Header Ads
Showing 6001 words to 9000 words out of 70788 words

Chapter 3 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt

Ads the beginning of article before Image

07 Jul 2024

741

Ads at the middle of Article

nasu ta hanyar gagara fita haƙƙinsu da kuma rashin iya kula dasu a makwancin , ɓangaren sabta rashin iya kalami mai laushi da kuma rashin girmama miji kesa suna fita daga zukatan mazajensu , mtswww nima dai gani nan.... Fita dai haƙƙin iyali kawai shine mafita.


Ɗaure fuska yayi ya fito da fuskar rashin mutunci , baima Yusura magana ba ya wuce tabi bayanshi tana mishi sannu da zuwa , bai tsaya ba bai kuma ansa ba itama bata daina binshi ba , motarta ta koma ta ɗauko wayarta da wata "yar ƙaramar food flarks wai tayo mishi danbun nama....


Da Abbakar suka gaisa shima ba magana sukayi ba hannu sukayi kawai ya wuce , Abbakar shima bayanshi yabi kamar dai yadda Yusra kebin bayan shi , haka yaita gaisawa da mutane sune rufa mishi baya , duk taron mazan nan Yusra ce kaɗai mace da shiga irinta kafirawan da basa zuwa coci , har wurin da Dikko yake zama , daga nan yace kowa yaje kenan zai gana da Yusra , bayan sun fita ne ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa ya gda ? Lafiya qalau ranka ya daɗe ta faɗa tana miƙa mishi kular data zubo mishi danbun , ansa yayi a mutunce tare da kallonta kamar na minti ɗaya , sauke kanta tayi ƙasa tanajin kunyarshi , ɗan tauna cingom yayi sannan yace zauna yayi maganar yana harɗe ƙafa ɗaya saman ɗaya.


Bata zauna saman kujera ba ta zauna ƙasa dan bashi girma , ta fahimci shi mutum ne mai san a girmamashi , su masu kuɗi duk ƙanƙantarsu suna so a basu girma na musamman saboda kuɗi , kuɗin ne kesa musu girman kai , izzar kuɗi kesa suke ganinsu su wasu manyan shegu ne na daban , tou bare Dikko daya raina mutane , gashi da rainin hankali dan idan ya raina maka ƙura babu daɗi , bare su dama Mom insu bata nuna musu sanin darajar mutane ba wanda yin haka ba kyau ba , kawai dai iskanci da rashin kunya a cikin jininsu take.


Buɗe kular yayi tare da cewa ya akayi ne ? Ya maida ya rufe , ba komai ranka ya daɗe kawai dai naji anyi maganar dambun nama ne shekaran jiya da kuna fira sai nace bara inzo maka dashi , ba tare daya sake kallonta ba yace da kyau , bayan wani lokaci yaci gaba da cewa zaki iya tafiya , ba haka taso ba , dole ta tashi ganin shima ya miƙe ya fice , kallon kular tayi sannan tabi bayanshi da kallo tuni ya fice , a waje ta sameshi yana magana da mutane , saida safe tayi musu ta wuce , su Abbakar suka cinye dambun nama , shi kuma mota ya koma yana tunanin girman rashin kunya da raini irin wanda Sultana tayi mishi har 12 tayi , lokacin nayi ya buɗe wayarshi ya fara ansa kira daga mutane daban² , waya biyu kawai ya ansa duk da tarin yawan kiraye²n dake shigowa ya leƙa yanar gizo , a whatsapp saƙo biyu kawai yayi reply , ɗaya na ɗiyar ƙanwar Dady , data turo mishi fatan alkairi da addu'ar samu nasara a rayuwarshi , ya tura mata ngode. Saina wani abokinshi daya ya samu ƙaruwa , yace Allah ya raya , saƙon Yusra kuwa kasa kalla yayi , yana ƙorarin gogewa text in Sultana ya shigo a ɗayar wayarshi.


Dubawa yayi , bayan ya gama karantawa ya kirata , An mata ki kiyayi ɓacin raina tara ki nakeyi karki bari in riƙeki , magana tayi cikin kuka , yanzu me zan miki ne ? Magana ta sakeyi , to wai me zan miki a gidan ne ? Bayan tayi magana , yace da Allah bazan dawo ba , wallahi bazan zo ba karki ɗaukeni ƙaramin yaro mana , ba yanzu kika gama zagina ba ? Ey bazan dawon ba sai 3 na dare , yana faɗin haka ya ajiye waya.


