Showing 12001 words to 15000 words out of 46793 words
Chapter 5 - DINYAR MAKAHO Book 1 Complete Document by Ummu Maheer Miss Green txt
ƙe ta,shi kuwa sako tumaki ɓallo jakar tuni yayo waje yana ta kumfar baki.
Acen ɓangaren kuwa Inna Saude na fita,Hajiyar Ahmad ta miƙawa Inna Hafsa Naira dubu biyar lakadan ba ajalan ba,murna kamar ta kashe Inna Hafsa,don duk sana'ar da take yanzu babu ko jarin arziƙi,ga yaranta aƙalla yanzu sunkai goma,gana Saude ma guda sha ɗaya gidan dai su ashirin da biyu kenan a lissafe.
Gashi daɗin daɗawa an mata kyauta Inna Saude bata nan,tasan yau babu zaman lafiya acikin gidan amman duk da haka ko ajikinta,sai taga dama zata kulata don babu wanda ta rainawa hankali kamar Saude don faɗanta yawanci ihu bayan hari ne.
Ana cikin haka sai ga mahaifin Noor ya shigo,suka ƙara gaisawa da Umma abin mamaki sai Baba ya kasa yi mata rashin mutunci kamar yadda ya gama faɗa,Inna saude sai kallon hannun Inna Hafsa take,ganin ƴan dubu dubu bugun Abuja a hannunta,a take taji wani irin mashi me tsini ya soki zuciyarta,kar dai ace ƴar fitar nan tata ne aka yiwa wannan munafukar kyauta?.indai kuwa haka ne wallahi ko da ba'a bata ba,sai ta saka masifar da zata saka a bata itama.
Mahaifin Noor ya amince,umma taje don ta zauna da ƴarta duk dama ba wani abu za tayi mata ba,tunda duka jiki ya shanye fuskarta ce kawai bata taɓu ba.don idan kaji muryarta ma sai ka ɗauka lafiyarta ƙlau.
Hajiya da Hadixa su suka kama Umma har suka saka ta a cikin mota,sannan Hadiza ta tsaya awajenta cikin zuciyar Hadiza tana tuna yadda zasu wanye da Inna Lami don tasan halinta,ita bama mahaifinta ne aranta ba,don tasan sai abinda Inna Lami ta faɗa shi yake yi.
Shima mahaifin Noor Hajiya ta bashi kuɗi dubu goma.
Inna Saude fa hankalinta ya tashi ganin har yanzu ba'a sallame ta ba,sai ta shiga dabarar yadda zatayi ta tsokani Inna hafsa don suyi cece kuce don a bata itama don taga ruwa yana so ya ƙare wa ɗan kada.
Don taga tana shirin tashi babu ko ƙwabo,ƙarshe kishiyarta Hafsatu tayi mata dariya.
Wafce kuɗin hannun Ina Hafsatu Inna Saude ta yi,tana haki ta fara cewa"wallahi Hafsatu baki isa ki cinye kuɗin nan ke kaɗai ba,tunda daman da ta bamu ce wa tayi mu raba amman saboda tsabar son zuciya irin taki,shine kika karɓe wai ke me tsinannan wayo".
Sosai abin ya ƙular da Inna Hafsatu,ta ce"ke Saude ki fita daga cikin idona in rufe wallahi akan kuɗin nan idan ban miki tsinannan duka ba,kice ni ba ƴar gidan Malam jatau bace sai inyi miki lilis anan."
Dariya ma abin yaso ya bawa Hajiyar Ahmad,ganin duk haɗin kan da taga sunayi kuɗi zai shiga tsakaninsu,ashe daman zaman ba na Allah bane.
Ta ciro dubu biyar ɗin ta miƙawa Inna Hafsa sannan ta ce"ke ki riƙe waccen ɗin,ita kuma na bata wani don haka sai ku zauna lafiya,kuma ina yi muku Nasiha da kubi halin wannan ƴar uwarku taku,duk da tana buƙatar kuɗi amman basu tsone mata i'do ba,don haka kuyi koyi da ɗabi'arta don mutuniyar arziƙice."
Tana faɗar hakan tayi fitowarta daga gidan,tana mamakin hali irin nasu Inna Hafsa da Inna Saude.
Inna Saude ta yiwa Inna Hafsa gwalo sannan ta ce"oho dai koma menene hausawa sunce 'ƊINYAR MAKAHO'(ta nuna ahannusa,don da ba'abani kuɗin nan ba da anga masifa ƙwando ƙwando.
Ya sayyadi ya ƙaraso inda suke akan lifan ɗinsa,yake gaya musu yaje don ya shaidawa mahaifiyarsa abinda ke faruwa don kada aga ya daɗe.
Sannan Umma ta nemi da aje gidansu Hadiza a faɗa don babu daɗi aji shiru,kuma gata budurwa baya ga haka ma yarinyar tana cikin wani hali agidansu,don ansha rabata da Noor amman kuma sai kaga gobe ma ta koma.
*GIDAN SARAUTA*
............Gidane ƙato wanda ya yi matuƙar tsaruwa,su kansu bayin gidan sarki Abdussalam shigarsu ta dabance,gidane wanda yasha fenti fari ɓangare huɗu ne agidan basu da fenti fari,kowanne fentinsa daban ɓangarorine masu matuƙar kyau da ban sha'awa.
Idan ka garzaya fadar sarki kuwa,dukiyace aka narka ba kaɗanba idan ka shiga ɗakin baza kaso fitowa ba,saboda yadda tsarin wajen yake tafiya da mutane da dama.
Sarki Abdussalam shine mahaifin Yarima Yazeed ɗan kyakkyawan saurayi,Sarki yana masifar son Yazeed don bashi da ɗa namiji wanda ya wuce shi,duk ƴaƴansa mata ne yana da matansa har huɗu amman uku daga cikinsu duk mata suka haifa,shiyasa ya ke masifar son Yarima Yazeed tun yana ƙarami baya nuna masa fushi koda kuwa ya yi abin fushinne,idan kuwa aka taɓa Yazeed ko kai waye to daga ranar kun ɓata,ko da kuwa mahaifiyarsa ce to yanzu zaka ga sun samu matsala.
Sarauniya Zulaihat ta ɓangaren mijinta bata samun matsalar komai,amman akan Yarima Yazeed yanzu zakaga sun samu matsala,aƙwai wani duka da ta taɓa yiwa Yazeed ɗin,abinka da mara ƙwari har bakinsa sai da ya fashe daya ke yana da masifar rashin ji yana ɗan ƙaraminsa,ga ɓarna kuma baya ganin kowa da daraja saboda ƙaunar da mahaifinsa ya ke nuna masa da kuma shagwaɓasa da ya ke yi.
Wannan abu da Sarauniya Xulaihat tayi,ai ba ɗan ƙaramin yaƙi akayi agidan ba sai da sukayi kusan wata ɗaya basa ga maciji,don ko ɗakinsa taje sai kaga yana wani cin magani ya ƙi koda kallonta ma,kuma Sarki aduk cikin matansa yana masifar son Zulaihat,kuma kowa ya sani harda abokan zamanta.
Wannan faɗan da sukayi sai ya zamanto hatta kishiyoyinta suna goranta mata akan wannan,ashe ɗanta na sonta sai gashi shine ya sasanta su tunda alokacin ya kai kusan shekara goma,don Yazeed tun yana ƙarami Allah ya yi masa kaifin basira da shegen wayo don duk abinda ka ke sai dai ya kalle ka kawai.
Tub daga kan wannan faɗa da sukayi,Sarki ya nemi shawarar Sarauniya Zulaihat akan a fitar da Yazeed ƙasar waje don ya cika burinsa na zama me tsara gine gine,a farkon farawa bata yarda ba saboda lalacewar tarbiyya wacce ayanzu ɗama yana gabanka ya ka cika balle kuma yana wata uwa duniya?amman ganin mahaifin ya dage yasa tabi ɗanta da addu'ah kawai.
Ganin kamar ran matarsa tasa baiso ba,sai ya haɗasu su uku yakai ƙasar waje.
Aƙwai ɗan ƙaninsa Muhammad Turaki,aƙwai kuma ɗan wazirinshi shi me suna Aliyu duk sai ya haɗasu ya kaisu,sai dai kowa aƙwai abinda yake karanta,shi Muhammad ɗan gisan saraki yana karantar law ne wato lauya,shi kuma Aliyu fannin likita ya ke karantawa,shi kuma Yazeed fannin tsara gine-gine.
Farkon fara karatunsa lafiya suka fara ba suda wata matsala,sai daga baya komai ya canja don farko awaje ɗaya suke ƙwana a wani gari me suna Le mains dake ƙasar France.
Sai abokai suka shiga jansu zuwa gidan Club,farkon farawa Yazeed bai bi ta kansu ba sai ya ɗaukesu tamkar wasu shashu.
Makarantarsu aƙwai wata yarinya ƴar asalin ƙasar india ce me suna Roshni ta na cewa Yazeed sosai duk alokacin bai fi shekara ashirin ba,akanshi yarinyar nan har hawa bene ta yi tace zata faɗo wai idan baice yana sonta ba,Yazeed mutum ne me matuƙar tausayi,don haka ya yarda yace kuma yana sonta amman ba har cikin zuciyarsa ba,don shi arayuwarsa babu ne yi masa tilas ɗin duk abinda baya so,mutum ne tsayayya da in har yaga abu yace yana so to ya soshi kenan har abadan abadan,idan kuma yaƙi abu to yaƙi shi kenan har abada.
Sosai Roshni taji daɗin abinda masoyinta ya ce,sai ta ƙara zurfafa sosai acikin kogin sonshi,sai ta tsira shiga gidansu gashi duk mutanen gidan basa nan,tunda wataran idan su Aliyu suka tafi yawon Club ɗinsu sai sukai ɗayan dare,basu dawo ba saboda haka yasan daman sun saba sai baya damuwa dai dai ya ɗakko littatafansa ya duba daga nan ya kira iyayensa susha hirarsu ta ɗa da mahaifansa.
To mafarin ƙaddarar Yazeed ita ce Roshni,don Roshni tayi ta ƙoƙarin son su aikata abinda bai kamata ba,amman daya ke tsayayya ne bata samu wannan damar ba,sai ta tsiri zuwa gidansu wai don tayi musu girki,Yazeed ya kyaleta kawai ya saka mata idanuwa don yaga iya gudun ruwanta.
Da wannan girkinne ta samu ta ƙara shiga zuciyar Yazeed,sai dai fa har yanzu bata samu abinda take so ba daga nan sai ta fara ƙwaɗaita masa shan giya,nan ma bata samu abinda takeso ba.
Daga nan Roshni ta tafi hutu ƙasar India,Roshni mahaifinta wani babban boka ne a ƙasar India daga ƙasashe ma da dama ana zuwa wajensa.
Don haka sai Roshni tayi amfani da wannan damar ta faɗawa mahaifinta wai wani saurayi takeso shi kuma baya sonta,me abu da abinsa nan da nan ya fara aiki kan Yazeed,sai dai fa ya yi mamaki sosai don ganin wannan yaron iyayensa sun tashi sosai aransa.
Sai aka saka masa son zuwa club,daga nan ita kuma sai ta samu abinda take so.
Hmm tsafi gaskiyar meshi,don tun kafin Roshni ta dawo Yazeed ya fara bin yawon Club Club,abin ya bawa su Aliyu mamaki sosai.
Yazeed ɗin da suka sani me matuƙar tsantseni da rayuwarsa,sai gashi shi kuma yanzu ya damesu sosai shi da ya ke musu nasiha sai gashi yanzu shine harda ƙwana?abin ya ɗaure musu kai sosai.
Roshni na dawowa aka ɗora inda aka tsaya,don Roshni ta samu yadda take so sai dai kuma haƙarta na cin ruwa su Yazeed suka koma gida,don suma sun samu hutun skull,kuma ayanzu ma sun kusa gamawa.
Roshni tana masifar son Yazeed,har ciwo tayi lokacin da Yazeed ya tafi ciwon da farko ƙaramine amman daga baya sai ya zama babba,daga hawan jini sai ya komai ciwon zuciya.
Aka aikawa iyayenta,akazo aka tafi da ita ƙasar India cen ma suka rasa yadda zasuyi da ita,don baki ɗaya hankalinta yana kan Yazeed,abinda yafi bata tsoro ma shine bai wuce yadda Yazeed ya manta da i'ta ba,don ya yi mata alƙawarin idan har ya koma Nigeria zai neme ta da sabon layinsa,amman sai taji shiru tamkar malam ya ci shirwa.
A wannan hutun dasu Yazeed suka dawo,Sarauniya Zulaihat ta lura sosai da sabbin halayen ɗanta Yazeed,sai ta saka masa idanu sosai,amman daya ke Yazeed ɗin yana da wayo sosai sai yaƙi bata damar gane waɗansu abubuwan,haka ya lulluɓe ta daga bisani dai da taga kamar tana zarginsa ne sai ta kyalesa,ta cigaba da yi masa addu'o'i.
Alhmdh yanzu Yazeed ajikinsa ya ke jin,tamkar ya zalunci iyayensa idan har ya cigaba da aikata ɓarna don haka sai ya daina wasu abubuwan,kamar shan giya da sauran wasu abubuwan waɗanda ya ke yinsu a ɓoye waɗanda ba kowa ne ya sani ba,Sai Aliyu da Muhammad sune suka san halin miskilancin Yazeed.
To bayan komawarsu makaranta hankalinsu baki ɗaya yana kan exam(jarabawa)wacce ta yi zafi sosai don duk abinsu basa wasa da jarrabawa suna tsayawa suyi karatu sosai.
Roshni ma ta dawo makaranta,ta nemi su koma yadda suke ada amman gogan ya nuna mata babu wannan zancen,ranta ya ɓaci sosai amman sai ta ɓoye sai ta shiga kyautata masa sosai.
Duk ɗan adam yana son me kyautata masa,daga haka sai ya fara kulata amman wani abu na banza baya shiga tsakaninsu,ta nemi shawararsa tana son ta musulunta amman bata san yadda za tayi ba?.
Sai ya bata shawara akan ta sanar da iyayenta,sai ta gaya masa ce wa idan har suka sani to bazasu barta ba,sai dai ta musulunta a ɓoye daga baya sai ta gaya musu.
Roshni ta musulunta,don aƙwai wani malami wanda Yazeed ɗin ke ɗaukar karatu awajensa wanda ke ƙasar France ɗin,cikin ikon Allah ya musuluntar da ita wanda ya tambaye ta wani suna takeso ta ce Farida.
To wannan musuluntar da Roshni tayi sai ya ƙara mata wani irin girma awajen Yarima Yazeed,kai hatta matsalar ciwon zuciyarta shine ya tsaya mata tsayin daka har ta samu lafiya.
Sai suka cigaba da soyayyarsu.
Wannan shine taƙaitaccen tarihin Yazeed.
*Noor Pov*
...........Lokacin da su Umma sukaje gidansu Hadiza,mahaifinta baya nan sai Inna Lami wacce ke irga wasu kuɗaɗen da ta siyarda gidanta,da ya ke su Lami gidansu suna da kuɗi sosai,kuma mahaifinsu ya bar musu dukiya sosai.
Tana jin shigowar mutane da sauri ta danne kuɗinta,idanuwanta sukayi jawur tayi wuri wuri da ficificin idanuwanta.
Da Sallama su Hajiya suka shiga,bayan sun Gaisa Inna Lami ke ta kallon ƙadan zanin Hajiyar Ahmad,don ganin irin atamfar da ta saka.
Hajiyar Ahmad tana ɗagowa suka haɗa idanu da Inna Lami,da sauri Inna Lami ta juya ta waske kamar ma ba ita ce ta yi wannan kallon rainin hankalin ba.
Hajiyar Ahmad ta yi murmushi,don ta saba haɗuwa da irin waɗannan matan masu masifar sa ido ga dukkanin kayan daka saka.
Inna Lami kuwa azuciyarta ce wa take"Caɓɓijan yau Allah ya haɗani da Hajiya?irin wannan tsadaddiyar atamfa haka?don atamfar da Hajiyar Ahmad ta saka ko ba'a gaya maka ba kasan ke tsada ce,balle kuma Inna Lami wacce tasan atamfofi sosai don tana siyarwa kuma tasan duk kuɗaɗensu tunda tana siyarwa da manyan mata.
Hajiyar Ahmad ta nisa sannan ta fara magana kamar haka:
"Hajiya daman nazo ne don tambayar izininku?akan daɗewa da Hadiza ta yi bata dawo gida ba,don Allah kuyi haƙuri a faɗawa Babanta cewar ƙawarta ce bayan sun dawo daga makaranta ta yi hatsari wato Noor,shine abinda yada ta daɗe don haka don Allah kuyi haƙuri".
Inna Lami ta ce"a haba babu komai Hajiya,a'i nasan yadda suke da Noor Allah dai ya bata lafiya,babu komai ta ɗebi kayanta ma ku tafi tare asibitin sai ta zauna da Noor ɗin,tunda dai ita mahaifiyar Noor ɗin ga shi tana fama da lalura,don haka ku tafi babu komai idan Babanta ya dawo za'a gaya masa."
Sosai Hadiza ta yi mamakin Inna Lami,don tasan halinta sarai masifa da kuma hantara da zagi,duk babu wanda bata yi mata dai gashi yau wai ita ce da wannan daɗin bakin.
Ko da zasu tafi Hajiyar Ahmad ta ajjewa Inna Lami kuɗi akusa da i'ta,da sauri ta saka hannu ta amshe kuɗin tana washe baki tare da yi wa Hajiyar Ahmad ɗin godiya,sai ga Inna Lami da rakiya har soro tana ta washe baki,kamar wadda aka yiwa albishir da gidan aljanna.
Abin sai yaso ya bawa Hadixa dariya ta maze kawai amman mamaki ya cika zuciyarta,sarai Hadiza ta san Inna Lami da masifar son kuɗi,Inna Lami babu abinda baza ta iya akan kuɗi ba,masoyiyar kuɗi ce sosai duk kuwa da yawan kuɗin da take dasu amman na hannunta basu isashe taba na hannun wani take kallo.
Kai tsaye asibitin muka koma,Ya sayyadi ma kasa tafiya gida ya yi,shima ya biyo mu don ya ce bazai tafi ba har sai Noor ta tashi,kana ganinsa kasan yana cikin tashin hankali don sai yanzu yasan me yake ji akan Noor.
Ahmad kuwa har yanzu kallon Noor ya ke,har likitan ya dawo ya sameshi ya yi dariya sannan ya ce"a'ah mutumina har yanxu gadi ka ke?na ɗauka ma ka tafi gida,ashe har yanzu kana nan kana gadin gimbiya."?
Murmushi Ahmad ya yi sannan ya ce"Hmm to ai ya zamarmin dole inyi gadi,saboda duk wannan jinyar ni na janyo ta,kaga kuwa dole inyi ni tunani ma kada ta tashi ta kama jin haushi na,don wallahi yarinyar tayi masifar ƙwantamin don ina ji ajikina kamar zata yarda dani ɗari bisa ɗari".
Murmushi Dr Zain ya yi sannan ya ce"haba Ahmad daga buge mutum kuma sai ka zarce"?..
Suna cikin wannan maganar sukaji sallamar su Hajiya,Umman Noor suka ƙwantar da ita akusa da gadon dake kusa dana Noor.
hawaye ne ya shiga ƙwaranyowa aƙwarmin idanuwan Umma,ta hangi ƴarta wacce ke ƙwance rai a hannun Allah,tamkar babu numfashi ga wajen karayar da ta samu har an ɗora ta.
Ahmad sai kallon Umma ya ke,duk da Noor bata yi kama da ummanta ba amman ta ɗakko waɗansu kamannin na ta,don Umman Noor ba fara bace ita ba fara ba ita ba baƙa ba,wankan tarwaɗa kenan Ita kuma Noor kama tayi sosai da mahaifinta fara ce sosai amman ba fari ɗau ɗinnan ba,wai a hakan ma don fatar tata bata samu kular da take buƙata ba.
Hajiyar Ahmad ta ce"My son wannan ita ce mahaifiyar Noor,tana fama ne da stroke mun nemi da tabarshi ta xauna ta huta,amman kadan ɗa da uwa sai Allah shiyasa tazo don ta ganta,sai Hadiza ta zauna dasu don mun nemi izinin iyayenta sunce ta zauna."
Har gaban Umma Ahmad yaje ya tsugunna ya ce"Umma ina wuni"?.
A hankali ta juyo da fuakarta tana kallon Ahmad.
Sai dai tana kallonsa cikin tsoro ta ce"kai ne"?... . . . .✍🏿
@@Miss green ce✍🏿🍀.
_Ummu Maheer_
*DINYAR MAKAHO*
_Miss Hajo_
*KHADIJATUL SABREEN*
_Mrs Bukhari_
*ANGULU DAKAN ZABO*
_Ummu Affan_
*SANDAR MAKAUNIYA*
_Mom Islam_
*TSAUTSAYIN TAUNA*
*Ga tsarin yanda biyan yake*
_Guda d'aya 300_
_Guda biyu 500_
_Guda Ukku 700_
_Guda hudu 800_
_Guda Biyar 1k_
Kai tsaye zaku iya turo kuɗinku ta wannan hanya.
0037219728
FATIMA RABIU SUNUSI
StanbicIBTC BANK
Shaidar biya ta nan
0810 433 5144
Masu turo kati MTN ta wannan number.
0702 616 6536
Ƴan Niger zaku turo da naku kai tsaye ta wanna number.
0706 860 6171
Mun gode da kasancewa da gawurtattu biyar taku na biyu.
*TALLAH*
Ina kuke amare uwayen gida kai har ma da ƴan mata? Ko kun san Mrs Bukhari mai kayan ƙamshi, ai in dai batu na kayan ƙamshi gyaran jiki da na ɗaki to kai tsaye ku ne mi Badi'at domin gwana ce ta ko wanne fanni a ciki. "Wai ƙamshi kina nufin Badi'at dai marubuciyar nan tamu mai nishaɗantar da mu?"
"Tabbas Fati ita take magana, ai kin dai ji yadda ake magana a kai na, hatta me gidana ya jinjinawa Badi'at domin duk wani ƙamshi da zaki ji a jikina tare da gidana to daga ita ne, ke me kankat ma har gyara na nake yi domin gyaran aurena daga gareta ne, shi ya sa bana wasa da gyaran jikina da na gidana har kuke kirana da ƙamshi."
"Eh tabbas nima na jinjina mata, kuma zaki bani addireshinta domin nima na kwankwati wannan garaɓasa. Ko zaki iya faɗa mini abubuwan da take sayarwa.?"
"Bari na faɗa miki akwai...
Humra
Kulacca
Sudanese Humra
Kulacca ta gashi.
Turaren wuta ɗan gaske, iri daban daban.
Turaren mopping
Room freshner
Turaren turara kaya.
Turaren wuta na toilet
Sannan akwai ingantaccen maganin infection
Ina da magungunan mata, wanda zai gyara amarya da uwar gida.
Wanda zasu shiga daga ciki kuma
Akwai sabulun amare, da dilka ta amare, wanda zaisa amarya ta fito ta haska tas
Kabbasa
Setin kujerar tsugunno
Sannan inayin turaren wuta da kasko, da ashana wanda ake rabawa a taron biki ko suna.
Ina bayar