Showing 9001 words to 12000 words out of 70788 words
Chapter 4 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt
hawayen azaba dan tuno azabar da Dikko ya gana mata kamar yanzu ne yake zuba mata yajin , wanda ba kowa ne yaja mata ba sai Sharifa , kuma itace wacce Dikko yayi ma liƙi , kuma Sharifa karuwa ce ta gaban mota amma musulmin karuwanci takeyi , murmushi ɓacin rai Mai gilashi tayi tare da ɗaukar wayarta ta fara kiran Sultana....
Ina kallon kiranta yana shigowa yana fita nima nayi fushi. Murmushi Mai gilashi tayi tare da turama Sultana text , Allah ya huci zuciyarki uwar gidan D ' K kuma Amarya , daga kanki idan dai kuɗin da D ' K zai biya da sunan sadaki ne dan ya auri wata mace , tou ina miki albishir daya ƙare. Kina ciki muna waje , a gida kika san Dikko a waje mune zamu baki labarin ko waye D ' K , kizo makaranta idan Allah ya kaimu gobe akwai labari.
Maƙiyi zai iya mutuwa amma har abadan duniya gaba baza'a daina ba , kamar yadda na faɗa muku karuwanci shine abinda mai gilashi ta zaɓa , to shine cinikinta kuma karuwanci shine sana'arta , Sharifa ƙawar mai gilashi ce ta hannun dama kuma ƙawancen an haɗashi a bariki ne. Sharifa tana alfahari da Dikko da kuma gwamna , ko taɓota mutum yayi sai ta fara burga a waya Yaya D ' K kaza² alhalin kuma ko number wayar Dikko bata dashi a wancan lokacin. Gwamna Yayan Mom inta ne , munyi waya da Yaya D ' K yana saudiyya ko yanzu yabar Madina ya tafi Makka , yaje London ko yana America kullum shine ƙaryar Sharifa idan aka zauna a mutane. Kiran sunan Dikko da takeyi yasa ake santa dan su a ganinsu zata jasu suje wurin Dikko yayi danbe dasu ya basu manyan kuɗaɗe , dan da harkar mata Dikko ya nufa da tunin duniya ya lalace dan zina ƙarshen rashin kunya ce. Kuma ba ƙaramin ɓarar da mutunci daraja da kuma martaɓar ɗan adam take ba , sun ɗauka Dikkon ɗan tsakiyar fili ne ashe ɗan bayan fage ne basu sani ba , suna mishi kallo go ashe back ne basu sani ba , yadda suka fassarashi kuma suka kalleshi haka yake amma iskanci shi da duniyanci da duk wata tasharshi shidai An matarshi kawai yake mawa , kafin ita Sa'adatu tasan Dikko sunanshi ta faraji da rashin kunyarshi.
Sharifa tayi alƙawari wa su Sa'adatu idan Dikko ya dawo nigeria zasuje wurinshi , ita kuma Sharifa ganin Sa'adatu tana san ƙureta yasa ta fara neman faɗa da ita , amma Sa'adatu ta liƙe taƙi zuciya tana dai manne bayan kuma ita Sa'adatun tayi bincike ance mata Dikko yana nan baije ko ina ba , ana haka ne akayi rasuwa can ahalin Maman su Dady , ƙanwar Kakar Dikko ta wurin uwa data aifi Dady , dake ba'a abu dan Allah ƙwai da kwarkwata ƙannen Dady da "ya "yansu suka je ranar addu'ar 3 , anje kara wa Dady , shi kuma Dikko dama baya shiga hurumin kowa tunda ko family meeting da sukeyi shi baya zuwa ba abinda ya dameshi da sabgar kowa daga doki sai mota sai kuma bugun zuciyarshi An mata da tazo daga baya ta hana ma zuciyarshi hutawa da soyayyar ta , a wurin ta'aziyar ne Sharifa ta ratso dubun mutane ta isa wurin Dikko tace mishi dan Allah ya tsaya suyi solfie , idan sunce shi ɗan uwansu ne sai ace ƙarya sukeyi , yadda tayi sakin layin ne sai abun yasashi yayi murmushi Sharifa ta ɗauki solfie kenan yana cikin yanayin farin ciki , wannan hoto fa shine ta maƙale mishi take ta yaɗawa a kafafen sadarwa na yanar gizo. Face buk , Instagram , whatsapp d p inta shine kullum , wannan hoto shine status inta ba dare ba rana , da ƙawaye suka fara mata gori mai hoto ɗaya , sai ta shiga familynsu ta samo hotunan Dikko irin wanda "yan uwanshi ke sassakawa masu numbobinsu suke samu , nan fa tazo taci gaba da kafawa , kuma itace tasa Mom inta ta sama mata number Dikko a wurin Aunty Bilki abiyar zaman Momy kenan , Maman Sharifa kuwa ta faɗa ma Aunty Bilki tana san Sharifa ta auri Dikko bata ɓoye mata komai ba saboda su biyun nan aminan juna ne kuma aminci ake na ƙuryar ɗaki. Gashi kuma Momy bata shiri dasu saboda ta rainasu rainin har na wuce misali , dake taga kishiyarta zata shiga damuwa yasa ta miƙe itama sai anyi auren nan dan Momy ta ƙuntata tunda tasan bata sansu , tana so ayi auren kodan Momy ta gune , da kuma buƙatar ta na daban tunda ba Al ' Ameen , tana so Sharifa ta shigo. Ta nan ne ma kaɗai zata rufe littafin rayuwar Dikko , tayi waje da Momy ta fasa gidan dan Dikko shine ƙaryar Momy da ma duk wanda uwarshi bata gdan.