Yauma bai dawo gida ba sai 3 na dare , kuma idona biyu , inajin lokacin daya shigo ya kwantar da Papi ya kashe fitila ya fita , yana fita na kunna hasken , saida na tabbatar ya isa ya shiga wanka na nufi ɗakinshi , wayarshi na ɗauka nabi jerin kira babu kiran mace ko ɗaya kuma shima bai kira ba , danshi dama ba ma'aboci waya bane ba , inbox na koma ban samu ba dan haka na tafi whatsapp na fara dubawa , har cht in da bai buɗe ba saida na buɗe ,


Wayata na ciro daga jikina na fara ibar numbobi , bayan na gama naci gaba bin cht ina dubawa , wata irin zufa ta ketomin ganin hoton mace tsirara aihuwar uwarta a wayar Dikko , kyarma jikina ya fara , da sauri na fara ƙoƙarin turawa a wayata , jikina yana kyarma , bansan lokacin daya fito ba kuma har yanzu jikina bai daina kyarma ba , saida na gama na ajiye wayar , zan fita na ganshi jikin ƙofa tsaye ya rumgume hannayeshi yana kallona.


Baimin magana ba ya taro hannunshi in bashi wayata , ba gardama na miƙa mishi , goge videon yayi ya maidomin wayar tare da bani hanya ya nunamin da hannunshi in fice , ƙin fita nayi ina kallonshi , ya akayi ne ? Ya tambaye ni , cikin kuka nace kadai ji kunya , da yanayin ko a jikinshi yace you sai me ? Ni banji kunya ba kece dai kikaji kunya da kika kasa ɗaukemin idona akan su , yayi maganar yana nunani da ɗan yatsa , to kinga ke kin ɓoye naki , ga na wata nan a wayata , kyauta ta bani ko sisi ban biya ba duk saboda inyi farin ciki , kuma banyi "yar murya ba cewa a taimaka min na gani , bina takeyi na taimaketa na bata abinda ke nake haɗaki da Allah in baki bakya so , to ita ni take haɗawa da Allah in bata ya ƙarasa maganar yana riƙe ƙugunshi yana ci gaba da cewa shin na bata ne ko kuwa kina so ? Tirrrr na faɗa tare da fashewa da kuka , hanya ya sake bani a karo na biyu yana nunamin da hannunshi cewa ai baki fara kuka ba sai amarya tazo tunda ke daƙiƙiya ce , zoki fitar min daga ɗaki.


Fita nayi ban mishi magana ba na nufi ɗakina ina kuka , ɗan gajeren tsoki yayi bayan fitar Sultana sannan yace kyaji dashi , kashe haske yayi yai kwanciyarshi , tunda ya kwanta zuciyarshi ke cewa ya kira Sultana kartaje taita kuka , gyara kwanciyarshi yayi a bayyane yace da Allah ƙyaleta tunda bata da wayau.




Bayan sati 2.


Har yanzu banje makaranta ba , Dikko yayi faɗa harya gaji ya ƙyaleni , dan yanzu ko zai kasheni bana magana , bana tura mishi saƙo , idan dai yacemin inyi mishi kaza , zanje inyi ne , amma bana masa magana kuma bana masa dariya , idan ina palo ya shigo kawai zan tashi ne , ko ina naje idan ya biyoni zan bar mishi wurin idan yayi magana ba amsa saidai in aikata kawai a aikace. Na zamar mishi kurma a magana.


Ita kuma Inna naje wurinta kuma na faɗa mata Dikko zai ƙara aure , tace ni na jiyo kuma damuwar nice wannan bai shafeta ba , a ranar gidan na yini dani da Papi sai 9:37pm na koma gida , yace ina wuta ya sakani ina naje nayi wannan zaman ? Yafa gaji da iskanci na in ajiye mishi ɗanshi in koma daga inda na fito , keda ke gidanki idan kinji shi tou naji abinda yace , cike da masifa yazo gabana ya ɗallarmin bakina da yatsunshi , da sauri na zabura tare da rufe idona saboda azabar ɗallin da naji a bakina, bakyaji ina miki magana ne ? Ban kalleshi ba kuma banyi magana ba , shigowar Papi ɗakin ne yasashi fita yana magana ƙasa² wai zai dawo dana rainashi yanamin magana nake mishi shiru.


Har safe bai dawo ɗakina ba , ni kuma yau na shirya dan zuwa makaranta........








*JAMILA MUSA...*
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_






*KWARATA RETURN...*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_




Rubutawa...
*JAMILA MUSA...*






*SAI NA AURI D ' K*






*ASMA'U ZAYYAN* {{ Asmeenat Xeyyan }}






🅿 ------ 2






Palon ƙasa cike yake da duk wani ma'aikaci dake gidan mace ko namiji gaba ɗayansu hallare suke zaune a ƙasa amma shi mai gidan baya wurin. Duk yadda akayi zaibar ƙasar ne , duk lokacin da akayi irin wannan zaman zaiyi tafiya ne , idan zaije Abuja ko ina ne ba'a haɗuwa sai zai tafi yabar nigeria. Ina ganin haka banma yadda na sauko ba na nufi ɗakinshi.


Da sallama na shiga ya amsa yana gyara ma Papi riga , kusa dashi naje na tsaya ba tare da na sake magana ba , shima baimin magana ba yaci gaba da abinda yakeyi , bayan ya gama yace ma Papi yaje ya jirashi wurin Ashiru yana zuwa , saida ya taɓoni yana murmushi yace kayyalni nayi cau....? Murmushi nayi nima tare da cewa kayi kyau , na ƙarasa maganar ina kallon Dikko dake ta wani haɗe rai , Papi yana fita na ƙara matsawa kusa dashi nace ina kuma zakaje ne ? Rai a riƙe kuma bai kalleni ba yace inda kika aikeni.....


A ɗan tsorace na taɓashi da hannuna na dama ina kallon fuskarshi , da yanayin tsoro nace yanzu kuma meya faru kake fushi ? Ba komai ya faɗa a taƙaice yana matsawa daga kusa dani , ƙara matsawa nayi inda ya matsa jikin madubi yana tattara wasu takaddu , baimin magana ba saida ya ajiye makullin ɗaki a gabana , girgiza kai nayi alamar a , a , to minene ? Cikin rawar murya nace zanji babu daɗi ne idan ka tafi , da gaske ? Ey , kin tabbata ? Na tabbatar da haka , ai bazan daɗe ba ya ƙarasa maganar yana ɗaukar takkadun ya matsa gaban gado ya ajiye sannan ya nufi wurin weldrop , ƙara binshi nayi na fara kuka , har yanzu yaƙi ya kalleni , amma a tausashe yace kinsan ni bana san wannan kuka²n ko ? Yayi maganar yana miƙomin hannunshi. Riƙe hannun nashi nayi shi kuma ya riƙe tare da shigar dani jikinshi. A kasalance yace yi shiru An matana.


Cikin kuka nace to me yasa zaka tafi ne ? Yi haƙuri ai zan dawo in Allah ya yadda , kwantar da kaina nayi saman ƙirjinshi naci gaba da kuka , bai sake magana ba kuma bai ɗagani daga jikinshi ba , yadai cire hannunshi daga kaina ne tun lokacin daya shigo dani jikinshi. Kenan bai rumgumeta ba , saidai a ranshi yaji babu daɗi tanayin kuka , a zahirance kuwa ya nuna ko oho da yanayin ma idan tai mishi ɗanyen kai zai zaneta ba abinda ya dameshi , Allah ya sani yana san An mata kuma yana tausayinta amma ta rainashi iya raini dan ko gaban waye idan ta tashi mishi rashin kunya sai taje inda take so hankalinta zai kwanta , kuma ita rayuwa ba'ayinta haka wannan dalilin yasa shi yaja mata layi ya kuma tsare gida yanzu yasan tsoronshi ya fara hawa zuciyarta. Gashi yanzun ma taji tsoronshi shi yasa ta firgita dashi take mishi magana a tsorace , naso na tambayeshi abinda yasa zaiyi tafi bai faɗamin ba , kuma ince mishi kenan da banga ma'aikata a palo ba saidai inji labari baya nan , tou ya wani haɗe rai cikin rashin mutunci , sauka nayi daga jikinshi bayan nasha kukana harna gode Allah duk na ɓata mishi rigar jikinshi da hawaye , ina sauka ya cire kayan ya canja wasu.


Bayan ya gama ya ɗauki abinda zai ɗauka da wayoyinshi danshi bayayin tafiya da kayan sakawa shi kaɗai ɗinshi yake tafiya saidai ɗan abinda ba'a rasa ba , da ya tashi fita yayi bankwana dani kamar yadda ya saba , ya sumbaceni tare da shafa gefen fuskanta , ya riƙe haɓata yana ɗagota dan mu kalli juna , na kalli cikin idonshi yayi murmushi mai tattare da tsantsar so sannan ya ƙara shafa fuskata ya kama kumatuna da yatsu biyu kamar anayi ma yaro wasa yanamin wani irin kallo , ajiyar zuciya nayi tare da sauke idona wani wuri daban na daina kallonshi , wasa yayi da tafin hannunshi a gefen fuskata { kumatuna }sannan ya fita daga ɗakin ba tare da yayi magana ba. Yana fita na fashe da wani irin kuka mai kama zuciya , yana jin kukan Sultana har a ranshi amma ya daskare yai tafiyarshi.......


Wani irin ihu nayi tare da buga wayata da bango ta watse lokacin da naga kuɗi sun shigo a cikin asusun bankina , kuɗin banza kuɗin wofi ko an faɗa mishi kuɗi nake so ne wai....? Nayi kuka׳ , bana san Dikko yanamin nisa nafi so ya zauna gida muyi ta faɗa.... Duk taron mutanen dake palo suka ɗinguma dan rakiya bayan Dikko ya bulalesu da manyan kuɗi , su Ashiru kaf dasu aka tafi hada Papi.


Sai azahar nabar ɗakin Dikko bayan nayi sallah kuma banje makarantar ba , a ɗakina na haɗa wayata data fashe na kira Mai gilashi , babu wani ɓayata lokaci ta ɗauka , bayan gaisuwa nace ko kirana bakya iyayi kinga kwana biyu bana zuwa makaranta , ai kyace ita wannan lafiya....? Daga haka nayi shiru danjin amsar da zata bani , wata irin dariya nayi sosai dan wata irin ƙatotuwar batsa data sako , jin ina dariya yasa tace bana san iskanci fa sai anjima , ah jira Mai gilashi zaki zo gidana ? Keni fa na faɗa miki bana iya zuwa gidanki , babu munafurci tsakanin ni da kuma ke , D ' K ka haɗa hanya dashi ya maka rashin mutunci ina kuma kazo gidanshi....? Gaskiya ni bana iya zuwa gidan D ' K , baya nan fa , kizo dan Allah , kashe waya Mai gilashi tayi tare da ƙurawa wuri ɗaya ido.....


A bayyane tace gidan D ' K , hmmm....


Kyakkyawan murmushi ta hasko yayin da aka gurfanar da ita a gabanshi , da wannan kallon rainin wayan nashi da yake ma mutane ya kalli Mai gilashi , cike da duniyanci ya ke wani murza bakinshi yana cin cingom cikin salonshi mai ɗaukar hankali , kuma shi bawai dan ya burge wani ko wata ba yakeyi , a , a ra'ayinshi ne yake ci , sai yakeyin abun cikin yanayi mai motsa ma mata hankali , dan ita mace abu ƙalilan yake ɗaukar mata hankali tare da tayar mata dashi , yana da kyakkyawan baki ne , ga gemun daya ajiye kamu ɗaya. Kuma gemun yayi matuƙar martaba mishi kyakkyawar fuskarshi gashin gemun ɗan gazar² kuma gazar ɗin mai ladabi da sheƙi dan ko bai gyarashi ba baya wani duƙunƙune wa ɗin nan yayi kalar ƙazanta ko rashi kyau. Yana da kyakkyawan gashin gemu mai burgewa , sai kuma kyau ya haɗu da gyara , kuma shi gemun nan fa ba dan wata ya ajiye ba. Shima kwalliya yayi ma matarshi An mata dan ya riƙa burgeta tunda yaga gemun yana burgeta dan tana yawanyin wasa dashi idan suna tare. Shi yasa yabar mata dan tayi farin ciki. Ita kuma taunar cingom inshi baiwai taunar hauka yake mishi ba , baya buɗe bakin motsawa yakeyi cikin natsuwa sai salon ya bada wani irin sirrintaccen sirri mai ɗaukar hankalin mace da sa mace taji ya burgeta kuma ta kasa daina kallonshi , kawai dai zataji sha'awar yadda yakeyi , cikin sakata irin tasu ta rigimamin yara yace kece kike san gani na ido² ko ? Ya ƙarasa maganar yana murmushin mugunta , yadda yayi maganar ne yasa ya bata sha'awa dan haka itama mai gilashi tayi murmushi tare da sauke kanta ƙasa tayi shiru.


Murmushi Dikko ya sakeyi a karo na biyu ya ɗauka robar ruwan dake gefenshi yasha , turo leɓonshi na ƙasa yayi kaɗan tare da riƙe shi da leɓonshi na sama yana mata wani irin ƙazantacen kallo , saida taji cikinta ya juya lokaci guda jikinta ya nuna taji tsoro. Ɗan karkace kanshi yayi shima kaɗan da alamar kowa ya fita , da sauri ta fara juye² tabi mutane da kallo har suka gama fita , ya akayi ne...? Ya tambayi Mai gilashi , cikin rawar murya tace yi haƙuri ranka ya daɗe , a , a , kuka ta farayi tana ci gaba da cewa kayi haƙuri dan girman Allah , gyara zamanshi yayi cike da mugunta yana cewa har kin gama gani na ne ? Ya ƙarasa maganar yana mata kallon ɗage , shiru tayi shi kuma yace tou kin fasa ɗaukar hoton dani ne...? Tuba nake ranka ya daɗe , zo nan ? Yayi maganar yana nunawa da hannunshi ta matso gabanshi , matsawa Sa'adatu tayi tana ci gaba da kuka , tashshi { yaji } ya ɗauko cikin wata "yar ƙaramar roba ya watsa mata a ido....


A firgice Mai gilashi ta goge zubar data tsatstsafo mata a fuska ta goge idonta dake ɗigar da zufar

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads