Showing 114001 words to 117000 words out of 204612 words
Chapter 39 - BAKAR INUWA Original Book Complete Document by Billy Abdul .txt
nema towel ɗinta daya koma gefe ta saka.
Tsaf ta gyara ko ina har toilet. Ta tattara kayanta ta fice bayan ta saka hijjab. Tayi mamakin cin karo da su Aynah a falon, sai dai ta ɗauke kanta kawai da niyyar wucesu batare data nuna tasan da zamansu ba.
“ALLAH dai ya rabamu da karuwanci ni Aina'u. Tsabar jaraba baza'a iya riƙe kai ba saboda an saba da maza tun a titi tamkar uwa da danginta. Ni ALLAH ma yasa cikin na Yaya Ramadhan ɗinne ba wani yayisa ba tun kan a shigo.”
Har cikin rai maganganun Aina'u sun soki Raudha, amma sai ta wuce abinta batare data tanka mata ba. Kai ko kallon inda suke batai ba ma balle ta nuna tasan da zamansu tai shigewarta ɗakinta.
Sai da ta kammala shiri tana ɗan kimtsa ɗakin nata maganganun Aynah na ƙarshe ke mata kaikawo a rai. (Ciki? Wa take nufi nada cikin?) ta tambaya a zuciyarta batare da tunanin lalubo amsa ba. Haka dai ta ƙarasa aikin da wannan tunanin tai zaman cike takardun jiya dan ta jona wayarta a caji tunda ta shigo.
★★★★
A office kam murmushi ya kasa barin face ɗin shugaban ƙasa Ramadhan. Dan babu abinda ke masa kai kawo a rai sai hidimarsa shi da Raudha na safiyar yau. Shigowarsa office da cos ya fara ganawa akan tsare-tsaren abinda zaiyi a yau. Amma shi kansa cos sai satar kallonsa yake ganin yau babu ɗacin ran nan sam tattare da shi. Hakama a zaman meeting da yay da sabbin ministers fuskarsa ƙawace da fara'a tamkar bashi ba. Bayan sallar azhar ya samu hutun awa biyu shi kaɗai a office. Jiyay tamkar ya kirata a waya. Sai dai zuciyarsa na gargaɗinsa akan idan ya kirata mizaice mata to? Karma ta ya yake rikitata duk da dai yanzu Alhamdulillahi sun saki jiki da juna sosai. Yau ma sama-sama yake jin kansa shiyyasa bai biye mata ba.
(Humm🤳🏻).
*_TAURA HOUSE_*
Tun wayar da tai da su Munirah ranta yake a ƙololuwar ɓace. Koda ta kira Adda Asmah ta sanar mata itama ɓacin ran ta nuna sosai, hakama Fulani. Kai tsaye shawarar Adda Asmah sukabi akan zubda cikin jikin Raudha kota halin ƙaƙa ita da fulani.
Tana gama waya da su ta kira Safina.
“Maah lafiya kuwa kira a wannan lokacin!?”.
Tsaki gimbiya Su'adah tai idanunta na sake rufewa da ɓacin rai dan ba ƙaramin fanfata Asmah ta sakeyi ba, ita kuma ta riga ta yarda da ita tsakani da ALLAH. “Maganin zubda ciki nake so mai tsananin ƙarfi da zai rikito a cikin mintuna goma”.
“Na shiga uku Maah waye da ciki?!”. Ta faɗa a cikin tashin hankali da tunanin cikin ƴan uwantane wata ta yayo musu abin kunya.
“K dalla ba abinda kike tunani bane. ALLAH ya tsari zuri'a ta da fasiƙanci. Wannan ƴar iskar yarinyar ƴar karuwai ce, wai harni Ramadhan zai yaudara Safina ya lallaɓa yay ma shegiya ciki”.
“Innalillahi... Anya Maah kun tabbatarma nasa ne? Kinsan fa yanda Brother yake da taurin kai akan abinda bashi yaso ba. Kuma kowa yasan Bappi ne ya manna masa auren nan bawai yana so bane, ƙilama asiri sukai masa wlhy inhar ya kasance cikin nasa ne ma.”
Sosai maganganun Safina sukai tasiri a zuciyar gimbiya Su'adah. Takai zaune tanajan numfashi mai nauyi. “Safina maganarki kuma nakan hanyar wlhy. Da harna ƙullacesa a raina. Tabbas inhar cikin nan ya kasance nasa yarona baya cikin hayyacinsa sun masa asiri. Nasan wacece kakar yarinyarnan komai zata iyayi dan tayi a baya akan mahaifina”.
“Humm kin gani ko Maah. Nidai nasan Brother bazai taɓa son yarinyarnan ba. Idan ma ƙyau ne ai yanada shi, sannan akwai tarin mata dake binsa wanda suka fita ƙyawun amma bai kula ba sai ita banza ƙaramar alhaki sa'ar Basma fa. Autarmu, inagama Basma ta girmeta wlhy”.
“Aiko zataci ubanta, zan tabbatar mata damu asiri baya cinmu, dan na kula saka mata idon da nayi ban ɗauka wani mataki a kanta bane ya kawo hakan. Yanzu ki aikomin da sunan maganin”.
“Indai magani ne kwantar da hankalinki, zansa doctor Wali ya kawo miki ma har gida. Sai ma nakejin dama kar a zubar da cikin mu nuna kawai bana Brother bane mu kunyata ƴar iska nasan zaima iya sakinta....”
Ɗan jimmm Gimbiya Su'adah tai tana nazari, sai kuma ta girgiza kai kamar Safina na ganinta. “Ina bazai yuwuba baki da hankali. Idan kuma yace cikinsa ne fa? Ramadhan da shegen kafiya kema kin sani. Sannan tsoffin nan zasu iya cewa bazataje ko'ina ba ta zauna a wajensu har sai ta haihu anyi DNA test. Ke dai kawai mu ɓarar da ɗan iska mukuma san matakin ɗauka da zai hanata damar ɗaukar wani”.
“Okay Maah duk yanda kikace haka za'ayi. Bara na kira Dr Wali ɗin. Amma ya za'a bata maganin?”.
“Wannan mai sauƙi ne ba su Lubnah nacan ba, ai na sake maidasu zama can bayan na tsara tsoffin nan akan zasuje suɗan dinga ɗebe mata kewa injisa. Bayan na masa gargaɗi shi kuma”.
Safina tai ƴar dariya daga can tana faɗin, “Kai wannan shegiya ta zame mana *ƘARFEN ƘAFA*”.
“Nikuma zan zame mata *BAƘAR INUWA* kuwa da sai ta gwammace zaman ranar data baro dani dan ubanta”.
“Shiyyasa nake sonki Maamana”.
Kashe wayar Gimbiya Su'adah tai tana murmushi.
Mintuna arba'in ba'a cika ba Dr Wali ya iso da maganin, tsabar muhimmancin maganin har falon baƙi gimbiya Su'adah tasa aka saukesa taje da kanta suka gaisa ta amso. Tafiyarsa babu jimawa Munirah da zata amshi maganin ta iso. Duk yanda Dr Wali yay mata bayani haka taima Munirah. Tai mata gargaɗi akan su lura da abinda zasuyi.
Munirah ta tabbatar mata da sai tayi alfahari da su insha ALLAH. Da ga haka ta shiga mota driver da tasa ya kawota ya juya da ita government house.
*_GOVERNMENT HOUSE_*
ALLAH sarki Raudha batasan mike faruwa ba. Bayan ta kammala cike takardu ta nemo littafin data ajiye numbers na Mommynsu da ƴan uwanta ta loda a sabuwar wayarta da har credit cart sai da Ramadhan yasa aka loda mata a layin nata. Cikin farin ciki tai kiran number Mommynsu. tana ɗagawa taji muryarta sai ta sa kuka dan daɗi. Ita Asabe ma sai abin ya bata dariya. Amma tunanin ko Raudha na cikin wani ƙunci ne data guda tun farko yasa dariyartata kasa fitowa ta hau jera mata tambayoyi. Da ƙyar Raudha ta haɗiye kukanta ta tabbatar mata da babu komai jin daɗin jin muryartane ya sata kukan kawai.
Ajiyar zuciya Asabe ta saki, sai kuma ta hau saka mata albarka. Sunyi hira sosai ta sanar mata zancen makarantarta ta tayata murna. Daga haka ta gaisa da sauran ƴan uwanta har hajiya mama da hajiyar birni da yanzu ta daina zuwa shago sai su Fatisa. Sai dai tana zuwa taga yanda komai ke tafiya ta koma gida.
Bayan kammala wayar ne taji yunwa na ƙara damunta dan bata karya ba. Mikewa tai ta fita da fatan ALLAH yasa akwai abinci table. Addu'arta kam ta karɓu, dan haka babu ɓata lokaci tai zaman cin abincin da tunanin idan ta kammala ta ɗan sauka downstairs dan duk yau basu haɗu da su Mama ladi ba.
Wani irin cafkewa su Munirah dake laɓe sukai lokacin da Raudha take haɗa shayi. Sun tsiyaye ruwan flask ɗin duka suka bar dai-dai kofi guda suka saka ƙwayoyin maganin fiye ma da yanda akace su bata. Maimakon 2 sai suka saka har 6 dan basu da hankali. Wai yanda cikin zai rikito da wurwuri kowa ya huta.
Tsaf Raudha ta shanye shayin ta ɗan sha farfesu saboda bakinta babu daɗi. Dama ita idan tana period tata kwaɗayi kenan tamkar mayya. Ko abinci bata cika so ba tafi son nama a irin wannan lokacin. Riƙewar da mararta tayi ya sata ɗan dakatawa da ga shan farfesun kamar mai hasashe. Kirjinta yay wani irin yankewa tamkar ana kiɗa a kan zuciyarta. A take kanta ya fara juyawa cikin ficewar hayyaci ta kife fuskarta akan kwanon farfesun tana ambaton sunan ALLAH. Ba tare data fahimci mike faruwa ba taji abu na ɓulɓulowa ta kasanta da gudun tsiya yana sauka jikin ƙafafunta...........✍
🤦🏻
*_Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹🏻♀️⛹🏻♀️😘_*
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
__________________
*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*
Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F
*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼
+227 95 16 61 77
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62b9f997e1f6b1b5d98322a0
*_Episode 39_*
..........Sai da suka tabbatar ta fita a hayyacinta sannan suka fito a inda suke ɓoye fuskokinsu washe da fara'a tamkar ba mata ba. Ba imani babu tausayi duk da ganin jini na gudu a ƙasan Mable's ɗin dining ɗin, har yana gangarowa cikin falon da gudu.
Shigowar kuku da yazo kwashe kwanika da tunanin an kammala da su ya saka Lubnah da ta farga da shi sakin wata irin ƙara tana nufar kan Raudha da tayo ƙasa zata faɗi cikin fita hayyaci. Munirah zatai magana itama ta farga da kuku sai ta sanya nata ihun itama. Ihunsu ya rikita falon gaba ɗaya har Mama ladi da Mama Tambaya dake falon ƙasa jiyosu suka hauro babu shiri.
★★
Dole akai gaggawar mika Raudha clinic na cikin gidan. Dan duk wanda yaga yanda take zubda jini abun sai yayi matuƙar firgitashi. Doctors ɗin kansu ruɗewa sukai, haka suka rufu a kanta kusan su uku domin ƙoƙarin ganin sun tsaida jinin sun ceto rayuwarta, dan tuni numfashinta ya bar gangar jikinta.
Mama Ladi da duk ta gama ruɗewa ce ta kira Anne ta labarta mata abinda idonsu ya iya gani. Haka ma Mama Tambaya ta kira Aunty Hannah ta sanar mata. Cikin ƙanƙanin lokaci sai ga aunty Hannah ta iso saboda ta ɗanfi kusa da Anne. Itama Anne ba'a haɗa mintuna talatin ba ta iso harda Yafendo da Inna duk da suna fama da tsufansu.
Har kusan azhar doctors ɗin gidan na gwamnati basu ce komai ga su Anne ba, dan Dr Hauwa ma da sukazo tare da su Anne itama ta ƙaru cikin doctors ɗin. Kowa yay jigum-jigum cike da fargabar abinda suke tsoron ji. Bama su ba shaƙiƙanta hatta da ma'aikatan gidan duk wanda al'amarin yaje kunnensa a tsorace yake. Gaba ɗaya sai gidan yay tsitt.
Ramadhan baisan halin da ake ciki ba sai da suka fito salla COS ya samesa a office yake sanar masa kiran da ya samu da ga Chief security na gidan game da Accident ɗin da Raudha ta samu wanda har yanzu ba'a san musabbabin sa ba. Sosai hankalin Ramadhan ya tashi, amma a fuska bazaka taɓa tabbatar da haka ba, sai nanata kalmar cos ɗin yake a cikin ransa tamkar karatu. Gashi yana da shiga meeting a dai-dai lokacin kuma mai matuƙar muhimmanci. Haka dai ya dake cikin dauriya ya shiga meeting ɗin badan ya fahimci komai da aka tattauna a wajen ba. Baima haɗa mintuna talatin ba ya fito ya barsu su ƙarasa.
Ya sake ganawar sirri da wani babban mutum da ga ƙasar Nigeria akan wani aikin haɗaka da suke sonyi da ƙasar ta Nigeria ɗin. Sai dai zaman nasu bai wani armashi ba saboda hankalin shugaban ƙasa rabi yana cikin gida. Awarsu guda suka kammala ya fita sallar la'asar. Abubuwan da suka rage masa na sauran awoyin ba wasu masu tsawwalawa bane idan ka cire ganawa da vice ɗinsa Alhaji Yaro glass, dan haka yasa cos sokesu sai gobe idan ALLAH ya kaimu shi kuma ya shiga gida.
Iske su Anne da yay a gidan ya sake tabbatar masa da al'amarin babbane. Gashi sun sanar masa har zuwa lokacin basuji da ga doctors ɗin ba. Zama yay kawai cikin kujera ransa duk a dagule. Gaba ɗaya yama rasa wane kalar tunani zaiyi shi kam, yasan jiya ta shiga wani hali, amma lafiya lau ya fita ya barta yau ai.
“Anne har yanzu basu ce komai ba? Kuma babu wanda yasan miya faru daga nan ciki?”.
Cikin jimami da damuwa Anne tace,, “To ALLAH kaɗai dai yasan musabbabin gaskiya. Amma su su Lubnah sunce tana cin abinci ne abin ya faru, suma sai ganin jini sukai malale a ƙasa, shine ma suka shiga ruɗanin da har ya fargar da su Ladidi”.
Iska ya turo daga ƙirjinsa ya fesar ta baki a hankali tare da kai hannu saman goshinsa yana ɗan murzawa. Cikin jimamami Yafendo ta karɓe zancen da faɗin, “Shi dama cikin fari na mai rabo ne, sai dai fitar nata yazo da haɗari. Dan tsinkewar jini irin wannan kam tashin hankaline babba ga mai ɓari, sai kace wadda aka ba wani abu”.
Aunty Hannah da tun ɗazun batace komai ba sai satar kallon shugaban ƙasa da takeyi, dan yau ne ta fara ganinsa ido-da-ido itama a cikin gidan tunda take zuwa. “Da alama cikinne ma dai baiyi wani ƙwari ba shiyyasa. Amma al'amarin yayi kama da wadda tasha wani abu kam gaskiya”.
“Ciki?!”.
Shugaban ƙasa ya firta cikin kasa ɓoye al'ajab nashi. Kallonsa sukai gaba ɗayansu duk da kuwa yayi maganar ne a hankali. Anne tace, “Ikon ALLAH, kai bama kasan da cikin ba kenan? Amma jiya ba Hauwa'u tazo ta dubata ba?”.
Kansa ya ɗan jinjina mata sai kuma ya haɗiye dukan abinda ke masa kaikawo a cikin rai. “Itama sai yau zata bamu sakamako dama Anne”.
Yay ƙoƙarin danne gaskiyar zancen saboda wasu abubuwa da ke masa kai kawo a rai da zuciya. Shiru falon ya sake ɗauka na wasu mintuna. Kafin ya miƙe da kansa ya fita da ga falon zuwa Clinic ɗin.
Koda ya fito securitys sukai masa caa hana kowa binsa yay, sai dai duk da haka odilan ɗinsa bai yarda ya barsaba duk da dai a cikin gida ne. Ba wata tazara bace mai yawa tsakaninsu da clinic ɗin. Zuwansu yayi dai-dai da fitowar doctor Sambo da ga ɗakin ya baro su Dr Hauwa dake ƙarasa gyarata. Cikin ɗan rikicewar ganin oga kwata-kwata da kansa ya fara miƙa gaisuwa. Hannu kawai Ramadhan ya ɗaga masa, sai kuma yay masa nuni da office alamar su koma ciki..
Suna shiga Aynah na Munirah dake laɓe suka kaima bango duka. Tunda suka kira Gimbiya Su'adah suka sanar mata ta basu umarnin zuwa su sami likitan su masa maganar komi za'ai kar bakinsa ya faɗi cewar da safe tasha maganin nan. Ya nuna tun jiya ta sha shi da yamma kuma ba yau ne na farko data sha ɗin ba. Shine sukazo fa, suna gab da isa ga doctor Sambo da suke zaman jira tun ɗazun sai kuma ga yayansu da kansa. Hakan ya saka su ɓuya dan kar ya gansu..
“Wane issue kuka samu?”.
Ramadhan ya tambaya kansa tsaye dan shi baya son ɓoye-ɓoye ko jan rai a magana”.
Cikin in-ina da fargaba Dr Sambo ya fara magana. “Ranka ya daɗe zuwa yanzu dai munyi nasarar ceto rayuwarta, mun kuma tsaida jinin. Sai dai ta zubar da