamar aa
to miye yasaki kuka kallan matar tayi da idanta wanda suka sauya launi dan kukan datake
cikin kukan tace ba mutuwa zanyi ba yanxu tunda jini nafita tajikina
murmushi matar tayi wayace maki zaki mutu hainan shiru tayi
wata maganar taqara yimata to bakiso kimutu ne eh tace
sbd mi ke bakiso kimutu
nima inaso naga babana yana daukata yana man wasa kamar yadda baffa keyima mai kudi aikinga baffa yaceshi va babana bane
takalli matar toke kinsan babana din inkin sanshi kikaini wurinshi shima yayi wasa dani kuma bazan kara zowa wurinsu baffa ba
kwalla matar tashare dan tausayin hainan taji sosai
kiyi shiru hainan kibar kuka kinji bazaki mutuba tashi mifita daga bayin nan saina fada maki komi kike
suna fitowa hainan taga wasu kaya aje kusada kayanta kallan matar tayi amma batace komiba
saida tagamayi mata shafa wanda hainan batasan daga ina aka samu kayan sshafarba
kana tace mata jeki dauko wa incen kayan kisa ba musu tatashi tadauko
masha Allah kawai matar take fadi dan wani masifafan kyau tayi tamkar yar India Mira danfodio ce tasaki baki tana kallanta
saida nata bata haba Mira harda jilalan yawu LOL taga kyakkawar yarinya
saban pant tadauko zo zauna kiga yadda zanyi pad tadauko tasa apant din kinga yadda nayi daga mata kai tayi mika mata sauran pad din tayi jeki ajeta cikin kayanki kidawo kiboyeta sosai
wajan kayanta tatafi wanda kala biyune kacal ganin ba inda xatasa aqi gani yasa matar kiranta
kawo nan na ajiye maki da kaina mika mata tayi to zauna
zama tayi itadai babu uhm bare aa kallan matar kawai take amma taji dadin yadda take mata dan tunda tatashi ba mutuman daya taba rabarta kamar haka shiyasa take taimata ladabi dan kartace bata da kunya kamar yadda uwale kecemata
kallanta tayi hainan ya cikin yabar ciwo eh tace mata murya chanciki
nasan kinaso kiji koni wacece to nidai nan nake makwabtanku gida na ukku dagowa hainan tayi takalleta
indai gidan datace ne aitasan kangone yazube tuntuni kuma ko dazun data wuce taganshi yadda yake haka yake
murmushi matar tayi kina tunanin yaushe aka gyara gidan ko gyada kai tayi
to dana mai kudine sosai shiyasa aka ginaman dasauri kuma ginin cikin burni yasha bam ban dananan muchan inza ayi gidan kawai ake daukowa asa awurin
nandai taitaba hainan lbr dan tanaso tasaba da ita sosai kana tai mata bayanin komi game da on din data fara
saida aka kusan kiran sallah magarib kana tamiqe zata tafi bari natafi ya'ta naga uwale takusa dawo wa duk da baki tambayi sunana ba
sunkuyar da kanta tayi alamar kunya kana cikin siririyar muryarta tace kiyi hqr
ba komi 'yata sunana halimatu sadiya amma ke inaso kikirani da mama kinji ko dan allah baibani ya' mace ba kuma anjima inkin fito zaki rafi kibiyo tagidana kinaji
eh mama dagani taji dadin sunan data kirata dashi kamin sukuma wata mgn uwale tashigo ko sallama babu
da sauri hainan takalli inda matar take saidai bata gantaba bata waniji tsoroba dan tadauka tana kallan uwale ita kuma tafi wani banxan kallo uwale tabi hainan dashi
saidai bayarda zatai da ita ubanwa nene yabaki wa innan kayan jikin ki cikin rawar murya tafara mgn inna watace taban
wata matsiyaci duk cikin rugar nan bamai irin kayan nan ballantana kice kwance aka baki kici rosu konazo nai maki dukan tsiya shegiyar yarinya mai irida aljannu
kokarin cire kayan take amma takasa tana dan juyawa ne uwale ta hango sawun jini garigar
wata uwar ashar tasa wace tafirgita hainan mixan gani haka zonan dan ubanki saikin gaya man
*Ansholly*
ðŸ˜BAKAR IZAYAðŸ˜
60_61
*this page is for member for Arewa hausa*
😘ANSHOLLY😘
haisham ne xaune shida Nafi sai wani kanai nayeshi take
sallam akayi aka shigo palon da sauri haisham yatura nafi daga jikinshi dan yayar hajiya maryam ce tashigo
amsa salamar yayi kishigo hajiya wata uwar harara da nafi tayi mashine yasashi yinshiru
kamarya tashigo ciki ita batasan taga mata d miji nazaune ba takoma saita wani shigo kai kuma harda tureni
wani kallo tabi hajiya fadila dashi kana tabuga wani uban tsaki mutum yagirma amma baisan ya girma ba
ke baki ganin lokacine tunda sassafe zaki shigo mana adaki inda kinzo kintadda mu awani halifa kai wanda yagirma baisan yagirma ba anyi asara
daga kai hajiya fadila tayi takalli agogo yanxu wurin 12pm dama abinda yasa tashigo suna san suta fine gashi sunjishi shiru baizo ba da Ameen zata aiko sai bata ganshi ba shine ita tazo da kanta
kallanta tamaida wurin haisham dantaji wane mataki zai dauka
matarshi yariqo yanata bata haquri tamkar xaiyi kuka
juyawa tayi tafice daga palon dan bata taba tunanin haisham zaiyi hakaba ita atunaninta zaitashine yayima Nafi tas kuma yafada mata ko ita wacece wurinshi
komawa tayi dakin da aka saukeso jiki asanyayi nanfa suka fara tambayarta ina angon
karya taimasu nacewa tundazo akace yabar gidan wai wani aikine yataso mashi nagaggawa
sundai jitane kawai amma basu yarda ba inshi yatafi to ina matarshi ita baza tazo sugaisa ba nandai suka gama shiri suka dauki hanyar kd
akabar amarya da angonta yayinda haisham yakejin wani tsoranta azuciyarshi dan yanaji zai iya batawa dakowa akanta
dan koda mahaifiyarshi takirashi tanuna mashi bacin ranta kan abinda yayi chaye ai laifin hajiya fadilar ne dan ita tashigo masu tunda safe kamar yace shibazai jeba
tunda yafadi haka hajiya maryam takashe waya dan tasan haisham baya cikin hankalinshi wanda baitaba yi mata musuba amma yau gashi harda gaya mata mgn akan yar uwarta
koda tagayama alhaji hamza baice komiba addu'a yace kawai susashi dan sai da yakoma kauyansu nafin dan hankalinshi yakasa kwanciya da abinda tsohon nan yafada mashi
aiko yana komawa yayi binkice saiso saiga gaskiya tafito to lakaci yariga daya qore har andaura aure shiyasa yayi haquri kawai yaci gaba dayi mashi addu,a
yanxu dai haisham da Nafi suna cikin wata3 amma haryanxu baije ganin gida ba wanda da bai iya sati1 baijeba
amma yau gashi har wata3 babushi babu lbrn shi dan ko waya aka kirashi