Showing 81001 words to 84000 words out of 97223 words
Chapter 28 - JUHUD BY OUM HAIRAN .txt
Meenah tace “to kinji dai sai kiyi takatsantsan koda wasa kada ki yarda su baki kisha wadannan mutanen babu Allah a ransu.
Jinjina kai tayi sukayi sallama ta tafi sashinta ta kwantaTunaninta Yana bata to da me Addah Abulle ta shiryawa cikinta da Mom ta ganota?" Tabe baki tayi ta juya baya suna chat da Ya'isha taji an turo qofar da sallama ta tashi ta zauna tare da amsawa Amrah ce ta shigo tayi mata murmushi itakam tsayawa tayi sororo tana kallonta ta nemi guri ta zauna tare da cewa Aunty Meenah Ina yini" fuzgo numfashi tayi tare sauke ajiyar zuciya tanajin abin wani bambarakwai wai namiji da suna Fatsum bata gama wannan tunanin ba taji Amrah tace.
“Abubuwa da dama sun faru da suka sanyani nadama tabbas ita gsky duk inda take sunanta gaskiya lkcn da labari ya isheni cewa kedin yar yayar Mom ce jikina yayi mugun sanyi kunya ta lullubeni a lkcn da Mom ta dawo take sanar da Mai Martaba cewar kece akwai yayarta data dade tana nema a 9ja tabi rugage ds dama domin gano inda zata sameta hakan ya faskara ta tabbatar bayan dogon bincike d ruwan da akakai Rana baffaninki da sukazo suka sanar damu kedin Mayyace sun kwatanta mata inda zata same kakanki harma da bata tsoffin hotunan Kati guda biyu na kakarki wacce ta haifi mahaifinki Aminatuh wadda kikaci sunanta da Kuma na mahaifiyarki, a jikin wannan hoton ne ta fara fuskntar wani abu"
Shiru Amrah tayi kana ta dago ta kama hannun Meenah tace “ganin kamanni da yanayi na jininta jikin wadannan hotuna yasata bin duk wata hanya ta roqi alfarmar wadannan baudaddun Fulani su rakata inda zata samo miki danginki ke Saida ta hada musu da qaryar cewa kin cinye mata yayanta biyu ne jin ba abin arziqine zai kaita ba yasasu yarjemata Amma da sharadin zata biyasu ladan bata lkc hakan kuwa akayi suka dunguma ta biya musu kudin jirgi sai Senegal ga mamakin Mom sai taga sun nufi gidan sarkin birnin da suka sauka Wanda yake kakane a gurinta shine ya haifi mahaifinta itadai bata tofa ba har suka isa ciki sunata karbar gaisuwa suka Isa sashin kakarta wadda itace uwargida a gidan ta tsufa sosai tana ganinta tace “yar qaniya ashe kina tunawa da mutane" nandanan labarin isowarta ya cika gdan ta sallami Manga ya tafi masauki bayan anci ansha an huta komai ya lafa mom ta fito da hotunan nan ta miqawa Attajiri Dodda ya karba Yana ganin dayan ya tashi zaune yace “Aminatuh Aishatu Ina kika samo hoton babarki Aminatuh?" Hawaye ne ya zubo masa yace “Aminatuh ta mutu tun baa haifeku ba dama su biyu ns Haifa daga mahaifinki Garbu sai Aminatuh naso riqe dan Aminatuh wato Haruna Amma Ina sun hanani banason zumunci ya mutu na sake Basu auren Aishatu yayarki nidai tun daga auren nan ban sake sanin labarinta ba sunbar inda nasansu sun hanata nemanmu duk da hakan shi Haro yakan kawo mamu ziyara daga baya kuma mukajishi shiru shima bayan yan watanni na tashi yaje ya ganomin ko qalau Haro shekara uku an tafi hudu baizo ya ganni ba shima mukaji lbrn mutuwarsa nayi kukan rashin Haro, babban tashin hankalin sun sake tashi a inda mukasansu Babu Indo Babu dalilinta babu yarsu guda daya tun daga lkcn na baza koma ta a Nigeria neman wannan yarinya saboda naji lbrn baqin fentin da akayi masu ta dalilin kakarta data haifi uwarta Hamida sun zama abin tsangwama ababen kyara wai ana musu kallon mayu"........
Dakatawa tayi ta dago ta zubawa Juhud da jikinta keta rawa ido tace tana Shirin mgn ta miqe da mugun gudu ta nufi cikin gdan Kareem dake nufo sashin ya rufa mata baya tana shiga ta fada jikin Mom ta qanqameta ta rushe da kuka me sauti Mom ta dora hannunta akanta tana Shirin mgn Meenah tace “Ashe kin nemomin asalina Mom kikaqi fadamin kika barni cikin zullumin tunanin ta Ina zan fara nemansu Mom meyesa kikeson boyemin duk abinda ya kamata na sani"
Murmushi Mom tayi tace “wato Dana Hana a fada miki Saida aka samu Wanda ya gumtsa miki Meenah tawa yata ta kaina Ni dama bantaba jinki daban da jinina ba kiyi hqr bawai na boye miki don banaso ki sani bane aa na boye miki ne don inason idan kin haihu sai kisan komai na daukeki nakaiki har Senegal da Mali kiga dangin mahaifiyarki ke yar gata ce mu goma ne gurin mahaifinmu biyu sun mutu mahaifiyarki Indo da Abdulrasheed babbanmu Wanda shine yasa mukasa sunan yayanki dan'uwanki Rasheed yanzu saura mu takwas maza hudu mata hudu zakiga kowa zakisan kowa Kakarki mahaifiyar Ummanki Kumbo Hami tace tana tafe cikin satin nan zatazo tayi aikinta tamayi na gayyar sodi balle me dalili".......
Sosai yinin ranar Juhud ta yini da damuwa me gauraye da farin ciki yanzu hankalinta ya tattaru guri daya a baya Baffa'am dinta sunan mataimaki ya Amsa a gareta ya rasa mahadi ya rasa madadi yanzu Kuma matsayinsa ya nunku yayanta ne dan qanwar babarta shin meye sakayyar daya dace tayima wadannan mutane?" Ta rasa mafita ta rasa mahanga amfanin abokin shawara kenan yanzu da ace tanada mashawarci da ya bata mafita.
Yini tayi tana safa da marwa a falonta zuciyarta tayi baqi Rasheed kawai ke haskata shine keyi mata yawo a cikinta shaidan Yana raya mata abubuwa da yawa saidai tayi a'uziyya ta kawar da tunanin kawai da haka Kareem ya shigo ya sameta da kula a hannunsa ya zubanta ido yayi murmushi yace “duk kinbi kin takura kanki kwana biyun nan akan abinda baki isa canzashi ba am bama wannan ba wainar fulawa naga Fadila nayi nace Bari na taho miki da ita" zama tayi don tun shigarta da taji Fadilan na cewa tanason yin wainar taji tanaso nutsuwa ta kasa samu da tuni tayi aikuwa ta bude kular sai tiriri takeyi ta mangyada taji lawashin albasa da attaruhu ta hadiyi yawu ta gutsura zatakai bakinta tayi Bismillah kenan taji an tankwabe hannunta tana dagawa taga Amrah cikin hawaye tace “Karka barta taci wannan wainar sun zubanta guba ne don su kashe dan dake cikinta Ya Kareem nayi tunanin lkcn da Addah ta tabbatar da cewa Meenah ba mayyah bace zata sauko ta dawo hanya Amma abin mamaki sai naga dawa ta qara shiga su Hajiya Bilki da Dada Hanne suna zugata, Ya Kareem meye ribarsu idan sun kashe dan dake cikin Meenah sunada tabbacin zaka qara samun wani ne kaida Meenah waye yafi asara tunda ita ko ba komai tanada Sarki junior kaifah?" Tunda ta fara mgnr gumi ke karyowa Kareem tana kaiwa nan bata Ida rufe bakinta ba taji an daki hancinta Addah Abulle tana huci tace “shegiya munafuka nayi danasanin Bari Mom ta shayar dake dana sani Madara na dura miki qila da bakiyi sakaryar zuciyar nan ba ni dama nasan haka zata faru to bari kaji na riga na tsani Meenah tun daga lkcn da tabarka ta auri Rasheed bakuma zan taba sonta ba ban qaunarta ban qaunar jininta Abdulkareem zabi biyu zan baka kodai ka saki Meenah ko Kuma ka dawo da Zahrah idan kaki zabar daya cikin biyun nan zan dagsnka nono nabarka da duniya da macen daka zaba akaina ka gani idan zaka qare qalau kanadai kallon yanda qarshen Rasheed ya qare daya zabeta yabar uwarsa da ubansa shima da takeso kenan bakai dan karere ba da ake maleji dakai a rashin uwa akai uwar daki dakai".................
Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank
Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...
Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....
*Oum Hairan*
[8/16, 8:25 PM] Oum Hairan: Tunda ta fara mgnr Juhud ta zubanta ido tana murmushi har Saida ta ida kaiwa qarshe sannan ta tabe baki tace “dama zabi daki kika bashi na rabuwa dani da yafi muku Alkhairi dukkanku dama neman gaba nakeyi banji a Raina zan iya rayuwa ta har abada da danki ba saboda haka ki kwantar da hankalinki saura kadan lkc yazo....." Daganta hannu yayi da qaraji yace “Meenah ya isheki haka" dubansa tayi tayi murmushi tace “akanme zan shiga hankalina bayan nasan cewa ko nayi shiru din ba gwani zanyi ba Kareem nagaji da rashin mutuncin danginka wlh bazan dauka su doramin ciwo a banza ba...." Daga hannu yayi zai mareta ta riqe hannunsa tana murmushi tace “karka soma wlh ramawa zanyi" ji tayi an dauketa da mari ta dafe gurin tare da dagowa Mom tagani hawaye ya zubo mata tace “akan wannan mutumin zaki mareni Mom na rantse da Allah na gaji Mom nagaji ni nagaji...." Riqeta Mom tayi ta jata suka shiga ciki ta zaunar da ita tace “bana tunanin haka daga gareki Ina hqrnki yafara tafiya ne Meenah komai fah na duniyar nan lkc garesa don Allah kici gaba da kawar dakai akan lamarin gdannan huccewa zaiyi kamar baayi ba" haka Mom ta rinqa bata baki hardai taga ta russuna tace “ga rubutun an kawo miki" karba tayi tayi Bismillah ta shanye Mom taja numfashi tace “ki huta Rasheed ne yaje yacemin Yazo gurin qawarsa Kareem ya hanashi shiga" gdy tayima Mom ta tafi itakuma ta zauna tana tunanin Wannan rayuwa tata idan nan ta kau sai nan ta bulle tabbas akwai aiki a gabanta.
Har goman dare Kareem bai nemeta ba itama bata nemesa ba haka suka kwana washegari ya fice tun kafin ta tashi itama data gama abinda takeyi tayi tafiyarta sashin Mom wajen la'asar Kumbo Hami ta iso tana zuwa ta rungume Juhud tana kuka me tsuma zuciya tana shafa kanta tana cewa “tun ranar dana fara ganinki naji Ina qaunarki a jinina ashe kedin jinina ce kaicon rashin sani Meenah Ina tare da jinin Aysho bansani ba Ina tare da gudar jikata bansani ba Allah na gde maka daka nunamin wannan Rana duk da banga Aisha ba naji sanyi a Raina domin naga jininta" itama kukan takeyi tana qara shigewa jikin kakarta yau gata gata cikin gata gata ga kakarta data haifi uwarta sun jima suna kukan tuntunin kafin su samu nutsuwa suka balle sabuwar hira wasa² batabar sashin Mom ba sai taran dare data shiga bata isheshi a falo ba tayi shigewarta dakinta domin yanzu ba shine a gabanta ba mafita ta gaba take nema.
Sun shafe ya kusa kwana biyar suna kallon kallo ita dashi shi a izza irin tasa jira yake ta nemesa tabasa hqr ita Kuma tunaninta baima bata laifi tayi ba balle taji a ranta zata iya nemansa ta wani basa hqr, lura yayi da batama fahimci abinda yake nufi ba hakan yasashi dole ya nufi dakinta ya tarar da ita ta kwanta ya zauna a gefen gadon Yana shaqar iskar dakin data hade da qamshin turarensa yace “wato ke ban isa kiyimin laifi kibani hqr ba ko?" Tanajinsa tayi masa banza yasan tajisa hakan yasa yaci gaba da cewa koma meye Addah zatayi miki bata cancanci fada ki fada ba domin kinsan bazanji dadi ba Amma wai kece zaki tsaya gaban mahaifiyata tana fada kina fada"
Yunqurawa tayi ta tashi zaune ta zubansa ido yanata maganganunsa tana kallonsa qurrr har ya gama tunaninsa zatayi mgn sai yaga ta gyara kwanciyarta taja bargo tace “idan ka gama ka rufemin qofar" kallonta yayi da sauri Yana mamakin qeqashewar zuciyarta cikin dan qanqanin lkc tabbas Meenah akwai abinda take nufi a zuciyarta shiyasa takeyi masa wannan iskancin a zuciye ya tashi ya fice daga dakin yaja mata qofar da qarfi ta diro daga gadon ta sanyawa qofar key ta koma ta kwanta ashe yanzu wasan ya fara daga wannan gabadaya ya fita a harkarta idan ya shigo gdan bai nemanta idan zai fitama saidai taji fitarsa abun Yana qona masa zuciya itakam ko a jikinta harkar gabanta kawai takeyi da yan'uwanta da kakarta haka lkc ya rinqa tafiya har ubangiji ya kaita gabar haihuwarta ta shima Tasha wahala kafin ta haifo qatuwar yarta mace kyakkyawar gaske.
Wannan haihuwa ta mantar da Kareem abinda ya faru ya rinqa rawar qafa akanta da babyn komai yagani ya kwaso ya kawo musu dake haihuwar dare ce da safe aka sallamesu suka dawo gda wani abin mamaki daya soki zuciyar Kumbo Hami da Mom Addah Abulle da Fadila duka suna gdan Amma babu wanda ya leqo domin ganin mai jegon da diyarta hatta Amrah da Ya'isha da suke waje sunzo Aunty Hamida kuwa da ita suka kwana a asibitin ashe ba iyakar Mom da Kumbo Hami abin yayima ciwo ba Kareem yafi kowa jin ciwon abin aikuwa dif ya daukewa bangaren mahaifiyartasa qafa har akayi kwanaki hudu da haihuwar wannan karon Aliyah da Nana matan Ya Arman da Salman kunya ce ta ishesu irin abubuwan da suka rinqa yima Juhud ita Nana ashe ma Juhud jininta ce kullum dasu ake yini gdan Juhud sai yammaci kowa ya kama gabansa.
Ranar kwana hudun ne ya fita yayo siyayya a mai jego ya dawo Urwat ya tareshi a parking space yake fada masa Addah na nemansa Saida ya shiga yaga babynsa sannan ya dauki hanya ya nufi bangaren Addah Abulle suka gaisa shiru ta ratsa ya dago yace “Urwat yace kinason ganina" dagowa tayi ta kafesa da idanunta kusan 6 minutes tana kallonsa sannan taja numfashi tace “ya mgnr da mukayi dakai? Meye makomar zabin dana baka?"
Gumine ya fara karyo masa ya dago zaiyi mgn ta daga masa hannu tace dakata ba shawara nake baka ba fah umarni ne Kuma ban baka don banasonka ba saidon nema maka mafita jin cewa Mom ta hada kutungwilarta tace Aminatuh yar yayarta ce bazai gamsheni daga abinda dangin ubanta suka fada akanta ba maita yanzu da kudi ma siyanta akeyi saboda haka wlh kaji na rantse a yau saika saki yarinyar nan ruwanka ka dawo da Zahrah ruwanka ka zauna a haka ba damuwata bace, tunda kunce rabo naji rabo Kuma gashinan an haifa saboda haka ayi komai a gama"
Miqewa tayi ta dauko masa biro da takarda ta miqa masa ya kawar dakai a zafafe tace “wlh muddin baka saki Meenah ba saina tsine maka...." “Abdulkareem karbi rubuta mata" muryar Mai Martaba suka jiyo ta bakin qofa ya tako ya shigo ya dubi Addah Abulle yayi murmushi yace “saki nawa kikeso yayi mata?" Shiru tayi tana hura hanci ya dauki biron da takardar ya miqawa Kareem yace “kayi mata abinda takeso hakan zai faranta ranta...." Hawaye ne ya zubo masa ya bude baki zaiyi mgn Mai Martaba ya dagansa hannu yace “kada kace komai kayi" hakanan ya dauki takardar ya rubuta mawa Meenah saki daya" Yana rubutawa Yana hawaye bayan ya gama ya dago ya rushe da kuka jikinsa na rawa yace “don Allah kubarni da matata wlh inasonta" murmushi Mai Martaba yayi yace “tayi biyayya a baya bata taba qin jinina ba ta faranta min itama tana buqatar farantawa Kareem kayi hqr, ke Kuma na juyo gareki daya yayiwa Juhud ke Kuma kije da biyu in an hada uku kenan"........
Dafe qirji tayi cikin tashin hankali tace “nashiga uku Mai Martaba...." Murmushi yayi ya fice yabarta da danta da yake neman ficewa a hayyacinsa har yakai bakin qofar ya tsaya yace “nayi miki hakane domin kina iqirarin kina da haqqi amma banson ki manta nima inada haqqi ga Kareem nan ciwon kai idan yayi ki dauki nauyinsa banida lkc ko kudin da zan kashe abinda kikeso ne anyi miki fine"
Ficewa yayi daidai lkcn da Kareem ya zube a qasa sumamme tayi kansa a guje cikin tashin hankali shikam Mai Martaba yana fita part din Kareem din ya nufa ya ishe Mom tana yima takwararta Ayshatu baby wanka ya zubama jaririyar ido kyakkyawa da ita Masha Allah yayi ajiyar numfashi yace “idan kin gama inason ganinki"
Amsawa tayi da to ya fita Saida ta gama shirya babyn sannan ta kaiwa uwarta ita daki tana kwance tun safe batada walwala hakanan gabanta yake faduwa batasan dalilin ba tun kafin ta haihu rabonta da ganin Rasheed sai jiya takeji a gurin Kumbo Hami wai Yana gurin magani dauke hawaye tayi a fili tace “Allah ya baka lfy Baffa'am" murmushi Mom tayi tace “amin ya Allah Bari naje Mai Martaba yakeson ganina" jinjina kai tayi ta fice itakuma ta dauki yarta tana bata abincinta bayan kamar Awa daya taji Kumbo Hami tana salati tace “saki Kuma Aishatu me yayi zafi haka?" Bataji me Mom tace ba Amma Saida gabanta ya Fadi ta miqe Kumbo ta shigo ta dauki jaririyar tace “aikuwa shima Mai Martaba din bai isaba wlh sai tabar gidannan Mom tanason mgn ta katseta tace “karma kicemin komai idan zaki iya ki nemomin me kaini inda zani" a sanyaye Mom tace “Amma Kumbo magaruba tayi koma me kikeson yi kibarma gobe Mana" murmushi tayi tace “matsiyaci shine yake jira nikam bana jira" da haka ta dubi Meenah data kasa gane komai tace “muje Aminah" mgn takeson yi Kumbo Hami taqi sauraronta ta figi hannunta suka fito suna fitowa taga Muntaz yace “ina Kuma zaku tsohuwa da daren nan" kallonsa tayi tace “yo jiyemin fah dannan wannan Tataccen ne da gantalalliyar uwarsa suka wulaqantamin jiki wai saki a halin jego to debemin albarka gyatuma tayi da zan Bari mukai gobe a gdannan"
Jinjina kai Muntaz yayi yace “Ya Kareem din ne ya saki Meenah Kumbo...." Daquwa ta watsa masa tace “aa tatsunniya nakeyi maka ja'irin yaro zo ka kaini cikin gari akwai wata yar qasarmu mu kwana acan da safe saimu tafi" yasan rikicin Kumbo Hami idan ta fusata hakanan ya debesu da Meenah da taketa matsar hawaye batasan dalili ba sai taji abin yanayi mata yawo a kwanya ta tambayi kanta yafi sau goma ashe Kareem zai iya rabuwa da ita ashe dama duk abinda yake fada mata na ta rayu dashi forever itane zuciyarsa itane rayuwarsa qarya yakeyi mata?
Sosai takejin qunci a zuciyarta batasan zafin saki haka yake da qona zuciya ba hawaye ta rinqa daukewa lkc zuwa lkc har suka Isa unguwar da Kumbo tace akaisu dake tayima