Header Ads
Showing 42001 words to 45000 words out of 70788 words

Chapter 15 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt

Ads the beginning of article before Image

07 Jul 2024

752

Ads at the middle of Article

shine yake kaini yake kuma ɗaukoni , ga wayar ta idan an kira ba'a samu , sai na haƙura kawai.


Har yanzu Dikko bai cire wayarshi a jirgi ba , kuma satin nan ya bigeshi bai fita , ko gidansu rabon da yaje tun ranar daya kwantar dani a gado yaje. Kuma ya taho da Papi saboda Nabeela ta tare gidanta. Banje ba , abinda yasa kuma saboda ciki shi yasa ya hanani zuwa.


Sharifa da Aunty Bilki ganin ana neman a buga musu game over yasa ta samu Dady akan yayi ma Dikko magana yaje wurin Sharifa , ya kama waya ya rufe sati 1 kenan da kusan kwana 2 basa waya kuma basa haɗuwa. Tadaiyi "yar barikinta a gaban mijinta irin tamu ta mata , Dady kuma ya kira Dikko yace duk abinda yake yau yaje ya haɗu da Sharifa. Shi Dady gani yakeyi ita Aunty Bilki tafi Momy mutunci tunda tana san "yan uwanshi har take tunatar dashi akansu.


Wani irin ihu Dady yayi tare da zubewa ƙasa somamme. Yayyen Hafsa suka rufa mata da duka wanda sune sukayi tsaye wurin nemota. Can abuja suka kamo "yar iska a wata asibiti wai tana jinyar Amisty tana so ta dawo taji ina kuɗi suke ? Shine suka tattaro su dukansu da Amisty da ita Hafsa..... Shine fa kawai ya wani some dan Hafsaf fa kawai ta tabbatar mishi da ɓarayi sun kwashe kuɗi , daga an faɗa mishi shine kawai zai wani zama mataccen bakin maƙabarta.........????


















*JAMILA MUSA...*
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_






*KWARATA RETURN...*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_




Rubutawa...
*JAMILA MUSA...*






*SAI NA AURI D ' K*






🅿 ------ 8




Saida sukayi mata lullusar fitar hayyaci sannan suka shafawa Dady ruwa ya dawo. Kamar ƙaramin yaro haka ya riƙa gumza , muuuuu , tutu² sai kace sabuwar mota ta haɗu da tsohon inji. Dady kayi haƙuri ka daina kuka , saida ya gama kallonsu sannan ya kalli Hafsa yace shin an kamo ɓarayin ne ? Suka ce a , a , luuuu Dady ya sake komawa suma. Haka sukayi ta dawo dashi daya dawo sai yace an kamosu ne ? Amma da ance masa a , a , sai ya sake somewa. A na ƙarshen ne ya wani babbanƙare ya riƙe yaƙi lanƙwasuwa baya gaba kuma yaƙi yayi baya kamar aljannun mata sun taso. Bayan ya tabbatar musu da cewa kada wanda ya sake dawo dashi idan har ba'a kamo ɓarayin nan ba. Babban ɗanshi yace Dady idan ba'a gansu ba fa ? A hankali ya maida kanshi ƙasa ya lumshe idanuwanshi cikin tashin hankali sannan yace ku barni kawai in mutu.....


Cike da farin ciki Yazeed ya isa majalisarsu. A mota ya warware tsumman daya ɗaɗɗaure jikinshi yana dariyar ƙeta. Lallai Jiddah muguwar daƙiƙiya ce. Wato ita har ga Allah ma ta yadda anje anyi mishi dukan ? Ballagar mace uwarki tayi asarar aihuwa. Fita yayi daga cikin motar haka ya shiga cikin da'irar abokansu yaci gaba da fallasa Jiddah , wai wasu zawarun ballagazu ne. A kyauta yake shan iska babu wani damuwa. itama kanta a kame take kamar barden goyon daya yini baisha nono ba , da yaji gari yayi mishi zafi can yake tafiya yawon honey time. A can dai yake zubda ƙura ya dawo gida , ga kuma kuɗi kwance a account , ya nuna kwanciya da hannun shi yana ci gaba da cewa lallai Yazeedu babbar ƙaddarar mata ne ni. Ɗan yatsina fuska yayi sannan yaci gaba da cewa bafa laifi tana barbaɗa wuta a filin wasa D ' K ya kowa mata doguwar tafiya. D ' K...? Hmmm Dikko duniya sai Allah , ya faɗa yana riƙe haɓarshi da yanayin mamaki ya ƙurawa wuri ɗaya ido alamar tunani.


