Showing 45001 words to 46793 words out of 46793 words
Chapter 16 - DINYAR MAKAHO Book 1 Complete Document by Ummu Maheer Miss Green txt
arabian gown,wacce tayi masifar yimin kyau ɗaya daga cikin wacce Ammi ta bani ne wato matar ya sheik.
Mu biyu aka bari afalon,Ahmad sai kallona yake wai na yi kyau sosai kamar an canja ni.
Sai dai kawai inyi murmushi,sosai Ahmad ya yi murna da sosai da samun lafiyar Umma,anan ne ma yake faɗamin wai har ya kai gaisuwa gidanmu,Babana ya ce wai sai an saka rana awajen.dom haka yanzu an saka ranar aurenmu da Ahmad wata biyar masu zuwa.
Sosai na dinga yi masa shagwaɓa har da kuka na,wai ni ban girma ba har yanzu ina 15 ban ƙarasa 16 bama.shi kuwa sai murmushi yake don shagwaɓa ta tana burgesa sosai.
*****
*Yarima Yaxeed*
. . . . . .ƙwana biyu kenan Fareeda ba ta nan,kuma bata gaya masa inda taje ɗin ba ya yi mamaki sosai don sai da ta yini ma da tafiya sannan ya san cewa ba ta nan ɗin,bayan da ya kunna CC camera ɗinsa ta gidan duka anan ne ya tabbatar da ce wa,Fareeda ba ta gidan abin ya basa mamaki sosai ya tambayi gate man suka ce masa ai ta fita da troley ɗinta tunda safe bayan ya fita.
Ya dawo kawai yana tunani to ko ta koma India ne?haka dai ya gama tunaninsa azuciyarsa ma ya ce ai gwara ta koma cen ɗin,don shi dai sam Fareeda bata cikin ransa ma don har mantawa ma yake da ɓurɓushinta.
Yana dawowa ya zauna a falo.daga shi sai doguwar rigar bacci pijamas,yana shan coffie yana kallon world news.
Ƙarar bell yaji kamar kada ya tashi sai kuma ya tashi,yana buɗewa ya tarar da ƙannensa Twins Afra da Afreen.
Afra ce me dauriya ta ƙarasa ta rungumesa tana ce wa"Bro munyi fushi da kai ko kaje ka taro mu".
Yaji daɗin zuwan ƙannensa sosai ya yi missing ɗinsu,amman saboda kada ya nuna hakan sai ya tsuke fuska,ga kuma kunyar kayan da ke jikinsa don shi arayuwarsa baya son takura ko kaɗan,ta surutu ko kuma ta yawan mutane,ya fi son yayi rayuwarsa privite babu me takura masa.
shigewarsa ɗaki ya yi,Afreen ta ce"you see ke ƴar shisshigi kinsan fa ce wa Bro baya son irin wannan amman kika wani rungumesa yanzu ai gashinan".
Afrah ta ce"to ina ruwanki?tsakanina da bro babu me shiga tsakaninmu,ƴar baƙin ciki kawai don kinga yafi sona akanki."
ɗan faɗansu suka fara wanda suka saba,ga troley ɗinsa na gefe suna ta cacar baki har Dai prince ya fito.
Tsawa ya daka musu yana ce wa"hyyyyyy!Parrot,ku yi min shiru shiyasa na ce wa Ammi kada kuzo min shine ta ce kunyi hankali ashe har yanzu kuna nan da halin Animal".
Sosai suka kama kawunansu,ya kallesu ya ce"zan tafi aiki za a kawo muku abinci".
Ya faɗi hakan a taƙaice ta fice ya barsu,ai yana fita ma suka cigaba da diramarsu abin dariya.
Ƙarshe kuma suka shirya abinsu kamar ma basu taɓa faɗa ba.
Da aka kawo musu abincin ƙin ci sukayi,sai suka tashi suka shiga kitchen suka dudduba kayan da yake madafar kusan aƙwai komai.
Tuni suka fara girkinsu,don ko da suna america su suke girkinsu da kansu,kuma wani girkin ma Ammi ke turo musu ta waya idan ta dafawa Mahaifinsu wato Sarki Abdussalam,da kanta take masa girki ba ƴan aiki take sakawa ba,kamar yadda wasu matan ke yi sai dai su saka ɗan aiki ya yi musu.
Shiyasa xa kaga wata matar babu abinda ta iya sai barci da son holewa,daga nan sai kiji me aiki ta yi wuf da megida.🫣
To ta fannin girki dai su Twins sun ƙware saboda mahaifiyarsu duk da basu wajenta bata barsu haka ba.
Suna girkin ma faɗansu sukeyi,ya daɗe da dawowa ya tsaya yana kallonsu kawai,idan yana ganin ƴan uwansa sai yaga kamar Ammi yake gani,yana masifar son ƙannensa sosai yana kuma son hira dasu amman shi sam baya son yawan magana ko wani surutu.
*GIDAN SARAUTA POV*
. . . . . . .Sarki Abdussalam ne ke xagaye a babban falonsa,kansa ya ɗauki mugun zafin da bai taɓayi ba,yana masifar son yaga ɗansa tilo akusa dashi,amman hakan ya faskara gashi masarautarsa na son ɗaukaka fiye da sauran masarauta,amman rashin ɗa namiji akusa dashi yana cutarsa sosai,don harkokinsa da dama yana son yaga ɗansa tun yana da rai ya koyi wasu abubuwan ammsn hakan ya faskara.
Bayan wannan kuma gashi takaddar da yake nema ya sameta aɗakin Sarauniya Xulaiha,sakamakon zazzaɓin da tayi jiya yaje sashenta duba ta to anan ne ya yi katari da wannan takaddar.
Sosai hankalinsa ya tashi,don ya yi mamakin samun hakan ta ɓangaren macen daya fi so yafi ƙauna,amman haka ta faru daga gare ta?tabbas ya yi mamakin hakan.
Yana cikin wannan halin sai ga Kilishi ta shigo cikin takunta na isa da taƙama,ta gaishesa sannan ta samu waje ta zauna da yake ranar ƙwananta ne.
Mace da wayo da dabara har sai da ta gano abinda ke damunsa,Sarki Abdussalam ya ƙara da ce wa"ina masifar son ganin Yarima akusa dani,amman na rasa me ƙasar France suke mai wanda mu bama yi masa.?"
Kilishi ta ɗanyi murmushi mugunta,amman bata bari ya gani ba ta ce"Hmm ni yanzu Me martaba idan nayi magana sai ya zama kamar na ɓata maka ne,ammsn maganar dana keso inyi ita kaɗaice za ta kawo warakar komai".
Ɗan kallonta Sarki ya yi don yana buƙatar shawara ayanzu,ya ce"uhm ina jinki Kilishi".
Ni daman abinda nake gani kawai shine ayi masa aure,ga ƴar ƙanwata Nasibat na sonshi,ga ƴar gidan Turaki ƙaninka duk suna sonshi me zai hana duk a haɗasu a aura masa,kaga duk abinsa idan yaga anyi masa aure har mata biyu dole ya dawo nan abadan".
"Good ideas gaskiya Kilishi kin kawo shawara."
Ya faɗi hakan yana ɗan shafa ƙwantaccen sajensa.
🫣🤫Ni Umma maher Yarima da mata biyu?anya kuwa xai yarda?to menens makomar Fareeda kuma?Uhm lallai aƙwai chaƙwalin chaƙwakiya nan gaba.
*Bayan sati ɗaya*
Noor pov
. . . . . .muna sauka a filin jirgi na dinga kallon ƙasata,na ɗan lumshe idanuwa na ina bin ko ina na airport ɗin,ina ɗan ƙwance kan kafaɗar Umma na ina kallonta,ina mamaki har yanzu ta yadda akayi Umma na ta samu lafiya?alokacin da zamu tafi tana abin tausayi yanzu kuma ta zama abar kallo,abar sha'awa don yadda tayi ƴar ƙiba ta murmure.
Ahmad na gefenmu yana kallona yana kashemin ido ɗaya,ɗan murmushi nayi ina ce wa Umma"kin ganshi ko"?.
Murmushi Umma tayi duk kunya ta isheta,tayi gaba ta barmu abaya.
Muna ƙarasowa na hango Hajiyar Ahmad da Umma suna rungume juna,na ƙarasa nima ina gaida Hajiya ta amsa tana murmushi tana sanyamin albarka.
Xaliha kuwa na gefe tana kallona irin kallon ƙasan nan,sai dai wannan kallon na yau daban yake da rannan don kallon mamaki take yimin da ƙasan idonta,ina tunanin ko ganin canjawar danayi ne yasa take yimin wannan kallon oho.?
Baki ɗaya suka rakomu gida,ko da muka shigo cikin gidan duk suna tsakar gida,Safara'u na ƙofar gida tana zance sosai abin ya bani mamaki don ganin wani lalataccen da suke tsaya dashi,wandonsa trea quater ga gashin nan har da kitso hmm rashin tarbiyya dai ƙarara.
Ko da mukazo wucewa binmu sukayi da kallo,musamman ma lalataccen saurayin Safara'u inda ya bini da ficificin idanuwansa yana kallo na kamar zai ɗakkoni.
Inna Saude kusan suman tsaye tayi tana kallon da mamaki sosai akan fuskarta,ita kuwa Inna Hafsatu sai ga ta har da kukanta wai Umma ta yafe mata.
Ranar Inna Saude har da zazzaɓi sai da tayi,mahaifina baya nan yayi tafiya ashe bayan tafiyarmu yaje ƙasar Niger ƙasarsa ta haihuwa,ƴan uwansa da mahaifansa duk suna cen.
*********
Ahmad bayan ya koma gida ya wuce wajen aiki don yana son ƙarasa wasu ayyukansa da bai ƙarasa.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Abinda Ahmad ya ce alokacin da yaga Noor da wasu mugayen ɗamammun kaya,ta yi ƙwalliya me tafiyar da hankali akan kyakkyawar fuskarta.
Tana ɗan zuƙar tabar sigari,tana rike da hannun wani saurayi fari kyakkyawa.
Kanta ko ɗanƙwali babu,kyakkyawan lallaisan gashinta awaje.
Tuni hankalin Ahmad ya yi mummunan tashi,idanuwansa sukayi wani irin mugun jajir tamkar an sanya garwashi acikinsu,wutar kishi na azalzalarsa ya kasa fitowa daga cikin motar sai jan zuciya ya ke,ya yinda yake jin wani sashe na zuciyarsa na masa zugi da ciwo,ya dafe saitin zuciyar tashi ƙwaƙwalwarsa cike da mamakin wannan abinda idaniyarsa ta gane masa.
Wai Noor ɗinsa ce haka?tare da wani ƙato?.
Da sauri ya ciro wayarsa ya fara ɗaukarsu hoto a irin motion ɗinda suke.
Ya ajje wayar yana gyara packing ɗin motarsa zai fito.
Ai sai yaga sai tashin ƙurar motarsu fuuuuu. . . . . .✍🏿
*******
Ya sayyadi bai san mun dawo ba,kai tsaye ya wuce gidansu Hadiza wai don yaji ko tana waya da ƙawarta?don yana masifar son jin muryar Noor.fushin da yayi da ita ƙwana biyu sai yaji wani irin mugun sonta da ƙaunarta duk ya shigesa,ga wani irin mugun haushin Ahmad da yake ji don gani yake tamkar Ahmad ɗin na son rabasa da muradin ransa wato Noor.
A ƙofar gidansu ya tsaya amman bai samu damar ƙarasawa ciki ba,gashi ya rasa yaron da zai tura don ma wani sa'in yana shiga gidansu Hadizan don yana koyawa ƙannenta karatu.
Don haka ya shiga a hankali sallama ɗauke a bakinsa,da yake ɗakin Hadiza na farko ya ɗsn hango hasken fitila,amman sai yake jiyo wani irin abu kamar ƙara ƙara kaɗan.
Sosai tsoro ya bayyana akan fuskarsa,ƙaddara na cewa ya buɗe aƙwai abinda ke faruwa.
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.
Abinda ya ganine yasa shi yin gefe yana kiran sunan Allah,kansa na masa wani irin mugun juyawa hajijiya na son ɗibarsa. . . . . . .✍🏿
Hmm ikon Allah kome ya sayyadi ya gani oho?sai dai da alama abin ya girgiza ƙwaƙwalwarsa har da ta masu karatu.
Hmm cigaban duk sai a littafi na biyu,shin Yarima zai yarda ya auri mata har uku?
'Hmm shin Ahmad Noor ya gani ko ba ita bace?
'Shin waye Al'amin ɗin da ya koyawa Fatima shaye shaye?meye makomar rayuwarta?.
shin Ya sayyadi me ya gani?
amsoshinku duk suna littafi na biyu,ku biyo alƙalamina ni Ummu maher ta yadda zan ja alƙalamina wajen rubuta dukkanin amsoshinku.
Wannan littafin ya faru a gaske,don haka babu abinda na canja sai sunaye.
Kina son acigaba da wannan tafiyar dake?kuma ki amshi littafinki complete kina iya biyan kuɗinki tun yanzu naira ɗari uku kacal don more cigaba da karanta wannan daddaɗan littafin na wa.ga hanyar biyan kuɗin👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻💓
*Ga tsarin yanda biyan yake*
_Guda d'aya 300_
_Guda biyu 500_
_Guda Ukku 700_
_Guda hudu 800_
_Guda Biyar 1k_
Kai tsaye zaku iya turo kuɗinku ta wannan hanya.
0037219728
FATIMA RABIU SUNUSI
StanbicIBTC BANK
Shaidar biya ta nan
0810 433 5144
Masu turo kati MTN ta wannan number.
0702 616 6536
Ƴan Niger zaku turo da naku kai tsaye ta wanna number.
0706 860 6171
Mun gode da kasancewa da gawurtattu biyar taku na biyu.
_Ummu Maheer_
*DINYAR MAKAHO*
_Miss Hajo_
*KHADIJATUL SABREEN*
_Mrs Bukhari_
*ANGULU DAKAN ZABO*
_Ummu Affan_
*SANDAR MAKAUNIYA*
_Mom Islam_
*TSAUTSAYIN TAUNA*
Miss green ce🫵🏾✍🏿🍀💓