Header Ads
Showing 33001 words to 36000 words out of 70788 words

Chapter 12 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt

Ads the beginning of article before Image

07 Jul 2024

748

Ads at the middle of Article

ƙarya yayi miki dan har yanzu zuciyata ta ƙaryata aurenshi. Bata faɗamin ƙarya akanshi wallahi duk abinda ta faɗamin ko ta ansa akan shi tou wallahi zai faru , liƙi a idon bainan nasi bashine yake tabbatar da soyayyarki a zuciyarshi ba , idan ke iska ce to Dikko guguwa ne. Gittawarshi tashin hankali ne domin idan ya taho kowa saiya gudu ya ɓoye saboda girman hatsarinshi , sahun keke ne shi mai gasawa mata azaba a tafin hannu , naji ke iskace. Kanyar kaɗai kike iya ɓarowa banda ɗan kuka , zubdo ɗan kuka saida babban makami badai iska ba ko jifar ƙananun yara , Dikko kuwa iccen kuka ce shi koda karfinka saida rabonka ko ka jira bushewarshi , to shi ɗanye ne yini ɗaya zur kana jefa amma baya faɗowa sai kayi jan ido , idan kuma kika ce ki hau tou lallai sai kin sauko gurguwa. Icce kuka hawanshi sai an shirya , idan ba'asha dare ba asha rana. Dan haka ni soyayyar da yake miki bai shafeni ba , nawa na tabbatar tunda ya kawoni gidanshi ya adanani a matsayin matarshi , ku ya ɗauka mahaukata abon firarshi idan ya fita , jakuna banza da baya zuwa firar zance wurinku a gidan iyayenku saidai ku baro gidajen iyayenku ku biyoshi , ni ban ɗaukeki a bakin komai ba. Saboda duk abinda zaki faɗa masa ko ya faɗa miki a kaina ya fara faɗa , kuma daga gareni ni kalamanshi kaf suka ƙare banza sharar bisa titi mai kauyawan kalamai Dikko baya auren karuwa.......


Zagina tayi sosai tare da cemin *SAI NA AURI D ' K* nace ƙarya takeyi , ta sake maimaitawa , nima na maimaita ƙarya takeyi Dikko ba ƙaddarar mallakin ballagazun mata bane ba , haka mukai ta caccakar juna kowa yana yanka kalamai masu ciwo tare da yima abokin faɗar tashi gori , ita ta gaji da kanta ta kashe wayar ta bayan ta tabbatarmin da sai na fita a gidan Dikko. Tsoki nayi bayan ta kashe nace shirmen banza shirmen wofi.


Haka yaita garari tsakanin Qerau da duk inda yasan akwai wata madakata ta "yan iska har dare amma baiga Hafsa ba kuma babu Amisty , Qerau ya koma ya kafe motarshi ya fito ya daki gaban motarshi ya halbi tayar da ƙafarshi yace wallahi idan Amisty da Hafsa basu fito ba saiya cinna wuta ga duk wani gida dake cikin Qerau kuma haka duk wata karuwa daga yau kasuwarta ta mutu dan duk wata karuwa dake anguwar nan sai ta koma gidan ubanta , "yan iska kowa tabar jaharta da iyayenta sunzo sun zamar musu annoba a cikin garin Katsina. "Yan iska zuwen banza da wofi , tou yanzu zanyi waya a kawo min tankar man fetur duk saina babba gidajen dake cikin anguwar nan , haka yaita ɓuɓɓurma zagi kamar sabon hauka lokacin da sarara.


Babu wanda yayi ma Dady magana. Haka ya kashe santa yaci gaba da ƙaryar rashin kunya iskanci kuma sanka² , karuwan dake zaune a ƙofar gida saman dakali suna lido ko kallo bai ishesu ba , ganin zasu ɗaukeshi mahaukaci da hankalinshi yasa ya samu wani yaro yace yaje maza bakin titi ya kira mishi duk wani ɗan bunburutu kuma su taho da jarkar fetiri. Yaro ya ƙwalƙwala da gudu ya tafi dan tattaro duk wani mai siyar da fetir. Wata tsohuwar karuwa ce da ta gaji da karuwanci har ta gagara tuba ga Allah ta tsufa iya tsufa , breziya ne a jikinta sai zani ɗaurin ƙugu da kallabinta tayi mishi ɗauri irin na tsofaffin "yan iska , kai da ka kalleta kasan ba Allah a lamarinta domin har yanzu duniyar gaba suka bata ba baya ba , tsaye take a ƙofar gidan Amisty fitowarta kenan daga cikin gida tana shan sigari , riƙe tabar tayi da bakinta ta dafa hannayenta a ƙofar. Saida ta gama kalle waje tass sannan ta fito da rangwaɗa....


Wuri ta samu ta zauna ƙafa ɗaya saman ɗaya tana ci gaba da kora hayaƙi tana wani hankaɗe kai sama cikin iskanci da sanin hannunta wurin kwarema iya jan sigari. Kallonta Dady yayi yace ke tsuhuwar karuwa ko kinga Hafsatu ne ? Banza tayi dashi taci gaba da jan hayaƙi tana aikashi sama , wurinsu ya matsa yana cewa zaku fiddosu ko saina tona muku asiri ne ? Sai yanzu tsohuwar tayi magana cewa , karuwan yanzu kamar man kitse ne a saman wuta , yayin da suka ga hasken rana sai su gudu su koma ciki gudun karsu narke , zamaninmu mu kuma , ta nuna kanta tana tafiya da maganar ta cewa mu wutar muke nema ido rufe amma da ta hangomu sai ta suƙe kafin mu iso , ni da lokacin da nake Adda ta ce da saina rabaka gida biyu bayan na ɗaukeka na saka cikin ɗakina shegen nan dasai nayi maka fyaɗe , karuwan yanzu matsorata ne. Su ke gudun mazan ba mazan ke gudunsu ba , zamani na ni kuma da nayi iskanci maza idan suka ganni ɓoyewa sukeyi saboda wutace ta doso wuri , kallon taron yara²n karuwan dake zaune tayi tare da cewa mataye....... Gareku tayi maganar tana nuna Dady. Sannan ta haɗe kai dasu tayi musu ƙus² a dai² lokacin da yaron ya dawo da "yan bunburutu layi ɗaya kowa ɗauke jarkar fetir.....


Gaba ɗaya karuwan suka haɗa baki cewa. Dan Allah Dady kayi haƙuri , 🙏🏻idan ka ƙone mana gida ina zamu zauna ? Wannan gidan da kake gani ba namu bane ba , amma tunda munga da gaske kakeyi bara mu faɗa maka gaskiya , har yanzu tare suke magana kuma a tare kowa ta nuna da ɗan yatsanta manuni suna cewa ai Hafsa da Amisty suna hango motarka suka shige can gidan suka ɓoye suka nuna gidan da Dikko ke kiwon dawakan shi , tare sukeyin magana babu wanda yake wuce wani kamar suna biya karatu , amma kayi haƙuri karka ƙona gidan idan ka ƙonashi wannan gidan za'a siyar a biya masu gidan can kuɗin fenti da abinda ya ƙone , idan kuma aka siyar kaga shikenan kasuwarmu zata mutu kamar yadda kace kayi haƙuri don Allah , suka ƙarasa maganar suna haɗa hannayensu wuri ɗaya na neman gafara.....


