Showing 39001 words to 42000 words out of 70788 words
Chapter 14 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt
a jikin sitiyari , zana makullin nayi a goshina ina ci gaba da cewa Sultana bata ɗaukar fansa kuma ba ƙudirin wata fansa zamana da Dikko , kafin insan Dikko inayin rayuwa dan mun rabu yanzu kuma bazai sa in mutu ba , nayi maganar nima ina dukan sitiyari cikin ɓacin rai. Nuna Ashiru nayi da makulli sannan na cije leɓina na ƙasa na tashi mota ina kallonshi..... Riƙe murfin motar yayi yana cewa idan dai kinga kin fita a gidan nan sai idan bana numfashi.....
Ko kayi rayuwa ko ka mutu bai shafeni ba , nasan dai ni na gama magana kuma tunda na yanke hunkunci magana ya ƙare. Ba tare daya kalleni ba yace can baya na taɓa faɗa miki kiyi haƙuri idan baki manta ba , yauma shine nake daɗa baki Hajiya , bayanshi banda abinda zan iya baki a duniyar nan , tunda kike a duniya kin taɓajin wanda yace rashin haƙuri ya sa yacimma nasara ne ? Saidai kiji ance haƙurinta yasa ta cimma nasara , ba wanda zaiyi haƙuri yaji nadamar yinshi saidai nadama takan zo yayin daka gagara haƙuri.
Ban faɗa miki maganganun nan ba dan kiyi zuciya ba , raina ne yaimin babu daɗi. Baki gaji fushi da gudu daga gidan aure ba dan wani ƙalilin abu. Tarbiyya kika gada , Babanki idan yana nan bazai so yaga kinyi yaji ko kina cewa a sakeki ko faɗa da miji. Kuma da yana raye ko kin tafi zai dawo dake bayan yayi miki faɗa da ƙara nuna miki matsayi da kuma martabar miji , dika² ma miye abun fushi ? Ya tambayeni yana murmushin ƙarfin hali , yaci gaba da cewa ai anyi wanda yafi wannan kuma anyi haƙuri sai ɗan wannan Hajiya.....? Wanda bai dakeki ba bai zageki ba ? Ki ƙara haƙuri tunda an hau tudu ai gangarewar baya wahala , kalli ya nunomin hoton Papi a wayarshi , ji yanayin farin ciki kin ajiye ɗan digu²n Papi ina zakije ki barshi ne ? So kike yayi kukan rashin uwa bayan kina raye ? Rayuwar aure da kika ganta gaba ɗayanta haƙuri ne a cikinta , idan akayi haƙuri sai a samu mafita , kiyi haƙuri sai Allah ya baki ladar haƙurin , kibi mijin ki zauna lafiya kiyi masa biyayya saiki samu albarkar rayuwa. Ki nemi gafararsa sai ubangiji ya gafarta miki , fito ki koma dan Allah ki kwantar da hankalin mijinki kema sai naki hankalin ya kwanta. Ya ƙarasa maganar da yanayin tausayi..... Yana ci gaba da cewa ba'asan maci tuwo ba sai miya ya ƙare , masha ruwa magirbi karki biye fushin zuciya kiyi abinda zai jawo miki damuwa. Da yaji da tambayar sakin aure sai "yan gidan da basu da tarbiya , ke ko kina da tarbiya da ɗa'a kiyi haƙuri ki koma idan har kika tafi zaki naƙasa matsayinki da kuma mutuncinki. Kiba Mai gida haƙuri zai haƙura kuma bazaiyi fushi ba danshi mutum ne mai mantawa da damuwa , a inda akayi mishi yayi faɗa ya gama da wurin. Yana da zuciya amma yana da ba abun duniya baya..... Fita ki nuna masa ke ɗin "yar Babanki ce..... Ki basa haƙuri domin ya ƙara tabbatarwa keɗin mai tarbiyace , ki nemi gafararshi sai yayi alfahari da iyayenki domin sune suka koya miki tarbiyar bawa miji haƙuri.
Ko ba komai naji daɗi daya kira iyayena da masu tarbiya duk dai nasan za'ace niɗin eyar ɗan caca ne , ci gaba yayi da magiya yana bani haƙuri , kashe motar nayi tare da zare makullin na wuce banyi magana ba , ɗakina na koma na zauna gefen gado. Yayin da wani sashe na zuciyata yake cemin inyi haƙuri kamar yadda Ashiru yace , kuma in bawa Dikko haƙuri , ba ruwana da wani ciwonshi idan yayi aljannunshi idan ya gaji zai sauka , ya warke ko bai warke ba , ba damuwarki bane ba Sultana , abinda ya hanashi zuwa ya dawo dake tuni shima bai dameki ba , lokacin da ya saki Jiddah da binshi da takeyi dashi da ita da kowa ma can su ta matsemawa , kiyi tunani ki rufawa kanki asiri ki dawo daga rakiyar shaiɗan tun kafin duniya tai gwanjonki.
Tunda ta gama waya da Sultana take ta ɓaɓɓarka zagi , wayar Mai gilashi ta kira amma kafirawan company suka ce mata a kashe yake. Dan haka ta bugi mota tayi gidanta , ba yabo ba fallasa Mai gilashi ta tarbi Sharifa kuma bata , bata izinin shiga ɗaki ba. Haka kuma babu maraba bare kuma sannu da zuwa. Da yanayin tsinkuwa Sharifa tace Mai gilas an fa samu matsala , dakel ta kalli Sharifa tare da tambayarta meke faruwa ne ? Mu shiga daga ciki cewar ita Sharifa , Mai gilashi tace ba buƙatar sirri a ƙuryar ɗaki , magana dake a fili da ɓoye duk iri ɗaya ne. Da mutum yayi maganar sirri dake gara yaje B B C ya faɗa kila idan anci sa'a a ranar wani bai kamo tashar ba. Faɗi abinda ke tafe dake ko na iya baki shawara. Mai gilashi ni a gwadamin iskanci ne ? A , a , waye ya isa ya nunawa na rigingine hasken farin wata ? Cewar Mai gilashi. Sharifa tace to ni matar D ' K ta zaga , ta faɗamin magana , tayimin gori ta wulaƙantani ta muzantani ta tozartani sannan kuma ta tonamin asiri.......
Cikin ko in kula tace duk me yayi zafi haka ne ? Zama kusa da ita Sharifa tayi cewa kwana biyu kenan bama waya bama cht kuma bana ganinshi , Mai gilashi tace kila a tunaninta yana wurinki ne ko ? Cikin rashin fahimta Sharifa tace kamar ya ? Riƙe bakinta tayi da sauri tare da cewa rufama kanki asiri kar aji mutuwar sarki bakinki Ade.... Inji Mai gilas.
Sharifa tace kamar ya haka kuma ? Me zaki ɓoyemin ne bayan kinsan duk karatun iri ɗaya. Mai gilashi tace aini kin daina shawara dani faɗin gaskiya kuma zamanin nan yayi wuya , ina iya faɗa miki kije kiyi ta tallar terere dani , dan girman Allah Mai gilas faɗamin , Mai gilas tace gaskiya Sharifa ni inajin tsoro , dafa Mai gilashi Sharifa tayi tare da cewa idan dai baki faɗamin ba duk yadda tarenmu take tou lallai ƙullu yaci amanar koko , ɗan motsa kanta tayi alamar ta sanar da ita tare da cewa na baki dama kuma nayi miki alƙwari babu wanda zaiji ba wanda zai san anyi.
Mai gilashi tace:• shin bana faɗa miki kina da kishiyoyi ba ? Wanda suke ta harar Dikko a waje ba ? Sharifa tace kin faɗa , shin tunda kike ke Dikko ya taɓa² koda hannunki ne ? Ai bama ya kallo na , tou lallai cikin hijabi kike je mishi zance , Sharifa tace ey wallahi , kina zama kusa dashi ko a , a ? Shiru Sharifa tayi , Mai gilashi tace tou lallai nesa kukeyi da juna ta faɗa tana dariya tare da nuna Sharifa da ɗan yatsa , kallonta Sharifa tayi cewa ai babu ma ta yadda za'ayi ni na zauna kusa dashi , Mai gilashi tace da irin wannan baƙauyar soyayyar zaku cinma nasara har a kai ga matakin aure ? Miƙewa Mai gilashi tayi ta kalli Sharifa sosai sannan tace duk dabbar da tayi kuka tana da dalilin da yasa ta koka , yayin da wasu kan koka lokacin da suke buƙatar abinci , wasu kuma sukanyi kuka yayin da suka ƙoshi ne , kare yakanyi haushi yayin da rigimarshi ta motsa , duk wanda kika gani kwance kila yana rashin lafiya ne ko kuma yana da ƙatotuwar damuwa , haka take ga duk namiji daya tirki ƙarin aure.....
Dalili kuwa shine :• duk gero sunanshi gero. Yayin da aka sarrafashi zai tashi daga sunan gero ya koma wani suna na daban , misali , za'a sarrafashi zai zama fura , kunun kanwa , kunun tsamiya , wainar gero , tuwon gero , gumba , farin kunu , kunun zaƙi ke har danbun gero na gani kuma naci shi a bakina.... Amma duk miye silar zamar da duk wannan abubuwan dana lissafo ? Gero ne ! Shine duk aka sarrafa yayi duk abubuwan nan dana faɗa , tou haka take ga duk namijin daya baro gidanshi. Wasu mazajen zasu fito ne cikin soyayya da rashin jin daɗin sunyi nisa da ilayinsu , me yasa sukejin haka ? Kula , soyayya kissa kisisina kwarkwasa iya fira mai daɗi uwa uba kuma kindai gane ba........? Matansu zasu ɗauke musu tunani su kasance sunayin kewarsu da wa'ancan abubuwan dana lissafo har suje su dawo zuciyarsu da ƙwalwarsu baya barinsu su kalli wasu matan , ko kuma suyi tunanin kowa sai nasu , yana kasuwa ko office amma lissafinshi yana gida , burinshi ya tashi daga kasuwa ya koma dan kasancewa da shi wannan farin cikin dai. Dan haka zasu koma gida cikin farin ciki a taresu da soyayya kuma........ Kinga namiji ne ba , amma hikimar mace ta juyashi yasa ya zama wani daban..
Wasu mazan kuma zasu fito gidansu da ɓacin rai. Su fito kasuwa ko wata ma'aikata , idan ogane a wurin aikin abu ƙalilan zakayi ya ɗaga murya , ɓacin ran gida ya shafeka wanda kai bakaji baka kuma gani ba , idan ɗan sanda ko alƙali kila ma idan makuyi sa'a ba yace ku duk ɗin ayi gidan yari daku , tou a fara faɗo mishi karatun da shi kanshi baida lokacin da zai tsaya sauraronku ko yayi lokacin fitar da haƙƙin mai gaskiya dan haka zaice da mai ƙarar da wanda ake ƙarar duk a haɗaku a kaiku magarƙama. Shima mace ce ta juya mishi lissafi da kuma tunani , mazan haka suke sukan canja ne daga horon da matayensu suka basu , mai tunani ya zama lurasi , lusarin kuma ya zama jarumi. Ya danganta dai da horon da aka bashi daga gida , Sharifa anshe goruba a hannun kuturu ba abu mai wuya bane , tunda har ya ƙetaro iyakar matarshi ya fito sai ki bari matan waje su duma mishi wa² ? Shikenan ke kin haƙuri ? Ki bar musu ? Ke bakya da buƙata ? Sharifa tace ina da... Tou Yusra Jiddah da wata banzar yarinya dana manta sunanta duk kiyi ƙoƙari ki rabasu da Dikko , {{ banzar yarinya da ita Mai gilashi ke nufi itace Sharifa , }} taci gaba da cewa idan kin shirya kin kuma shirya ɗaukar huɗubata bisimillah , tashi sharifa tayi ta matsa kusa da Mai gilas kunneta ta kama tayi mata raɗa bayan sunyi alƙawari da kuma yarjejeniyar amana. Sharifa ta yadda ta kuma ansa , ta yadda da huɗubar *MAI GLASS...* abinda ta faɗa mata zamuji shi idan taje wurin Dikko ne. Dariya Mai gilashi tayi tana kallon Sharifa aka wani tafa , Mai gilas tace haka suke ai mazan iri ɗaya ne , kije ki jaraba. Wannan farashin da zakiyi tukuici sai buƙata ya biya.....
Bugu:• bugun bala'e sukayi ma Amisty bayan sunyi nasarar cafke banza. Kuma dukan bawai irin na yara ba ko na susar jiki ba. Basu bigeta da wasa ba duka na tashin hankali sukayi mata , dukan da idan dai akayi ma mutum irinshi to sai mutuwa. Tafiya babu dawowa. Tunda sukaji zancen kuɗi sukaje wurin suka kafa tarko , duk wani da zai shiga ko fita a gaban idonsu. In banda wawanci da rashin lissafi kuɗin nan wai suna cikin motar Amisty idan taje wai inda zataje sai ta canja da kuɗin ƙasar tayi hidimominta. Haka sukayi mata duka kamar wanda ya tun kari fadar shugaban ƙasa rungume da bindiga.... Ita kuma bayan ta tabbatar kowa yaje ya kwanta ta sulale dan ta gudu saboda bata yadda kowa ya kwana ɗaki ɗaya da wani ba. Ƙarya tayi musu wai zatayi baƙo shine taga dare yayi zata wani ɓace abunta. Tafa ci ƙaniyarta yadda tunani baya zato. Suka ɗauke motar da kuɗin suka barta nan zube kamar asarar tsakar dare.
Har gari ya waye ban samu nayi wani baccin kirki ba , haka kuma na kasa zuwa ɗakinshi , tsoro da fargaba kawai ke damu na , sai zantukan Ashiru dake tayimin luguden san zaman lafiya a zuciyata. Wannan dalili shine ya hanani san zuwa makaranta naji ni kamar wata mara lafiya. Ganin har 1 saura yasa na tafi ɗakinshi a tsorace , da sallama na shiga yana fitowa daga toilet ran nan nashi a haƙe fuskar nan tayi kalar ban tsoro dasa mutum ya shiga cikin yanayin firgicewa , ɗan rakuɓewa nayi cikin rawar murya nace barka da safiya , baimin magana ba bai kuma kalleni ba ya ɗauki wayoyinshi ya nufoni dan fita daga ɗakin..... Cike da tsoro na sake cewa Dikko ina kwana , ke........ Ya faɗa tare da yankamin wani irin firgitaccen mari saida na juya naje jikin bango dakel na haɗiye yawu lokaci guda zufa ya tsatstsafomin a fuska cikina ya juya yayi wani irin zakuɗa a tsorace na kalleshi , da ɓacin rai ya tambayeni wannan marin meya bayyana miki......?
Cikin kuka da marainiyar murya nace har yanzu jikinka da ƙwari , yace to ina nan a yadda nake , ban sauya ba ban kuma tashi a yadda kika sanni ba , dama idan baki manta ba na faɗa miki. Tou yauma na sake maimaitawa idan zaki kiyayi fushina tou ki kiyaye sai ki zauna lafiya , na warke ko ban samu sauƙi ba wannan bai shafeki ba saboda daga matar gida baki kau ba , ya nuna da hannunshi. Rayuwa da ƙaddara abokan juna ne , komai yana da ranar tashi daga aiki kama daga kifin gwangwani har zuwa mu "yan adam , kin gane ba ? Jeki........ Ya nunamin , tafi ya nunamin hanyar fita , ƙara yawan kukana nayi na taho daga inda nake na shige jikinshi ina cewa na bari Dikko na faɗa maganar ina ɗagowa dan kallon idonshi , sassauta murya yayi yana cewa bakijin magana , iskancin ki kullum gaba yakeyi , wai nine kike faɗa zaki zane ? Haba An mata....? Kayi haƙuri bazan ƙara ba , tou me nayi miki kika ɗaureni bayan ni ba mahaukaci ba. Ko abokin wasanki ne ni ? Ya tambayeni yana ɗagoni daga jikinshi , saida nayi shashshekar kuka nace bana so kana yawon dare ne , sai kuma ki ɗaureni ? Wannan wane irin hukuncin hauka ne ? Ai bana so kana fita na ƙarasa maganar ina komawa jikinshi. Murmushi yayi kaɗan a sakace yace An mata......... Ya ƙarasa maganar yana rumgumeni sosai. Cikin dariya yace wai wane mai bahaggon tunanin ne ya baki wannan shawarar ne ? Ɗagoni yayi kowa yana kallon idon kowa yace sai kawai tace miki idan kika ɗaureni zan daina fita ne ehem. Yayi maganar yana shan idanuwanshi. Suna shanyewa a hankali tare da murza su da salon duniyanci. A kasalance na koma na sake kwanciya , dariya yayi da murya mai kama zuciya ya ɗaukeni yaje ya kwantar dani saman gado , saida ya lulluɓeni ya sumbaceni yace jirani ina dawowa yanxu. Yayi maganar yana fita daga ɗakin........
Bayan sati 1.
Mijin Halimatu dai har yanzu baida lafiya. Jinya har ta kaisu asibiti zugar ƙawayenta kuma babu wanda ya bita sai Hadiza. Da ita ake yini akeyin komai sai dare suke dawowa gida ƙannen shi Abdul in maza suke kwana dashi. Da Halimatu ta tambayi sauran ƙawayenta me yasa basa zuwa cewa sukayi mazajensu basu yadda ba.....
Har sati ya cinye Yazeed bai zo ba kuma bayayin waya da Jiddah. Shiru kuma har yanzu baiyi maganar turo magabatanshi ba tunda ya tafi waccan ranar sai yau yazo , duk an ɗaɗɗaure mishi jiki da tsumma an sagale hannunshi da igiya an sargafa igiyar a wuyanshi , wai Jiddah ta bashi mamaki shine dan ta tura mishi wata banzar 5million zata turo mishi ɓarayi suzo su kashe shi su ansar mata kuɗinta. Ai ba dole² yasa ta bashi ba , basai ta turo a kasheshi ba , tou ya basu kuɗin ta daina kiranshi kar yayi mata rashin mutunci , shi da ta ganshi duk cikar garin katsina babu ɗan iska kamarshi. Kuka Jidda ta farayi ita wallahi bata tura kowa ba , Yazeed yace ƙarya zaiyi mata ne ? Bafa a wata banzar miliyan biyar inta ya fara riƙe kuɗi ba. Me yasa a lokacin can da bai santa ba ba'aje an dakeshi ba ? Sai akan ita data bashi ne ? Tou ya fasa auren taje tayi da wani.
Jiddah ta fara wallahi². Yazeed yace shi tama wani daina mishi kukan makirci yasan sharri irin na mata , haka taita bawa Yazeed haƙuri dakel ta shawo kanshi a yadda ya nuna kenan , saida ya sake buɗe fili akayi danbe Jiddah ta tura mishi miliyan biyu tace ta ba malamin ta anayin aiki , dakel Yazeed ya yadda ya anshi biyu , kuma ya tabbatar mata da kuɗin danbe ne ta biya , shi baya wani ra'ayi yana mata yayyafi ne dai dan ta rayu karta mutu. Tayi ma Dikko waya ya ƙaro wasu kuɗin......
Dady kuwa ya bugu iya bugu a yadda yayi fentin gida da sabbin filawowi , Umar ɗan iska ne kuma baƙin mugu , da Dady yasa aka sauke fentina yace ya bada kuɗin ma'aikata zaiji da komai , ya anshi kuɗi masu yawan gaske a wurin Dady hada na toshiyar baki , Umar kuwa wajen gida kawai yasa aka gyara sauran fenti yaci kasuwa...
Duk satin nan Mai madubi bataje makaranta ba , naso zuwa gidanta Mai gida D ' K ya hanani , makaranta ma