Showing 120001 words to 123000 words out of 204612 words
Chapter 41 - BAKAR INUWA Original Book Complete Document by Billy Abdul .txt
“Maah!. Aina'u?”.
“Eh ita, idan kuma ban isa ba kamar yanda ubanka da kakaninka suka isa har suka aura maka zaɓinsu ka amsa ba tare da bijirewa ba sai naji.”
Iska ya furzar da ƙarfi yana ɗan rumtse ido da buɗewa lokaci guda. “Maah Please calm down. Kibar zancen wata Aina'u a beg. S.......”
“Anƙi a bari ɗin, kai yanzu Ramadhan dan baka da mutunci har kana da bakin faɗamin nabar zancen ɗiyar ƴar uwata akanka? Aka saka kama auri karuwa....”
(Ya ALLAH) ya faɗa a zuciyarsa yana rumtse ido da murza goshi. Cikin zafin rai gimbiya Su'adah ta cigaba da sauke masa takaicin Raudha da shi kanshi da dama take ƙullace da shi tun lokacin first night da suke tunanin ya faru tun a waccan ranar. “Ita ga ƴar iska mara mutunci, tasan bata shirya haihuwa ba miyasa ta yarda da kai dan ubanta, nama godema ALLAH data zubar ɗin kuma mahaifar tata bazata sake ɗaukar wani cikin ba. Bani da rabon haɗa zuri'a da jinin karuwai!!”.
Sosai ransa a dagule yake. Amma ya daure dan mahaifiya ta wuce wasa. Babu abinda yake sai haɗiyar zuciya. Babbar matsalarsa auren Aina'u da ta ambata, koma mizai faru sai dai ya faru babu auren Aina'u a cikin tsarinsa. Yariyar daya gani da idanunsa a cikin tsakkiyar club a America ana lesbians da ita, ƴan iska na ihu suna ɗauka a waya (Wa'iyazubillah). Ta rufe fuska da mask, shiyyasa tai tunanin babu mai ganeta, sai dai tayi rashin sa'a shi ya ganetan da idonsa. Dan ya tabbatar mata ya ganeta ɗin kuma ya cire mata mask ɗin. A wannan rana baiyi barci ba dan tashin hankali, dan koba komai itaɗin jininsa ce. Da uwarta da tashi fa uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Sannan mahaifinta shima ɗan masarautar su Maah ɗinne ɗan uwa na jini matsayin Uncle yake garesa. Amma itace yanzu Mahaifiyarsa ke tabbatar masa zai aura. Ji kawai yake ana ambaton Raudha da ɗiyar marasa tarbiyya amma shi har yanzu bai tabbatar ba tunda bai taɓa ganinta tana aikata wani fasiƙanci ba. Itako Aina'u da idonsa ya ganta ba labari ba.......
“Tunda ga ƴar iska ina magana kamin shiru ko!!”.
Gimbiya Su'adah ta faɗa cikin dawo masa da hankalinsa gareta. Ajiyar zuciya ya sauke yana gyara zamansa. Cikin tausasa harshe yace, “Maah Please relax. Ki bari ki huce sai muyi magana daga baya. Indai dan haihuwa ne insha ALLAH jikoki har sai kin rasa yanda zakiyi da su a gidan nan.....”
“ALLAH ya tsareni samuwarsu da ga wannan jinin karuwan da talauci. Dan haka karka sake min irin wannan maganar zan ɓata maka rai”.
“Ok. ok!. shike nan kiyi haƙuri Please”.
Tsaki taja tana ɗauke kanta gefe. Kaje dare yayi, amma ka tabbatar ka samu kakaninka da mahaifinka da maganar Aina'u dan wlhy babu fashi saika aureta, sai dai in mutuwa kayi ko ita ta mutu”.
(Oh oh, shikam yau ya zaiyi da tsohuwar nan) ya faɗa a ransa yana dafe kai.
*_GOVERNMENT HOUSE_*
Tunda ya shigo ya zube a falon upstairs ɗin ransa duk a jagule. Kansa harya fara ciwo tsabar rasa ina zai kama. Magana da yake ji ƙasa-ƙasa kamar ana raɗa ya sashi sake nutsuwa da hasashen ta ina ne. Fahimtar da ga inda sautin ke tashi ya sakashi miƙewa. Kansa tsaye ya tunkari wajen, amma tsabar shagala da Aina'u tai a wayar da take yasa sam bataji motsinsa ba balle ƙamshin turaren sa.
“Amma naji daɗi Ummi da kika sake tunzurata, duk da dai wlhy a tsorace nake. Har zuciya ina son Yaya Ramadhan, amma nasan akwai matsalar da tai mana katangar danne zumuɗina. Gani nake kamar tursasawarku ma bazatasa ya amince ya aurenin ba......”
Shiru tai alamar an katseta daga can. Sai kuma ta sauke numfashi. “Wlhy zan jure Ummi, nidai yanzu burina ya amince ɗin, indai na zama matar tasa komai mai sauƙi ne. Sannan ƴar iskarnan nasan da wahala ta sake ɗaukar ciki kamar yanda doctor ya sanar mana. Kinga sanadin barinta gidan yazo kenan ƴar karuwai”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi sai kuma ta dumtse bakinta tana ɗan waige irin kar ajitan nan. Hakan yasa Ramadhan sauri ɓoyewa dan karta gansan. Janye hanunta tai a baki tana cigaba da faɗin. “Nifa harma mamakin yanda akai cikin nake Ummi, wlhy kinga wancan zaman har muka bar gidan nan bamu taɓa ganin ta shiga ɗakinsa ba ko shi ya shiga nata. Hakama yanzu banda randa muka gane tana da ciki datai pretending ya ɗakkota daga falonsa bamu taɓa ganinsu tare ba. Ni anyama cikin nan bada shi tazo ba....”
Shiru ta karayi na saurare. Sai kuma tace, “Wlhy Ummi komai zai iya faruwa. Ke dai ki cigaba da fanfa Maah dan ALLAH ayi-ayi nima na shigo wannan daular ta mulki a dama dani. Hhh Ummi nice nafi dacewa da first lady ba wannan ƙwailar yarinyar da ko ƙirar mata bata da shi ba”.
“Ok Ummi kije wajen Abban karya jimu kin sansa. Da safe ma karasa”.
Da kallo ya bita daga inda take tsaye harta shige lungun corridor ɗin bedrooms ɗin Raudha. Babu abinda ke masa turereniya a rai sai zantukanta da ya fahimci alaƙarsu da birkicewar mahaifiyarsu a yau. Wato Addah Asmah na tunzura Maah akan matarsa dan ya auri ƴarta. Wani murmushi ya suɓuce masa a bazata ya kai hannu ya shafo ƙeyarsa.
Maimakon ɗakinsa da ya kamata ya nufa sai ya wuce na Raudha kamar yanda zuciyarsa ke tunzurashi. Kansa tsaye ya murɗa ƙofar ya shigo. Mama Ladi da ke lallaɓa Raudha ta sha ko farfesu ne da shayi tai saurin kallon ƙofar tana amsa sallamar da yay a hankali. Tunkan ya karaso ta risina tana gaisheshi. Amsawa yay idonsa akan Raudha data dafe kanta saboda ɗan nauyin da yay mata.
“Wani abu ya sake faruwa ne?”.
“A'a ranka ya daɗe babu abinda ya faru, bayan fitarka ne ta sake komawa barci sai yanzu ta tashi. To tace tanajin yunwa ne an kawo abincin kuma tace ta ƙoshi. Shine nake lallashinta taci kodan ta samu ƙarfin jikinta kamar yanda likitar tace”.
Komai baice ba, sai alama da yayma mama ladin akan taje abinta. Cikin girmamawa ta risina da faɗin, “A fito lafiya ranka ya daɗe”.
Kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa. Yana tsaye hannayensa duka a aljihu har Mama Ladi ta fice ta rufo ƙofar. Raudha da har yanzu hanunta ke dafe da kanta cikin rashin ƙarfin jiki tace, “Ina yini”?.
Karon farko taji ya amsa mata gaisuwarta da “Lafiya, yaya jikin naki?”.
“Alhmdllhi naji sauƙi”.
Nanma baice komai ba ya taka zuwa bakin gadon ya kai zaune kusa da ita gab. Hanunta data tallafe kanta da shi ya janye da faɗin, “Oya ci abinci”.
Batare data yarda ta kallesa ba ta marairaice fuska kamar zata fasa kuka. “ALLAH na ƙoshi”.
“Ashe zan miki ɗura kenan ok! Bana son gardama maza ɗauka”.
Bata da zaɓin daya wuce bin umarninsa. Dan yayi kicin-kicin da fuska babu alamar wasa tattare da shi. Badan yana mata daɗi ba ko ɗanɗano ta fara tsakurar abincin, yayinda shi kuma ya ciro wayarsa a aljihu ya fara dannawa. Da wannan ƴar damar ta ɗanci tea ɗin ma kaɗan. “ALLAH na ƙoshi”. Ta faɗa a marairaice dan yaji tausayinta.
Wayar ya ajiye tare da ɗagowa yana kallonta. Yanda ya ɗan tsura mata ido kamar mai nazari ya sata fara wasa da zoben hanunta......
“Yanzu mike miki ciwo?”.
Kanta ta girgiza masa. “Ba ko'ina, sai dai ɗan jiri shima ba wani mai tsawwalawa bane”.
“Kina sakaci da abinci ne shiyyasa shima bai tafi ba. Idan ALLAH ya kaimu gobe inada tafiya zuwa UK, zan samu kamar 4 to 5days kafin na dawo. So bayan na dawo inada sharuɗɗa na canja tsarin zaman gidan nan”.
Wani irin ƙuuuu cikinta ya bayar amma batace komai ba. Shima bai damu da cewar tata ba ya cigaba da maganarsa a kausashe babu alamar wasa. “Dole ne ki koma tsayawa a kan masu girkin nan inhar zasu mana abincin da zamu ci ni da k. Zaki koma kwana ɗakina dan Maah tana buƙatar jikoki saboda tana tunanin ta rasa wani ne a yanzun......”
Cak numfashin Raudha ya tsaya a aiki, cikin rashin fahimtar zancen nasa dan ƙwalwarta ma jitai ta toshe baki ɗaya ta ɗago tana kallonsa. Shima kallon nata yake cikin sarƙe idanun nata a nashi. A hankali ya kai fuskarsa gab da tata ya hure idanun nata. Saurin rumtsesu tai da ƙoƙarin jan jikinta baya amma sai ya ɗaura hanunsa a fuskar gadon kanta ya sauka akai. Jikinta ya sake matsowa a nata shima idanunsa na ƙara ƙanƙancewa. Cikin wani sautin murya da shi kansa baisan ta suɓuto da ga ƙirjinsa zuwa harshe ba yace,
“Idan kaka taso ganin jikokinta laifi ne?”.
Ruɗanin da Raudha ta shiga ne ya sata fara girgiza kai jikinta na tsuma. Ya kashe mata ido ɗaya da janye fuskarsa a tata ya maida saitin kunenta “To ki shirya bata madadin babyn da take tsamanin ta rasa a jiya”. Ya ƙare maganar da ɗan sumbatar gefen kuncinta ya miƙewa lokaci guda da ɗaga mata yatsunsa biyu “Good-night”.
Fitsari ne kawai ya ragema Raudha ta saki dan al'ajabinsa, amma hatta da kayan cikinta sai turereniyar dunƙulewa suke waje guda. da ƙyar ta iya sake numfashin data riƙe a ƙirji lokacin daya maida ƙofar ya rufe alamar ya fita. Gaba ɗaya kalamansa sai suka saka hajijiyarta sake dawowa sabuwa dan jinin daya batan ma ƙasa ya dinga zirarewa ta cikin jijiyoyi yabi numfashi ya fice fit. Hannu takai taɗan mari fuskarta dan gani take kamar a mafarki take dai, sai dai jin tabbacin a zahiri ne komai ya faru ba mafarki ba ya sata faɗin, “Inaga bashi bane aljani ne”.
(🤣🤣saifa aljanin kam).
★★★★★
*_WASHE GARI_* kamar yanda ya faɗa kusan 8am ya shigo ɗakin nata cikin kwalliyar suit baƙaƙe da suka fiddo masa ainahin tsarin halittarsa da ƙyawun haiba da ƙuruciya. Duk ramar nan ta campaign ta ciko fatarsa ta sake fresh sai ƙyalli yake yi.
Kamar ko yaushe gaisheshi tayi sai dai taƙi yarda su haɗa ido dan har yanzu kalamansa na jiya basu bar bitar kansu a brain nata ba. Tsaf ya fahimci halin da take ciki amma sai ya basar. ATM card ya ajiye mata da wasu takardu guda biyu batare da ya mata wani bayani ba. Ya ɗan kalla agogon hanunsa yana furzar da iska a hankali....
“Zaki iya fara fita school idan kinji ƙarfi, idan kikaiwa gargaɗina ɗaukar wasa zaki iya rasa karatun baki ɗaya. Abota da wani namiji ko ɗan uban waye bana buƙata. Tarkacen ƙawaye bana ra'ayi. Kiyi abinda ya kaiki”.
“Insha ALLAH bazaka sameni da ƙinjin magana ba. Sai dai ina roƙon alfarmar securitys ɗin nan basai na dinga zuwa da su school ba, hakan zai iya nisanta idanu a kaina na zauna lafiya ga kowa dan ALLAH. Sannan ina son.....”
Sai kuma tai shiru ta kasa ƙarasawa.
“Bana son kwana-kwana, idan zakiyi magana kiyita kai tsaye”.
Nanma kanta kawai ta jinjina masa. sai kuma ta ɗan ɗago a marairaice yanda zaifi tausayinta ta ce, “Dama ina son ne naje gyaran kai da kitso na kuma je naga Mummy i miss her”.
Miƙewa yay yana gyara necktie ɗinsa, a ɗan daƙile yake faɗin, “Well kina da damar hakan, sai dai bako yaushe nake buƙatar ganin kitso a kan matata ba. Idan nai buƙatar hakan zance ayi”.
Sototo tayi tana kallonsa baki buɗe har yaje ƙofa. (Oh dama yana mata kallon mata ne wai dama? Ba ƙawance yace kawai suy.....) ganin zai fice tai saurin katse tunaninta. “Dan ALLAH zuwa wajen Mummy fa to?”.
Yanda tai maganar cike da zalama ya sashi ɗan waigowa ya dubeta, sai kuma ya ɗauke kansa “Zamuyi waya”. Ya faɗa yana ficewa gaba ɗaya..............✍
*_Ku garzaya AREWABOOKS ta link ɗin dake sama farkon page, domin samun pages fiye da wanda kuke gani a WhatsApp⛹🏻♀️⛹🏻♀️😘_*
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
__________________
*_JAMA'AR JIGER zaku iya biyan kuɗin littatafan ZAFAFA BIYAR kuma ta nan👇🏼_*
Guda daya=300F
Guda biyu=400F
Uku=500F
Hudu=700F
Biyar=1000F
*ZAKU TURA KATIN WAYA NA (MOOV ko AIRTEL) ZUWA WANNAN NUMBER,TARE DA SHAIDAR BIYA*👇🏼
+227 95 16 61 77
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*_BAƘAR INUWA...👇🏻_*
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
*_Typing📲_*
*_BAƘAR INUWA👉🏻AREWABOOKS👇🏻_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62bc34197660dfc79da0e14b
*_Episode 41_*
...........Yau kwanan shugaban ƙasa Ramadhan da wasu mutanensa uku kenan a ƙasar UK. Zuwa yau kuma Alhmdllhi jikin Raudha yayi sauƙi sosai. Abin ƙarin farin cikin kuma a jiya Asabe da hajiyar birni da Hajiya mama suka zo suka dubata, jitai kamar karsu wuce, dan kuka rurus ta dinga ma Asabe da ta shagala a kallon fadar Shugaban ƙasa da ALLAH ya jeho ƴarta ciki. Ko'a mafarki, ko'a hasashe bata taɓa kawo kwatankwacin hakan a ranta ba. Wani iko sai ALLAH, shiyyasa masanin gaibu sai shi. Bawa karka takurama ranka da hassada da ƙyashi dan baka isa canja komai daga rayuwar waninka ko taka ba. Duk abinda ALLAH ya ƙaddara masa sai ya cimmawa a duniya ko kana so ko baka so. Sai dai baƙin ciki ya cigaba da zama abokin taka rayuwar. Dan kuwa ita ƙaddara ta riga fata inji bahaushe.
Gaba ɗaya sai taji ta sake tsanar kanta da abubuwan da suka faru a Hutawa ita da M. Dauda. Tasan ko bajima ko ba daɗe sai an dingama ƴaƴansu har jikoki gori da waɗan nan halayyar, dan ma Raudha bata sanar mata an daɗe da fara mata gori da su ba.
Zuwan Bilkisu da take kira da Aunty B yay mata daɗi a yau ɗin, dan tazo ne a gabar da take shirin fita wanke kai tunda ya nuna baya ra'ayin kitson duk da ta kasa gano dalilinsa na waɗan nan sharuɗɗan. Tare da Bilkisun suka fita wajen wani haɗaɗɗen gyaran jiki, kai dama dukkan buƙatun tsafta da ƙwalisa na mata. Wajene mai tsaro da sirri, dan mai wajen aminiyar Bilkisu ce. Tunkan su tafi kuma tai kiranta ta sanar mata cewar gasu nan zuwa da first lady tana buƙatar raguwar mutane a wajen.
Cikin rawar jiki miss xoxo ta sallami kaso biyu da rabi bisa ukun mutanen wajen saloon ɗin nata da kayan ƙamshi. Vip section ma ko empty ya koma dan first lady ba wasa ba. Ta zaɓo ƙwararrun ma'aikatan ta da tasan aikinsu babu wasa a ciki irin su Hafsat Rano, Mamu gee, Huguma, Bilyn Abdull. Ta sakasu shirya komai.
(To Zafafa's kuma ba'a samu ministers ba an koma aikin saloon a *_YERWA INCENSE AND MORE_* 🚶🚶🏻😜)
Tarba ta girmamawa first lady Raudha Ramadhan Taura ta samu, duk da zuwane na sirri hakan bai hana wasu farga ba suka fara ɗaukar hoto a sace. Sai dai Alhmdllhi kasancewar shigace ta mutunci a jikinta hijjab har ƙasa da niƙaf ya taimaka ƙwarai da gaske wajen bata nutsuwa. Babu zancen zaman ɓata lokaci bayan gaisuwar girmamawa data dinga samu ga ma'aikatan wajen da har ƴar ƙwalla tayi aka fara mata gyaran jiki tako ina. Dan kuwa Bilkisu ce ta lissafa