Dady ganin sun tsorata shima ya haɗa kanshi da masu bunburutu yace tou kuyi da wasa ku yayyafa fetir ɗin nasan zasuyi musu waya su fito , masu fetir zasuyi magana Dady ya toshesu da kuɗi yana cewa idan dai dan wannan ga kuɗinku , su kuma suna so su faɗa mishi gidan Dikko ne ya duba yaga wace karuwa ta isa ta mallaki gida layi ɗaya tun daga farko da kuma ƙarshen santa , amma sai Dady yace ai bafa ashana za'a ƙyarta ba , ya ƙara musu kuɗi , aje ma Dady fetir sukayi ya ɗauka yaci gaba da watsi dashi yana cewa saina ƙone shi , su kuma karuwai sukaci gaba da cewa Dady dan Allah ka rufa mana asiri karka toya gidan nan. Idan ka ƙoneshi asirinmu zai tonu komai da muka mallaka zamu rasashi wurin gyaran gidan nan , Dady yace saina tona muku asiri , a tare sukaci gaba da cewa ka rufa mana asiri karka tona asirinmu , ci gaba yayi da mita yana saiya tona musu asiri , saida ya gama zazzaga fetir ya ɗauko layter ya kunna yana cewa zan cinna fa.... A dai² lokacin da Umar ya fito shi kuma warin fetir in ya fiddoshi , idanuwa ya zaro tare da cewa kai׳ kashe mu zakayi ne ?


Dariya Dady yayi tare da cewa halan ka tsora ko ? Umar yace ba dole inji tsoro ba zaka kashe mu ? Matsowa Dady yayi da wutar yana cewa to koma ka fiddomin Hafsa da Amisty ance sun sayar min da gidaje 3 da suke duk a cikin lay-out masu haya a gidan ne suka kirani akan ban musu adalci ba na siyar da gida babu notice , su fito su kaini wurin wanda suka siyi gidan ni a bani gidajena , kasan ko miliyoyi nawa na siya ? Tou kaf kuɗin gadon "yan ɗakinmu ne na lashe yayi maganar yana nuna lashewa da harshenshi. Murya ƙasa² tare da matsawa kusa da Umar yana cewa dukiya...... Akan kuɗi babu abinda bazanyi ba , da hannun haggunshi ya murza "yan yatsu biyu sukayi ƙara cewa koma ka fitomin dasu kafin in toye wannan gidan.....


Karuwai kuma cewa sukeyi mun tuba Dady kayi haƙuri karka toye , shi kuma Umar cikin rashin fahimta yake kallon Dady , dariya Dady yayi tare da nuno bayanshi yana cewa ya kaji suna cewa....? In rufa musu asiri fa , saina toye , shin na toye ko kuwa ? Zaɓa mutuwa ko kuɗin gidajena ne ? Umar ya fara takawa baya Dady yana binshi yana cewa me kace ne ? Hannu Umar yakai da niyar ɗora hannunshi akan layter amma sai Dady ya fizge , wurin fizagewar ne ta faɗi wuta kuwa taci gaba da ci.... Karuwai sukace yawwa tou kane asirin ka zai tonu gidan Dikko ne....... Suna dariya , aimu babu wani da ya isa ya kashe mana kasuwar karuwanci ko ya tona mana asiri saidai mu , mu tona asirin mutum , ana baka haƙuri kana rashin kunya , kaga sai kaje ka saido sauran gidajenka kayi mishi gara da ramuwar dokunanshi , tsohuwar tace dokin da aka kawo shekaran jiya na miliyan talatin da biyar ne , shin ka ajeta....? Kwaiwayon maganar Dady sukaci gaba dayi , yayin da Umar yayi gaba yana akawo ɗauki Dady kuma ya fara kiran "yan kwana² asara goma da ashirin.....


Amisty da Hafsa kwance a wata lafiyayyar hotel dake cikin garin Abuja , banƙararren rago ne aka gaso musu , sai kaji da aka kaso musu sunkai ashirin , manyan lemuna na kwali masu tsadar gaske da kwaleyen sigari an jera su da kwalaben giya , ɗakin cike yake da manyan karuwai da suka gode ma zamani da zuwan wannan rana , ita kuma Hafsa daga kwance ta kwance hannunta ta ƙara ƙwalƙwaleshi tasha kukanta sannan ta maidai abunta ta rufe..... Daga kwance Amisty ta fara gabatar da bayani kamar haka.......


Barkanmu da kasancewa a wannan lokaci manya karuwa maza da mata , na baya , gaba , haggu da dama duk muna muku barka da zuwa , {{ wato masu maɗigo da "yan luwaɗi sai kuma mazinata.... }} kamar dai yadda kuka sani muɗin masu sa'ar rayuwa ne kullum nasara muke samu babu faɗuwa , mune manyan jajirtaccin karuwai da muka kafa manya² tarihi a cikin jahar birnin garin Katsina , kuma mune zamani na farko da muka kawo wasan danbe a duniya , kullum nasara muke samu dan haka ya kamata a jinjina ma bariki don Allah , shewa sukayi gaba ɗaya tare da ɗaukar kwalaben giya kowa ya ɗaga.....


Saida kowa yasha yayi gyatsa alamar ta sauka ciki Amisty taci gaba da cewa. Bariki tayimin komai , ta biyani kuma ta raineni fiye da yadda nayi tunanin samu daga gareta , bariki ta itace uwata kuma itace ubata a cikinta na rayu tun bansan wace ce ita ba. Mutane na cewa bariki bata da tabbas , tou ni kuma na ƙaryata masu wannan maganar , bariki kuwa itace mai tabbas ga amana haɗin kai da kuma ƙaunar juna , a taƙaice dai ni bariki tamin tabbas....


A gurguje dai muyi abinda ya taramu a wurin nan , manyan gidaje dake can cikin lay - out na Dadyn su Hafsa mun siyar dasu akan farashi mai tsoka saboda kunsan komai shi ke siyar da kanshi , dalilinmu na siyarwa kuwa sirri ne tsakanin rayuwarmu mu biyun duk dai bama ɓoye ma juna sirrin juna tare ake ci kuma idan an samu , ku nawa ne duk taron ku ? Irga kansu sukayi sannan aka faɗawa Amisty ko su nawa ne , Amisty tace mutum goma ? Tou za'a bawa kowannen ku a ciki zunzurutun kuɗi har naira miliyan ɗaya a cikin kuɗin. Jibi kuma dani da Hafsa zamu wuce india mu wanko zumibi mu dawo..... Idan kuma aka sake samun wata sa'ar sai a tura wasu a cikinku su tafi , tou ya kuka ga tsarin ne ? Kowa yace haka yayi Kaka......


Shagali...... Suka faɗa gaba ɗaya , dan haka aka rufawa kwalaben giya da sigari , suma kaji da naman rago aka ciccinye aka kora da ruwan lemu , bayan sunci iya cinsu aka tattara sauran aka fitar.......


Mutumin da Amisty ta kai Hafsa a matsayin malamin tsibbu shine ya kira Amisty akan shima ta fiddashi , cikin maye tace ai babu kasonka a cikin , haɗata ya farayi da girman Allah amma fur Amisty tace ai ko Hafsa bata kashi da gaurayen kuɗin nan , kuɗi duka suna wurinta sun kuma zama nata. Mallakinta bata rage musu ko sisi kuma da asuba zata fece abunta ta tafi can ƙasar waje ta buɗe sabuwar da'irarta , karuwan suma da tace za'a basu one² miliyan ƙarya takeyi , ai ita ba daƙiƙiya bace ba tasan hannunta , ta siya sabuwar mota ta miliyan 5 dan haka daga nan zata canja akalar tafiyarta zuwa Mambila , idan taje ta huta daga can zata wuce gaba abunta ta wani ɓace cikin duniya kamar yadda jirgi yake lumewa a cikin giza²i dake saman sararin samani , dariya tayi sosai cewa kusha zamanku a Katsina Amisty ta tafi yawon buɗe ido sai mun haɗu a lahira. Hahahahaha tayi dariye cike da iskanci kamar zatayi kuka , Allah sarki zanyi ƙewarku Katsinawa...... Dariya ta sakeyi bayan ta kashe wayar tace Amisty tayi gaba kuma babu dawowa........


Wata irin ashar ya fesa bayan Amisty ta kashe wayarta. Cikin ɓacin rai ya sake daddana ashar kamar rainon mutane gafiya , yarinya idan kinsan wata baki san wata ba , shima dake kwallon gigiye ne wurin iskanci da taurin kai , cikin garin ya famtsama a daren saida ya gano har hotel in da Amisty take a Abuja , mutanensu na can Kaduna da kuma "yan iskan dake saƙe a sansanin yanki Abuja manyan "yan ta'adda ya buga ya rattaɓa musu komai ya kuma ƙara da cewa su hari Amisty. Su ƙwace kaf kuɗaɗen har motar karsu bar mata....... Shima yana zuwa Abuja a daren nan , suma bayan sun gama waya dashi suka sanar da mutanensu na Katsina suka kuma tura hotonshi da adireshin cewa su ɓarar dashi suna da kaso biyu a cikin kashi goma na kuɗin , shiri suka farayi ta yadda zasu riƙe Amisty da kuɗin cikin sauƙi......


Kirari yake ta goga mata kamar tsohon maroƙin da yayi shekara baici ba , su Jiddah saidai a juyar da kai ayi dariya kan׳ dariya irinta jakkan mata , haka Yazeed yaita ɗorata tana hawa shi kuma ya rungume banzar yaita lalubarta. Daƙiƙiyar ta saki baki taci gaba da dariya kamar kwarto yaga wa²n zama. Haka yaita suɗeta yana bazo mata manyan kalaman batsa , a cikin motar dai ya labbaceta ya buga round ɗaya na danbe , yau yanajin shi wani babban shege ne yabi hanyar da D ' K ya taka ya wuce..... Bayan ya karance tayi mishi transfer na 5miliyan. Sannan tace a tsaida ranar aure tunda an samu kuɗi , kai tsaye yace sati mai zuwa.... Da farin ciki Jiddah ta fice Yazeed kuwa ya wuce wurin harkar danbenshi tunda ya samu kuɗi.


A ɗakinta dake gidan Rabiya ta kwanta ruf da ciki a saman gado tana tunanin Dikko , jinjinoshi tayi sosai sannan ta jinjino haɗuwarta da Yazeed kai zanen ba ɗaya bane ba kuma karatun yasha ban². Dikko fa daban ne yayi zarra + zarra , gaskiya da gaskiya ce , jarumta ta zahiri duka da duka , salo bisa salo ƙwarewa da iya gugar zanar sanin abinda ake kira da danbe yana nan wurin Dikko , wannan shi ake kira jarumin namiji ba lusari ba , kana ta ina ne haka ? Me kakeyi yanzu ? Kana tunani na ? Koma dai miye ina nan dawowa gareka ka ƙara haƙuri ɗan uwana.


Sun nemeta har sun kaji , bokansu ya bugi ƙasa ya zana , ya goge amma ya kasa ganin inda Mardiyya ta shige , haka nan Suwaiba ta haƙura ta dawo Katsina. Kuma bata wuce Daura ba tana nan ta saƙe a cikin Katsina !


Bayan anyi nasarar kashe wutar dake ci a wajen gidan Umar ya riƙe Dady tare da cewa saiya kaishi wurin Mai gidansu. Haƙuri Dady ya bawa Umar cewa shi baisan haka abun yake ba , iyakar dai wutar waje , babu abinda taci sai fulawowin da sukasha fetir dan haka suka babbake bangon wurin yai duhu. Umar ganin tashin hankalin da Dady ya shiga bai faɗawa Dikko abinda ya faru ba , saidai zaiyi sabon zubi na filawowin da sukaci wuta , sai fenti da yace gaba ɗaya kaf gidan daga ciki har waje zaiyi fenti dan idan akayi a wajen gidan kaɗai Dikko zai gane , idan kuma ya gane zaiyi tambaya shi kuma zai faɗa masa kai tsaye baya munafirci , sai shi kuma a bashi na toshiyar baki.


Wannan tsohuwar karuwa ba haka taso matsalar ta tsaya ba , taso a toye kaf gidan dan Dady yaci uwarshi wurin yaron nan , ita sau ɗaya ta taɓa ganin Dikko shima abinda yasa yadda taji Hafsa tana zuzutashi , ita tasharshi da aka bata labarin abinda yayi ma Sultana ya burgeta yadda taga Dikko tana so taga Sultana itama , to shine fa ta matse lamba taga ɗan iskan yaron nan ,

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads