Showing 57001 words to 60000 words out of 204612 words
Chapter 20 - BAKAR INUWA Original Book Complete Document by Billy Abdul .txt
hakan yasa Raudha da mominta samun damar keɓewa da ƴan uwanta. Kuka ta dinga rusa musu akan wlhy bata son auren nan dan mutanen nan sunfi ƙarfinta. Duk da wasu sun nuna soyayyarsu gareta wasu ƙuru-ƙuru a ƙannensa da wata babbar mace da take ƙyautata zaton mahaifiyarsa ce saboda kamanni da suke ɗanyi suka nuna mata tsana da gargaɗi. Nan dai duk ta basu labarin abinda ya faru ranar zaɓen shugaban ƙasa.
Hankalin Asabe ya tashi, ta shiga yima Raudha faɗa akan miyasa ta amsa a wancan karon, dama irin wannan take guje mata tun farko. Maba danginsa ba ko shi bata ƙyautata zaton zai so ta. Mutumin da tun yana ciki ake ajiye masa kuɗi a asusun banki, ya girma yasamu ingantaccen ilimi, babu kalar ƙasar da bai zagaba yaga mata ƙyawawa ƴaƴan manya irinsa, amma tai tunanin zai iya dubanta matsayin mace. Kawai dai kakansa ke son wannan haɗin saboda alkairin datai musu.
Lallashinta su Fatisa suka dingayi da bata baki harma da shawarwari, dan harga ALLAH suma suna son ƴar uwar tasu ta auri shugaban ƙasa. Koba komai zasu fantama matsayin yayyen matar shugaban ƙasa. Zasu huce gajiyar wahalar da sukasha a hutawa a baya.
Sosai Asabe ta kasa zaune ta kasa tsaye, ji take kamar ta gudu da ƴaƴanta daga Bingo. Dama tasan idon Gwaggo idan yaranta sai wanu abu ya biyo baya. Dama wannan taita fargaba tun farko. Tunanin inda zataje da su ne ya sakata sake shiga damuwa. Har aka ɗaura auren aunty Hannah bata da wata walwala. Kowa tunaninsa aunty Hannah zata tare ne acan gidan Alhaji yaro kamar auren farko, sai sukaji saɓanin haka wai anan zata cigaba da zama tukunna. Hankalin Asabe ya sake tashi, dan tasan kuma babu danar sace Raudha kenan.
A ranar dai ko leƙe ango bai leƙo gidan ba, washe gari akai zaɓen gwamnoni. Wannan karon babu inda Raudha taje, hasalima wuni tai murƙususun ciwon mara har sai da suka dangane da asibiti. A asibitin ta kwana, washe gari suka dawo gida. Haka kwanakin suka cigaba da shuɗawa batare da Raudha ta ko sake jin labarin wani Ramadhan ba sai a tv kawai idan an ambaci sunansa ko an nunasa. Sannan Asabe ta kasa samo mafita game da auren na Raudha. Sai da auren aunty Hannah da Alhaji yaro ya cika wata guda cif suka fara ganinsa a gidan. Dan zuwa yanzu an kammala duk wasu zaɓuka sai jiran rantsarwa kuma. A ranar gyaran da ma'aikatan sukaima gidan ma na musamman ne, bai isoba kuma sai wajen tara na dare.
Raudha ta haɗo kan su Yasmin sukazo suka gaishesa. Baki ya saki da hanci yana kallon Raudha ɗin yana haɗiyar yawu. Dan harga ALLAH baisan haka yarinyar take ba. Bai taɓa ganinta ba sai a hoto, sai dai kuma a yanzu canji waje data samu ya sake fiddo mata da ƙyawunta da cikar budurci. Dan tana akan shekarunta ne na girma.
Harga ALLAH Raudha ta tsargu da kallon da tsohon ke mata, dan haka ta shiga ambaton sunayen ALLAH da jifansa da addu'oi. Tunda ta samu ta gudu ɗaki kuwa bata sake leƙo waje ba harda safe. Tanaji Yasmin tazo tana tashinta wai tazo a karya inji sabon Abba tai mata banza. Dole ta koma tace barci take.
Har Alhaji Yaro yace Yasmin ta koma ta tasota Aunty Hannah ta hana cikin kissa. Acewarta a barta tai barcin batajin daɗi, kuma anjima sunada wani trianing akan Raudhan. Badan yasoba dole ya haƙura, sai dai a ransa yana fatan ALLAH yasa kafin yabar gidan ta fito. Sai kuma akai rashin sa'a addu'arsa bata karɓu ba harya fitan batako leƙo waje ba.........✍
*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
_A AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.
*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.
*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.
A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).
--------
Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:
*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*
Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.
*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.
_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*
Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:
Amount Paid: - Nawa aka tura?
Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa
Transferred time: - lokacin da aka turo
Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi
Deposit date: - ranar da aka turo
Sai ayi SUBMIT.
*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:
MTN,
9Mobile
Glo
Airtel
Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Episode 23_*
............A ɓangaren Ramadhan kam yama manta da wani batun aurensa balle Raudha. Harkokin gabansa kawai yakeyi na shirye-shiryen rantsarwa da zaman meeting-meeting da suke yawanyi da ƴan jam'iyya a gidan gwamnati. Shi kansa ma haushi meeting ɗin ke basa a mafi yawan lokaci, dan wasu yakan rasa gane kansu balle inda suka dosa. Sai dai yana nutsuwa dai wajen maida kansa yaron da suke kallonsa yana karantar komai da nanufofinsu.
Sai dai abinda Ramadhan bai sani ba a garesa ne kawai ya manta da abatun aure, ga jama'ar gidansu da masu so da masu ƙi duk abin na ransu. Domin shiri su Anne keyi na musamman akan auren, lefe ya kammala haɗuwa tsaf, hakama abubuwan da duk za'a buƙata ga taron biki.
A ɓangaren su gimbiya Su'adah ma dai suna nan akan bakansu na hana tabbatar wannan aure, sai dai kuma tun randa Pa ya ritsata tana waya da Asma yaji kuma mi suke faɗa yaja mata dogon gargaɗi, tare da alwashin inhar wata matsala ta shigo a auren nan ta shirya amsar matsala a nata auren itama. Wannan ne ya tada mata hankali ya kuma ja mata birki, sai ta koma zungurin Ramadhan akan auren. Sai dai kuma rashin zamansa a gidan ya taimakesa da masifarta.
A yanzun kullum cikin ƙulla yanda zasuci uban Raudha suke inhar ya tabbata sai anyi auren. Tare da ɗaukar alwashin aurama Ramadhan Aina'u koda daga baya ne.
A hutawa ma dai Mal. Dauda ya shirya tsaf, dan gyara na haƙiƙa yayma gidansa tamkar bashi ba. Ya baza ɗinkuna yayma kuma kowa na gidan. A yanzu haka Innarsa da ƙaninsa da iyalinsa suma sun dawo nan gidan da zama. Hakan yasa Larai ta rasa kataɓus dan Inna cin uban surukai take babu ɗaga ƙafa. Balle ma yanzun da take ganin ɗanta yay arziƙi, ai koda wasa babu wanda ya isa zagin Asabe a gabanta duk da bata nan. Takance Asabe ai farar uwa ce tunda gashi sanadin ta haifi Raudha suna hutawa. Takanji takaicin saki ukun da ta saka Mal. Dauda yay ma Asabe a yanzun. Inama ɗaya ne ko biyu da yanzu sai ta dawo abinta.
To anan ma dai shirinsu suke tsaf duk da babu amarya har anko an fitar ma.
*_SATIN BIKI_*
Shiga satin biki ya saka ango da amarya dawowa cikin hankalinsu. Dan kuwa sun tabbatar yanzu kam da gaske ake ƙwarai. Ta ko ina sanar da wannan ɗaurin aure ake a kafafen yaɗa labarai dana yanar gizo, yayinda wasu baƙi dake ƙasashen ƙetare suka fara sauka ciki harda su Sultana daba taron bikinne ya kawotaba kai tsaye. Dan tunda akace Ramadhan ya fito takarar shugabancin ƙasar NAYA take son zuwa, sai kuma ga batun aurensa da yay matuƙar tada hankalinta har takaita da kwanciya asibiti. Halin data shiga yasa Babanta yarda su Mufeed suzo da ita taga Ramadhan ɗin.
Sai dai kuma tun jiya suka iso amma ganin Ramadhan yay musu wahala saboda yana can suna shirye-shiryen zancen rantsarwa. Za'a ɗaura auren ne juma'a, asabar ayi rantsuwa, lahadi su tare gidan gwamnati tilitin shugaban ƙasa ya fara shiga office.
______
Ga amarya kam itama ta yarda dai auren nan babu fashi, tunda aka shiga satin bikin aka sake ninka yanayin gyaran jikinta da akeyi, tayi ƙoƙarin toshe duk wata hanya bata sake haɗuwa da Alhaji yaro glass ba duk da yana yawan zuwa gidan yanzun. Ana saura kwanaki biyu ɗaurin aure daren da washe gari za'a maidata Hutawa kusan sha biyu yunwa ta addabeta, dan duk yinin yau bataci wani abincin kirki ba saboda damuwa. Bata son auren nan ko ɗigo a ranta, gefe ga tsoro da fargabar tsantsar ƙiyayyarta data hanga a cikin idon Gimbiya Su'adah da wasu a ƙannen mijin nata. Jin har kamar zuciyarta na tashi dan yunwa ya sata fito da nufin zuwa kitchen ko tea ta haɗa.
Da sauri taja birki jin kamar ana magana ƙasa-ƙasa dai-dai tana ƙoƙarin sanyo ƙafarta a falon, ta ɗan laɓe tana leƙe daga corridor ɗin ɗakunan barcinsu ita da su Yasmin. Aunty Hannah ta hango da wasu mutane uku, babu wanda ta gane a cikinau sai Alhaji Yaro glass kawai. shima dan rabin jikin aunty Hannah nakan nasane. Dan tana zaune kusan a jikinsa ne ko kunyar sauran mutanen bataji. amma sauran ukun babu wanda ta sani.
Jin an ambaci sunanta yasa gabanta faɗuwa. taɗan sake matsowa daf da hanyar fita corridor ɗin ta kasa kunne taji da ƙyau.
Wanda yake a kujerar ƙarshe mai sanye da jallabiya baƙa ya ƙara fuskantar aunty Hannah yana faɗin, “Hannah kinga dai mun matuƙar yarda da ke, dukkan wani shirinmu a yanzu tamkar ya rataya a wuyanki ne. Bama son kuskure ga yarinyar nan, dan idan aka samu kai tsaye ke zamu ɗaurama alhakin hakan”.
Kanta ta jinjina masa tana tashi zaune sosai. “Alhaji Wada karkaji komai, na riga na ɗaura Raudha bisa kowacce irin hanya da bazata iya bijire mana ba. Ku ɗauka tamkar yaron nan ya mutu ya gama a shekara biyun da kuka ɗeba masa. Adai ɗaura auren jibi, da zarar sun tare za'a fara bata maganin tana saka masa a abinci, ko abin sha kamar yanda first lady ta sanar min..”
“Hakan shine dai-dai, dan munaso ya fara masa aiki a hankali yanda ko bayan mutuwarsa za'a ɗauka diabetis ɗinsa ce ba wani ba, tunda dama maganin zai ƙara ƙarfin diabetis ɗinne ya kuma haifar da hawan jini mai ƙarfi. Sannan a yau da safe duk wani poison an sakashi a cikin ac ɗin falonsa da bedroom dan a hankali mukeso ya fara ratsa jininsa shima ta yanda zai zama bashi da wani kuzarin nutsuwa yay aikin ma, dan cikin idon yaron nan ka kalla kasan bazaiyi mutunci ba. Yana gama gane kan mulkin nan mukanmu ba ɗaga mana ƙafa zaiyiba wlhy.”
Alhaji Yaro glass ya karɓe da faɗin, “Ai dama shegene yaron nan, yanda kaga kakansa da taurin kai haka shima yake. Ni gani nakema mizai hana ita Raudha mu fito mata ƙuru-ƙuru akan aikin da muke son tai mana kawai dan yarinyace sai yanda mukai da ita.”
“A'a wannan ganganci ne, idan kuma aka samu akasi ya faɗa sonta fa? Ko kuma itama tana sonsa yanzu haka? Dan yaron nada qualitys ɗin da mata zasu so sa a ƙanƙanin lokaci. Giyar soyayya kuwa zata iya janta ta sanar masa. Kawai muyi yanda muka tsara ayi amfani da ita”.
Cikin zafin rai Mr MM yace, “Idan ma mun sanar matan tace zata tona mana asiri halakata zamuyi itama a banza....”
“Ai ko yanzu ɗin ba tsira zatai ba. Kana tunanin zata dinga shaƙar gubar nan ta cikin ac ta tsallake itama. Yanda zata dinga masa illa a hankali itama hakanne zata kasance. Sai dai akwai wata allura da za'ai mata wadda gubar bazata yi tasiri a jikinta da wuri ba kamar shi”.
A tare duk suka kalli Aunty Hannah bayan sun ɗauke idonsu ga Dr Bonba daya gama bayanin.
Kanta ta kaɗa musu tana watsa hannaye baya. “Miye na kallon nawa?, kun san dai Raudha ɗiyar ƙanwata ce. Duk da kuwa ina son zama first lady bashike nuna bana son abata ba. Nasan bai wuce kuce ya shawarar ta canja ba game da allurar riga kafin guba. Ku zauna kuyi tunani da hankalinku, babu ta yadda za'ai mu bari gubar tai tasiri a jikinsu lokaci guda, dan komai zai fito ne. Amma idan bayan ya shi ya mutu ne itama ta mutu za'a iya cewa zuciyartace ta buga saboda rashinsa itama tabisa”.
“Woow!”.
Suka faɗa a tare suna tafawa. Shugaban ƙasa mai sauka yace, “Hannah kinada basira, anya kuwa idan mutumina ya zama shugaban ƙasa bake bazaki koma juya ƙasar ba kuwa?”.
Wata shegiyar dariya tayi tana juya idanu, Alhaji Yaro glass ya sake rungumota jikinsa da manna mata kiss a kumatu. “Inaga shugaban ƙasa biyu kam zakuyi”. Ya faɗa cikin raha. A can ƙasan ransa kuwa yana ayyana ashe kuwa itama zata mutu nan kusa, dan Hannah bata isa shiga masa hanci bai fyatota ba duk da take matarsa.........
Zuwa yanzu sosai hajijiya ke neman yadda Raudha a ƙasa. Tai azamar dafe bango jin zata zube a ƙasa. Laɓɓanta sai faman rawa sukeyi amma sun gagara furta komai, dan ko tace zata furta ɗin batasan mi zata furta ba. Da ƙyar ta cigaba da laluben bango ta koma ɗakinta, batasan a yaya ta zube saman gadon ba harda jan bargo ta lulluɓe, jikinta ya shiga wani irin karkarwa na rawar sanyi
Yanzu ta fahimci ba ahalin Ramadhan bane zasu zama BAƘAR INUWAR ta ba, ba Ramadhan bane BAƘAR INUWAR ta ba, aunty Hannah itace BAƘAR INUWAR ta. Shi kansa Ramadhan sun tittiɗashi ya hau kujerar mulki ne badan ya ni'imtu ba, badan ta zame masa INUWA da irinsu talakawa suke hangen masu mulki na ciki ba. bai san sun kaisa BAƘAR INUWA bane, gara ace a rana yake da shiga cikinta. ta sake fashewa da kuka.
ALLAH sarki talaka. A kullum gani yakeyi shi a RANA YAKE, mai mulki shike cikin Ni'imtacciyar inuwa, ashe baisan da wata BAƘAR INUWAR MUKIN gara ranar da shi yake a ciki ba. Yau gashi saboda mulki yayar mahaifiyarta ta ɗauketa da hannunta ta kaita BAƘAR INUWA. Shiyyasa suka dage ashe, shiyyasa suka hana mahaifiyarta nuna ƙin auren, shiyyasa suka babbake ko ina da ina. Miye mafita? Zata bijirema auren ne ta hanyar guduwa ko zata haƙura ta zauna ta ceci rayuwar wanda a yanzu take kallo da fatan ya zama adalin shugaba madubin al'umma kamar yanda talakawa suka ɗora yaƙininsu a kansa da ƙwarin gwiwarsu?.
A take kanta ya fara sarawa, dan tama rasa kalar tunanin da zatayi saboda ƙarancin shekarunta. Ga wani irin tausayin Ramadhan ɗin da ahalinsa na dirar mata a zuciyarta, dan ta taɓajin cewar kakansa Baba alhaji aka bama takarar shi kuma ya bashi saboda yace bai ra'ayin mulki a shekarunsa. Ashe baisan ya kai jikansa BAƘAR INUWA bane. Tabbas bazata iya fahimtar komaiba a yanzu dole saita san komai, sanin komai kuma bazai yuwu a gareta ba sai ta yarda da auren Ramadhan. Sai dai kuma tana buƙatar shawara wajen na sama da ita, wazata tunkara? Hajiyar birini! (Kai a'a gwaggo sai a hankali ce) Hajiya mama (kai itama a'a duk tafiyar ɗaya ce) Mommynsu! (Ina bazai yuwu ba zata sake tada mata hankali) Su Fatisa! (Ina basu da hankalin da zasu iya fahimtarta ta wani fanin ma gara ita). Take wani irin zazzaɓi mai zafi ya rufeta, sarawar da kanta keyi ya ƙara ƙarfi..
Koda suka wayi gari da safe Raudha babu lafiya aunty Hannah bata kawo komai a ranta ba sai tunanin fargabar