Tambayarshi akayi ina ya samo zawara a arha haka ? Dariya yayi sosai tare da jinjina kanshi yace matar D ' K da suka rabu. Cikin dariya yaci gaba da cewa wai dan uwar biko shi D ' Kn yake bikonta dan ta ɗauki kanta alalan gero. Hmmm lallai iska tana wahalar da mai kayan kara , idan dai D ' K ne cikin ruwan sanyi zai kasheta bata san iskancinshi ba aradu labarinshi takeji. Tou kai meya haɗa ka da ita ne ? Waye ma ya sanar ma angulu a masai...... Ya ƙarasa yana ƙara gaggaɓewa da dariyar fita addini.


Bayan wani lokaci ya nuna kanshi yace wai ni ? Nine zan aureta , in banda haukar mata da rashin tunani ni ? Wai ni Yazeedu nine zan aureta ? Gaskiya bata da lissafin rayuwa. In banda abunta bata duba can²nta ne ? Idan na aureta uwar me zan bata ? Filawa ai tafi kyau da gidan masu kuɗi , shanyar dusa kuma da kauɗar bushashen tuwo wannan kuma ai sai gidan talaka. Zanyi ta zuwa dai ina karantawa inyi gaba , wata irin azzalimar dariya ya sakeyi yana cewa bata san itama ta gidan neman hanyar tsira takeyi amma bata samu sa'a ba , hahahahaha kai yarinya bakiyi ma cikinki da gangar jikinki adalci ba , zo zo² zoki mana idan dai nine ni naci uwar ɗan tasha , dan bana tunanin duk cikar faɗin birnin jahar katsina kawai irina , banda mutunci kuma na tabbatar da cewa tantiri iri na a duk faɗin yankin katsina bafa za'a taɓa samu ba. Dan babu tantirin ɗan iska kamata , idan dai kinajin wasa ki tambayi Dikko ya baki labarina.


Fat , Fat , ² haka lumfashin Amisty ke halbawa tsakanin rayuwa da mutuwa. Yau duk abokan tashar nata babu wanda yake ɗakin da sunan jinyarta. Uwa ko uba nata kuma ? Basu da labarin halin da take ciki. Tunda ko tana da lafiyarta basa ganinta basa kuma jin labarinta , a gari ɗaya ake amma kowa yana nashi matsugunin. Wani bushashen ɗan sanda aka aje wanda koke mace idan baki da yunwa kina iya bashi kashin bala'e. Wai shine aka ajiye dan ya kula da Amisty. Idan ta dawo hayyacin ta , ta nemo musu inda takai musu kuɗin Baba. Likita ne ya shigo tare da malaman jinya bayan yayi ɗan abinda zaiyi aka taimaka ma tafiyar numfashin nata da iskar bature. {{ Oxygen }}.

Kallon agogon dake ɗaure jikin tsintsiyar hannuna nayi sannan na kalli inda yake tsaye jikin madubi yana murza hula , ta cikin madubin ya kalleni so ɗaya sannan yaci gaba da abinda ya shafeshi. Bakin ƙofa na koma na tsaya ina cewa gaskiya ba inda zakaje na ƙarasa maganar kamar zanyi kuka. Juyowa yayi tare da jingina da jikin madubi ya dafa hannunshi ta baya cewa. Nace miki bazan daɗe ba , tou kuma tunda kasan baka daɗewa ai ba buƙatar fitar ko...? A hankali ya fara tahowa yana cewa tou ki hanani fita da ƙafafuwa na in gani mana. Kwanciya nayi ƙasa a bakin ƙofa kaina na kallon sama na miƙe ƙafafuwana da hannuwana nayi irin kwanciyar gawa. Cikin kuka nace shikenan ka tsallake kabarina Dikko ka wuce. Da sauri ya maida ƙafarshi baya daya ɗago da niyar tsalleki ne ya wuce. Cike da shagwaɓaɓɓiyar muryarshi yace haba An mata wai miye kike haka dan Allah ? Ban tashi ba kuma ban daina kallonshi ba nace ba kace sai ka fita ba ? Kai da ƙafafuwan ka ? Tou gani nan kwance ka tsalle gawata kawai kaje abunka na ƙarasa maganar ina zarge hannayena a ƙirjina na rufe idanuwana. {{ hmm taf aradu idan wani namijin ne ba kabarinki ba ko makomarki ya gani sai yayi abinda yasa kanshi can ke ta matse mawa . }}


Cire cingom in bakinshi yayi yana wasa dashi a hannun shi , bayan wani lokaci kuma yayi ɗan latse² a waya ya kara a kunnenshi. Saida na cikin wayar yayi magana Dikko yace Abbakar kuje , ya ƙarasa maganar yana ɗan shan idanuwan shi da suka canja launi. Ey ya faɗa yana komawa ciki. A , a kawai dai na fasa fita ne , kaina yanamin ciwo ya faɗa a dai² lokacin da yake zama gefen gado yana nuna kan nashi da yanayin damuwa. Ey , yayi bacci tun ɗazu. Babu damuwa saida safe. Ya faɗa yana ajiye wayar , ɗayan wayarshi ya ɗauka ya cireta a jirgi , data ya buɗe tare da antaya duniyar yanar gizo.


Saida saƙonni suka fara shigowa ya ajiye wayar ya tashi yana rage kayan jikinshi. Tasowa nayi daga inda nake kwance na matsa inda yake nace yi haƙuri. Ba tare daya kalleni ba yace kawai ya wuce yayi maganar yana komawa inda ya ajiye wayoyinshi ya ɗauka ya koma palo , ƙasa² nayi dariya bayan ya fita a zuciyata nace shegiya ni , na ƙarasa maganar ina kwanciya a gado na ɗauki wayata na fara kiran Hajiya Mai gilashi. Wayarta a kashe har yanzu lallai duk yadda za,ayi in Allah ya yadda sai naje gidanta idan Allah ya kaimu. Allah dai yasa ya barni inje , wani sashi na zuciyata yace kawai cewa zakiyi ya kaiki , wannan shine gaskiyar magana , saukowa nayi daga saman gadon na fita palo inda yake.


Ya toshe ɗayan kunnenshi da abun sauraron magana , ya ƙurawa waya ido yana murmushi. Duk maganar da nayi kwata² ma bayajina sam² , zagawa nayi ta baya da niyar in ɗan riƙeshin nan irin idan mata suka tashi labbatar namiji idan suna san wani abu daga gareshi. Amma kafin in riƙeshi sai me...? Wani irin ruɗaɗɗen ihu nayi tare da faɗar da wayar daga hannunshi. A firgice ya juyo ya kalleni sannan ya tashi da sauri zai ɗauki wayarshi a lokacin har na zagoyo na rigashi ɗauka , bani wayata yayi maganar ranshi a matuƙar ɓace , kyarma jikina ya farayi saboda na tsorata da irin kallon da yakemin. Dakewa nayi tare da cewa idan fa naƙi bayarwa ? Sai in kashe ki............ Ya faɗa yana nuna shaƙewa da hannunshi saman wuyanshi , cike da tsantsar ɓacin rai nace ai yau nice zan kashe ka. Nayi maganar idona yana kallon ƙasa. Wani irin wulaƙantaccen kallo yayi min tare da nuna kanshi nine zaki kashen ? Kafin inyi magana Papy ya shigo yana kuka , ihun da nayi ne ya tasoshi daga koma ina yake yana bacci , cike da ɓacin rai Dikko ya jinjina kanshi ya matsa yaja hannunshi suka fita.


Wuri na samu na zauna na shiga binciken waya. A raina kuma addu'a nakeyi Allah yasa Papy yaita kuka ya hanashi dawowa da wuri , dan abinda na fahimta baya so yanayin wani abu wanda bai kamata ba idan ɗan shi yana gidan. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , wata irin yamutsa kaina yayi da sauri na rufe idanuwana dan irin ƙazantar dana gani , tunda nake da Dikko duniya bai taɓa abinda naji na tsaneshi ba sai yau , wayyo Allahna ? Mayun mata wai ina ruwanku da mijina ne ? Kunzo kun daddaɓeshi sai kace ƙuda ya samu ruɓaɓɓen nama. Ga kira waya sai shigowa yake ba ƙaƙƙautawa , saƙonni sai kokawa sukeyi wurin shigowa , jikina na kyarma idona cike da hawaye na fara neman number Sharifa , dakel na gano ta ɗan iska wai "yar uwarshi ya rubuta a jikin numberta , kam bala'e wai duk ina , ina wannan iskanci ya faru ? Da wata ɓeranyar yarinya shegiya zata girmeni baifi da shekaru biyu zuwa 3 ba , ta ciko mishi saƙon nata itama da ɗanyayen kalamai daɗaɗa , sanyaya , Sharifa kuma ta rubuto mishi cewa ni na kirata na zageta , nayi mata gori wai ni injini ni Sultana wai nice nace wa Sharifa ita karuwan Dikkon ne , a taƙaice dai ita Yusra kaf a cikin kwaratan itace ta saman iska , kaf babu feƙaƙen ɗan tasha na sama a wayar nan sama da ita , guguwar "yar iska ce , dan kalamanta data faɗa tana tattaɓa wasu sansa na jikinta nida kunya ta haifa na rantse da girman Allah ba a baki ba a rubuce duniya ni bana iya rubutawa bare kuma azo fagen in furta. Karuwai.....?׳ hmmm karuwai na sha'aninsu idan suka samu mazajen ballagazanzun mata , a hayaƙe ya dawo saida ya wanwanka min mari ya anshi wayarshi. Cike da rashin tsoro nace kadaiji kunya kuma kayi asara daka kallar da idonka tsiranci haram , naji kunyar kuma naje na kalla haram ɗin naki ne ko nata ? Banyi magana ba na nufi hanyar fita , har na fita zuciyata ta hayaƙoni na dawo ,


Nima dai a daren nan nayi ɗan ƙaramin hauka , haka na rufe idona naci gaba da zage² ba shi nake zagi ba su Yusra nake ta ɓaɓɓarkawa zagi , keda ke gidanki idan kinsan halin da nake ciki Dikko yasan ina nan ko yanajin abinda nake cewa ya basar dani yaci gaba da cht inshi hankalinshi kwance , inda yake saman kujera naje na kamo ƙafarshi na jawo da ƙarfi ina cewa saina faɗar dakai na ƙarya maka kashin baya , da ɗayar ƙafarshi yayi min wani irin kyakkyawan harbi a fuska saida hancina ya fashe. Shi kuma yaci gaba da latse² a wayarshi da yanayin shauƙi , baya nayi inajin juwa ɗakin na gani yana juyamin duniyar tayi shiru banajin motsin komai watan saurarena ya ɗan ɗauke shima numfashin an riƙeshi. Ina dawowa jin sauti na sake tafiya inda yake ina faɗar saina kashe ka , janye wayarshi yayi daga fuskarshi yana kallona da wani irin jarabben kallo , a kasalance yace wai nine zaki kashe....? Ya nuna kanshi , ey , An mata dukana ? Ey , har wannan shima zaki ? Ya nuna daddatsewa da hannunshi , gemunshi kenan , dai² lokacin dana iso kusa dashi , riƙeni yayi da yanayin mayata yace muje saman gado mu kashe kanmu nima saina kashe ki...... Ni ka sakeni , anƙi a sakekin ya ƙarasa maganar yana rufe ƙofofin hancina da "yan yatsunshi biyu , da hayaniya nace wai ba nace ka ƙyaleni ba ne iye ? Shima da irin magana na yace wai bana ce bazan ƙyale ba iye ? Ya faɗa a gajiye yana sauke numfashin jaraba yana min wani irin kallo.


Kwacewa nayi , ya riƙoni da sauri yace ai ƙarya kikeyi yarinya , ina ne zakije ? Sai kin kashe ni..... Ya ƙarasa yana lumshe idanuwanshi tare fitar da numfashi cike da kissa , ƙiƙi² muka fara rigel². Ni ina so in ƙwace , shi kuma yana so ya riƙoni har ya sauko daga saman kujerar , saina tafi , bana sanka׳ na ƙarasa ina ƙara yawan kukana. Ai basai kinsha wahalar faɗa ba nasan wannan shekaru 3 zuwa huɗu da suka wuce. Jana ya farayi hanyar bedroom wai muje in kasheshi. Da Allah ka ƙyaleni kaji , ah ni bazan ƙyaleki ba aradu sai kin kasheni yayi maganar yana murmushi tare da kafe ni da mayataccen kallonshi.


Nanfa abun yaci tura naci gaba da ɓarin maganganu , tun yana kallona har ya fara rufe ido ya sake hannuna. Nan gori ya tashi tunda na lura yana da buƙatuwa dani , haka na warware kamar farfera na ci gaba da zazzaga ranshi mutunci ni matar da za'a sauke buƙata a kaina , ƙarshen film in nace tafiya zanyi , cike da ɓacin rai yace ina ne zaki iya zuwa ? Bayan baki da gidan da yafi wannan ya nuna ƙasa da ɗan yatsanshi na hannu dama , yana ci gaba da cewa kije mana ? Idan kin tafi zan mutu ne ? Ya nuna kanshi cikin tsatsanin fushi mai sa kaji cikinka ya juya na kasa kallonshi , dan kinga ina lallaɓaki ? Idan kinyi haƙuri baki je ba kin zama banza , ki tafi ya nuna hanyar fita , rage murya yayi da cewa ina da dubunki a waje sai me ? Ko an faɗa miki wai bana iya rabuwa dake ne ? Kullum² zakije sai na tafi gidanmu kaza² tou kije ko wani ne ya baki haƙuri ? Hmmm ke baki san iskanci na ba , nafi ki ƙaryar rashin kunya wallahi , inda duk kike zato na tuni na wuce wuri nayi gaba.... Idan kina nan wata zan kawo idan ma kin tafi haka dai zan sake kawo wata.


Kina iskanci ana baki haƙuri tou an daina cewa kiyi haƙuri ki tafi duk gidan da zakije , ba burin daya fi duk macen da bata da lissafi tanayin faɗa da miji tace gidanmu zanje , fuuuu tayi yaji ya nuna da hannu , tou idan baki sani ba babu babban kuskure da yafi wannan jakancin , ko shi mijin dake aurenki bai san kuna da gida ba ? Ai yasan ba a sama kika faɗo ba , ya nuna yana ci gaba da cewa ai ina ganin idan yaso zaice kije gidanku. Mahaukaciya ma dake da Allah , fitarmin daga ɗaki yanayin fushi ya fara hawa kaina kafin inji miki ciwo , kuma na rantse da girman Allah idan kika fita gidan nan ko ina kikaje har can zan biki saina lalata miki fata , kaca² zan miki. Fita nace........................ Ya faɗa yana nuna hanyar fita tare da rufe idanuwanshi cike rashin mutunci. Fashewa nayi da kuka nace yi haƙuri don Allah , zo nan , ya kirani da hannunshi , tafiya nayi ina kuka ina kallonshi. Riƙeni yayi a jikinshi yana sauke ajiyar zuciya bakiji An mata , wai

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads