Showing 24001 words to 27000 words out of 204612 words
Chapter 9 - BAKAR INUWA Original Book Complete Document by Billy Abdul .txt
binciken yanda rayuwar matarsa da ƴarsa ta salwanta. A cikin wannan halin kuma Anne ta kawo shawarar Ramadhan B. Hameed Taura ya maye gurbin kakansa a kujerar shugaban ƙasa da akai masa tayi. Inda dudu shekarun Ramadhan B. Taura 36 a duniya. Ya rasa iyalansa yanada shekaru 31. Yanada ashirin da bakwai yay aure. A yanzu shekaru 5 cif da faruwar komai kuma.
A hasashe ba'a taɓa samun wani shugaban ƙasa mai adadin shekarunsa na ƙuruciya ba a ƙasar ta *NAYA* ba sam.
★
“Kana nufin dole kenan mu amince da zancen Alhaji Hameed Taura indai muna buƙatar cikar burinmu Your Excellency?”.
Monday Mazier ya faɗa a ɗan hasale.
Shugaban ƙasa da Alhaji yaro glass suka kalli juna suna murmushi mai kama da takaici suma. Yayinda Alhaji Haladu Gwandu ya dafa kafaɗar Monday Mazier ɗin yana faɗin. “Mr MM cool down abeg. Muma duk irin zafin da kakeji munjisa a lokacin daya tabbatar mana ya amsa tayinmu, amma kuma jikansa ne zaiyi bashi ba. Ƙwarai da gaske ya shammacemu, shammata maiban mamaki. Dan yayi hakane dan mu janye buƙatarmu kodan kasancewar jikan nasa yaro, tunda yana ganin ba'a taɓa shugaban ƙasa mai ƙarancin shekarunsa ba a wannan ƙasa ta NAYA. Sai dai kodana zauna nai zari sai banji komai ba, domin Ramadhan baida maraba da hoton bango da kowa zaizo ya kalla ya wuce manne a falo batare daya amfana masa komaiba. Shine surikina da yarinyata ta rasa ranta a dalilinsa, yana can U.S tsahon shekaru biyar tamkar zararre. A ganina wannan damace a garemu mai sauƙi, duk da naji a raina Taura yayi hakane danya dawo da hankalin yaron gida kamar yanda sukaita fata a shekarun baya yaƙi hakan. Amma idan Taura yasan wata ai baisan wataba, Idan muka fitar da yaron matsayin ɗan takara zamu kawo wani sabon abu a ƙasar nan da ba'a taɓa yiba, sannan matasa zasu yarda da gaske muna tare da su. Babu tantama mulki zai cigaba da kasancewa a hannunmu ne”.
“Woow exactly my man”.
Mr MM ya faɗa yana bama Alhaji Haladu Gwandu hannu suka tafa bakinsa washe da dariya tamkar yanda shugaban ƙasa da Alhaji Yaro glass da Alhaji Balarabe Andu keyi suma alamar hankalinsu yaɗan fara dawowa jikinsu.
Alhaji Yaro glass ya gyara zama da faɗin, “Tabbas nima sai yanzu na fahimci manufar Taura na yarda cikin sauƙi, kuma hakan yamin daɗi, dan mu idan bai saniba wata damace ta ɗaukar fansa sau biyu akan abu guda. Ramadhan zai hau mulki na tsahon shekaru biyu kacal, sannan zai mutu sau biyu......”
“Sau biyu kuma?”.
Shugaban ƙasa ya katse Alhaji Yaro glass cikin rashin fahimta.
Alhaji Yaro dake murmushi yace “Ƙwarai kuwa sau biyu, dan dole ne mu ɗauka fansar Amnah data mutu dominsa, sannan mu kashesa adalilin taurin ran kakansa da ubansa. Na farko zai kasance cikin nasararsa da jin daɗin mulki a shekarar farko, a shekara ta biyu zai fara ciwo a dalilin guba da zata zagaya jininsa zuwa ɓargo da jiki. A shekara ta uku muyi bikin mutuwarsa da biznesa vice president ya hau kujera ya shekara biyu biyar cif kenan. Shekar ta ƙarshe a sake sabon zaɓe wannan shine amsar mutuwa biyu”.
Ya ƙare maganar yana ƙyalƙyalewa da dariya, suma sauran suna tayasa kamar wasu zararru. Sai da sukai mai isarsu kafin suyi shiru suka koma shan shayi da cigaba da ƙulla tsiyatakunsu........✍
🤔🤔Hummm wani lokacin ma rasa abun magana ake.
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
__________________
*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*
Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F
*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼
+227 95 16 61 77
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*
https://arewabooks.com/book?id=628103f05798291d0ecedd09
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_Episode 10_*
.............*_WASHE GARI_* shugaban ƙasa yay waya da god father nasu na siyasa dake faɗa aji a ƙasar baki ɗaya, sai dai a siyasance babu mai iya jin sunayensu. Ya sanar musu dukanin tsare-tsarensu. Sosai nasu tsarin yay masa shima harya yaba musu, dan yasan komai sai dai suna bayan fagene, ya kuma tabbatar musu komai zai tafi dai-dai dan Alhaji Hameed Taura a tafin hannunsu yake.
Cikin farin cikin yabon da shugaban ƙasa ya samu yace, “Na gode ranka ya daɗe. ALLAH ya ƙara girma da ɗaukaka. Badan ku ba babu mai ganin koda hotonmu a ƙasar nan. Shiyyasa muke addu'ar tsahon rai a gareku domin muyita cin karenmu babu babbaka”. (Ashe kasan shi mai mutuwane, rayuwarsa mai ƙarewace excellency. Inhar kuwa zai mutu to bai isa amfana maka komaiba face wanda yazo cikin ƙaddarar duk wanda kuka hara. ALLAH ka bamu shugabanni na gari🙏🏻🤦🏻).
Bayan ya gama masa kirari da yabon dake sake buɗa masa kai ya ɗora da bayanin...
“Ranka ya daɗe a yanzu haka mun gama yanke shawarar ganawa da shi yaron kawai muji ta bakinsa shima”.
“Tunani mai ƙyau, sai naji ku”. Daga haka ya yanke wayar. Shugaban ƙasa ya cireta a kunnensa yana jan kakkauran tsaki da ballama wayar harara. Cikin ƙunƙuni yace, “Mugu ƴan hana ruwa gudu, ALLAH dai ya kusa kasheku muma mu babake ko'ina, daga sama har ƙasan ta zama tamu. Dan badan kuba da mune taurarin duniya ta kowanne fanni.”
(Kai jama'a kamar bashi bane ya gama masa ƴar murya yanzun🤣, siyasa shegiya😂).
*_TAURA HOUSE_*
Kamar yanda al'adun ƙasashen da hausawa yake dama musulinci baki ɗaya, irin wannan lokacin ko nace wannan ranar ranakune masu muhimmanci na shirye-shiryen bikin salla. Tamkar kowanne gida dake shiri haka Taura family house ma keyi ƙwansu da kwarkwata. Danko duk ƴammatan gidan zaka gansu da zanen lalle baƙi ko ja. Wasu sunyi kitso wasu gyaran gashi kawai. Hakama matan Alhaji Basheer Hameed Taura babu koma baya dan duk ɗinsu ƴan gayu ne kuma ƴaƴan manya, dan kowacce tana alfahari da irin gidan data fito ne.
Misalin ƙarfe tara na dare da yay dai-dai da sanarwar ganin jinjirin watan shawwal daga bakin mai girma sarkin musulmi ƙararrawar dake sanar da taron meeting na iya manyan gidan ta kaɗa. Ba sabon abu bane hakan a duk daren kowacce salla, sai dai a wannan karon taron meeting ɗin yazo da banbanci. Sakamakon manyan gidan kawai ake buƙata banda yara.
Cikin tunani da taraddadin lafiya duka matan Alhaji Basheer Hameed Taura suka kimtsa kawunansu zuwa sashen surukan nasu domin amsa kira. Sai tsoffi guda biyu da suka kasance ƙanne ga Alhaji Hameed Taura da suma suke zaune a gidan a halin yanzun. Sai ƙanin Alhaji Hameed Taura ɗin autansu da ya iso da iyalansa daga ƙasar Dubai a daren jiya domin halartar bikin salla da sukanzo a kowacce shekara...
Duk wani wanda ake buƙatar gani a katafaren falon na alfarma da an tsarasane kawai domin gudar da meeting na ahalin gidan ya iso. Kowa ka gani zaune yake cikin mutuntawa ga dattijo Alhaji Hameed Taura da matarsa Anne. Dan dukan matan Alhaji Basheer kansu a ƙasa yake kasancewar suna gaban surukai.
Bayan an buɗe taro da addu'a Alhaji Hameed Taura da ahalin gidan ke kira da suna Bappi yay gyaran murya da tasaka kowa sake nutsuwa a wajen.
“Da farko dai ina tayamu murnar ganin wannan wata na shawwal da rai da lafiya. Ina roƙon UBANGIJI ya amshi ibadunmu da mukayi, ya yafe mana kura-kuranmu. Yasa muna da rabon ganin na gaba da rai da lafiya.”
A tare suka amsa da (amina).
Ya cigaba da faɗin, “Nasan zakuyi mamakin canzawar zaman meeting ɗin yau, dalilin hakan kuwa ya dangantane ga Ramadhan kacokal”.
Da dauri Gimbiya Su'adah da yaran ke kira da (Maa) ta ɗago jin an ambaci sunan gudan jininta mafi soyuwa. Yayinda firgici da taraddadi ya bayyana cikin ƙyawawan idanunta. Dan batason mi kuma ya samu Ramadhan ɗin ba koya aikata. Tunda yau kusan satinsu biyu rabon da suyi waya sakamakon ta masa maganar ya daure yazo musu salla gida......
.... ya katse mata tunani da cigaba da faɗin, “Wani babban al'amarine ya tasoma gidan nan, sai dai mun ɗaukesa kacokan mun rataya ga shi Ramadhan saboda wasu dalilai. Na farko yin hakan zaisa ya dawo kusa damu dole. Na biyu zaisa yazo shima yay aure. Na uku ya isar da abubuwan da muka kasa isarwa ga sauran mutane bisa ga abinda ALLAH ya azurtamu da shi.”
Duk da a dunƙule yay dukan bayanin hakan bai hana farin ciki bayyana a fuskar Maa ba. Ji take tamkar Bappi ya mata albishir ne da wani yanki na farin cikin samun ƙyaƙyƙyawar makoma. Tana matuƙar burin ganin yaronta a kusa da ita. Tsabar jin daɗin hakan harta gama yanke masa matar aure a ranta. Dan wannan karon tanason zaɓama yaron nata matar aure ko hakan zaisa ta sanadin matar ya dawo gareta ba wajen Anne ba....”
Dogon tunanin da gimbiya Su'adah ta tafi yasa har Bappi ya kammala jawabinsa ma bata ƙarasaji wasu abubuwan ba. Sai murmushi take wanda ya kasa ɓoyuwa bisa fuskarta.
★
Ana tashi da ga taron tun kan ta ƙarasa sashenta ta fara kiran wayar gimbiya Asma'u yayarta da suke uwa ɗaya uba ɗaya (Adda Asmah). Su baƙwai mahaifiyarsu gimbiya Naja'atu da ake kira fulani ta haifa, sai dai sauran duk mazane su biyune kacal mata, kuma sune manya. Hakan yasa musu wata shaƙuwa da son juna na musamman dan sun tashine tamkar tagwaye. Kasancewar kuma irin gidansu gidane na tsantsar ƙabilanci da ƴan ubanci yasa kowa da nasa yake shaƙuwa.
Dai-dai tana saka ƙafarta a ƙawataccen falonta na alfarma da yaji kayan more rayuwa har zaman musaltashi zai iya zama ƙauyanci gimbiya Asma'u ta ɗaga wayan. Itama tayi aure tuni, anan cikin garin Bingo ma take, rana ɗaya ma akai musu aure. Sai dai ita tayi kusan shekara biyar bayan aurensu kafin ta samu haihuwa. Yaranta biyu kuma kawai. Mace da namiji.
Batare data dubi su Zuhrah dake zaune a falon kowa na harkar gabansaba ta shige tana mai zolayar yayar tata da faɗin, “Haba ƙasa badai har kin fara barcin naki ba ko?”.
Amsar da aka bata daga can ta sata sakin ƴar dariya tana tura ƙofar glass na corridor ɗin bedrooms ɗinta ta shiga. Ta kan wani tattausan carpet dake a tsakkiyar corridor ɗin ta taka zuwa ƙofar tsakkiya. Ɗaki ne da musaltashi ɓata lokacine. Dan haka kowa ya musalta da kansa. Ƴar sarki matar Alhaji Basheer Hameed Taura. Ta kai zaune tana sake ƙawata murmushin fuskarta da faɗin, “Amin Adda Asmah. Dama albishir na kiraki nai miki”.
Tai dariya saboda zumuɗin Adda Asma daga can. “Oh god hajiyar ruɗu kwantar min da hankalinki. Bafa wani abu bane yaronkine kawai zai dawo NAYA, dalilin kiran naki kuwa maganar aure da mulki da ya sakko a ciki ne. Inaga lokaci yayi da zamu cika burinmu na haɗa auren Ramadhan da Aina'u tunda ta kammala karatunta”.
Dariya ta kuma saki wadda inba Asma ɗin ba babu mai iya ganinta a saman fuskar Gimbiya Su'adah saboda izzarta da girman kai. A take a wajen suka gama yanke hukunci komai game da auren ƴaƴan nasu, batare da gimbiya Su'adah tayi wani dogon tunani ko bincike akan mike a ran Bappi ba.
*_★★HAJIYAR BIRNI HOUSE★★_*
Tun shigowarta ɗakin kwance kawai take tana faman murmushin samun mafitar damuwar data shigo da ita cikin gidan. Dan tabbas da damuwa ta shigo kamar yanda hasashen ƴan uwan nata yake, damuwar da keda nasaba da zuwanta wajen first lady.
Ita ɗin mace ce ƙyaƙyƙyawa kuma gogaggiya, inda a dalilin harkar barikinta ta haɗu da Alhaji Yaro glass babban ɗan siyasa dake riƙe da babban muƙami a ƙasar ta NAYA. Tun a haɗuwarsu ta farko taji sonsa a ranta, inda akai dace shima ya kamu. Dan haka sukai aure cikin ƙanƙanin lokaci. Sai dai abinda bata saniba Alhaji Yaro glass a ƙarƙashin mulkin mace yake a cikin gidansa. Dukkan faɗa ajinsa iyakarta waje ne. Daya taka gate ɗin gidansa sunansa mijin hajiya Fanta. Tabbas ta fuskanci ƙalubale kala-kala a zamanta da Hajiya Fanta da bazasu musaltu ba, har takai sai da ta tsigeta a gidan hankalinta ya kwanta. Ta kuma kauda hankalin Alhaji Yaro glass da ga gareta baki ɗaya, duk da ƙulafucin son komawa garesa da takeyi musamman saboda ƴarsa ɗaya tilo da suka haifa tare dake wajenta. Tun farkon zuwanta gidan suke ƙawance da Hajiya Bushira hamada, wadda sam bata shiri da Hajiya Fanta duk da kuwa mazajensu abokaine shaƙiƙai. Koda yake ance ada ƙawayene suma na amana, sai dai ƙawancen ya watse ne a dalilin ƴaƴansu. Mafari kenan Hajiya Bushira taita tunzura Alhaji Yaro glass ya ƙara aure, tun baya biye mata har yaji sha'awar yin hakan lokacin daya haɗu da Aunty Hannah.
Bayan fitowarta a gidan hajiya Bushira tayi iya ƙoƙarinta na ganin Aunty Hannah ta koma gidan Alhaji Yaro glass amma hakan ya gagara, har suka samu nasarar ɗarewa kujerar mulkin ƙasar ta NAYA. Inda Prof... Usama D. Hamada ya samu nasarar zama shugaban ƙasa bisa ƙoƙarin su Alhaji Hameed Taura. Su kuma su Alhaji Yaro glass suka koma gefe matsayin manya sunacin karensu babu babbaka. Dan ko muƙami ɗaya basu amsaba a bayan fage suke nasu mulkin su.
Hankalin aunty Hannah ya sake tashi dan tana son Alhaji Yaro glass sosai, amma sai Hajiya Bushira Hamada (First lady) ta kwantar mata da hankali akan karta damu, inhar tana raye sai ta koma aure gidan Yaro glass. Aunty Hannah tana cikin manyan ƙawayen first lady da suke mata ayyuka a ɓoye, amma tana ɓoye kantane saboda Alhaji Yaro glass.
A yau ma first lady ce ta buƙaci ganin aunty Hannah ɗin tun daren jiya akan wani aikin sirrinsu, a hirarsu ne first lady keɗan tsoguntama aunty Hannah batun wanda su shugaban ƙasa suke son tsaidawa takara, tare da burinsu na salwantar da rayuwarsa daga baya Alhaji Yaro glass ya maye gurbinsa, dan shine sukeso ya zama mataimakinsa. Wannan al'amari ya matuƙar saka Aunty Hannah a farin ciki matuƙa. Har takejin zata iya bada gudunmawarta akan wannan al'amari. Sai dai maganar data biyo bayan hakan ce ta sakata a damuwa, dan kuwa first lady ta sanar mata sun tattauna da shugaban ƙasa akan suna son samawa yaron matar auren da zata dinga musu aiki a kansa batare da sanin kowa ba, amma suna tunanin ta yadda zasu ɓulloma Alhaji Hameed Taura game da hakan. Dan samawarwa Ramadhan matar aure daga ɓangarensu ne kawai mafita da hangen nasararsu a tafiyar. Hakan yasa tacema aunty Hannah taje ta tayata tunani da nazarin mafita dan tana son ita ta fara kawoma shugaban ƙasa mafita koda ƙara samun ɗaukakarta na mata garesa, sannan ita kuma ta zama first lady kodan cusama hajiya fanta baƙin ciki. Dan ba hawan Alhaji yaro glass bisa kujerar matamakin shugaban ƙasa ko zama shugaban ƙasa bane matsalarta ita. Hajiya Fanta ta samu muƙami dai-dai da wanda ta taka shine damuwarta kawai. shiyyasa take so ta shiga ta fita wajen ganin ta nakasa Hajiya Fanta kafin lokacin Aunty Hannah ta koma gidan ta zama tauraruwa a mulkin da Alhaji yaro glass zaiyi.
Wannan shine dalilin shigowarta da damuwa gidan. Sai dai kuma abinda ta tarar na boran Raudha ya kawo mata mafita cikin sauƙi da take tunanin first lady zatayi matuƙar farin ciki da ita har itama ta samu cikar burinta na komawa gidan Alhaji Yaro glass matsayin matar vice president.
Ta saki murmushi mai ƙayatarwa tare da jawo hamshaƙiyar wayarta 1phone ta shiga sarrafata. Kai tsaye number first lady ta laluba. Harta tsinke ba'a ɗaga ba, dan haka ta yanke shawarar sake kira dan tasan saƙon da