Itace ta miƙe da gaske tasa Dady yasa Dikko ya auri Sharifa dan tasan Dikko baya tsallake maganarshi , su kuma maza basa gane makircin mata da irin "yar nehun nan , sai akayi ma Dady nehu haɗe da bariki shi kuma ya fahimci hakan abune mai kyau da kuma ƙara martabar zumincin su , shine fa Dady ya tura Dikko yaje wasan ya kuma ƙara da cewa ya riƙa zuwa zance akan lokaci dan su samu fahimtar juna , banda fushi ɗaure fuska kar yayi duka ya zama mai haƙuri da sakin rai idan yaje , Momy kuwa tace masa bata so , amma sai yace ta kwantar da hankali shi bazai riƙa zuwa zance ba , tace ita ba ma zancen ba auren nan ne gaba ɗaya bata sanshi kuma baya yinshi , dan jakanci fa shine ita kuma Sharifar take zuwa wurin Dikko , ko zai kai ƙarfe nawa bai tafi gida ba zata zauna dashi tana mishi fira , da lafazin su dai irin na "yan bariki har akayi mata liƙi , wanda kuma duk karatun Aunty Bilki ne dan itama sai jawo Dikko jikinta take danma shi Allah yasa mishi wani irin hali haka na kamar dai yanajin tsoron mutune , kuma baida sakin jiki dasu , kana iya zama dashi yau kuyi fira yafa sanka amma idan ya ganka gobe ya nuna shi baima taɓa saninka ba kwata² a rayuwa , kai ta mishi bayanin ka yace shifa bai wani gane ka ba , kuma zaiyi wahala ka bashi abu yaci ko yasha ko kuma ya saki baki kamar sakarai yaita maka surutu ko yawan murmushi , wallahi Allah akan Sultana kawai Dikko ya faracin abunda ya fito daga hannun mace a waje kuma daga kanta ya daina , shi kanshi ya natsu yayi nazari tunda yake bai taɓa ganin macen data bashi wahala kamar An mata ba , kuma shima babu macen da tasha wahalarshi a duniya sai An mata , yana santa soyayyar da tunda yake bai taɓa ma kowa irinta ba sai ita , akan An mata ya fara mafarkin mace , kuma itace farkon macen daya bi ya wuce , itace mace ta farko data mareshi ta zageshi taja mishi gemu yayi murmushi bayan ta gama , itace macen data kashe mishi dokin daya fi ƙauna wanda har yanzu idan ya tunoshi sai yaji babu daɗi saboda san da yake ma dokin , itace macen data maida rungumarshi ba,a bakin komai ba , yana san Sultana fiye da yadda tunanin mai tunani baya iya hasasowa amma bata kunya ko kaɗan haka kuma ta rainashi sai babban iskancin data koya yanzu na raba shinfiɗa dashi , ya ƙyaleta ya kuma zuba mata ido bawai dan baya san su kasance taren ba a , a saboda cikin da take dashi ya ƙyaleta dan idan ya riƙeta da fushi tou fa lallai za'ayi ɓarna. Yana addu'a ta sauka lafiya zataci ƙaniyarta idan ya riƙeta a ɗaki.....
Sa'adatu kuwa wani abokin barikinta ne ya haɗata da Yazeed , Yazeed shine ya kaita wurin Dikko bayan ya biye allonta shima { danbe }, daya faɗa mata ranar da zusu wurin Dikko shine take faɗa zatayi hoto da Dikko idan suka haɗu. Kuma tayi mishi shirin hana bacci , yau duk wasu musu ƙaryar suna tare da Dikko suma zasu je wurinshi kuma zatayo hoto dashi , Sharifa ce ta bawa Dikko labarin zuwan Sa'adatu wai akwai wata karuwa tana faɗa a gari zata zo tayi mishi fyaɗe , abun ya bashi dariya amma baiyi ba a gaban Sharifa saida ta tafi , yaso yaba Sultana labari amma daya koma gidan tai² mishi ɗanyar ƙwalwa , shi yana so ko abu ya faru dashi , ko ya gani , ko yaji yana so ya riƙa faɗa mata suyi farin ciki tare amma ita kwalwarta tana kallon ƙasa , ita kuwa mai gilashi tayi alƙawarin miƙewa tsaye da ƙarfinta da barikinta da tasharta sai ta rama abinda Sharifa tayi mata dan raba tarayyarta da Dikko kamar yadda ita Sharifa ta zuge wani mai san ita Sa'adatu ya fasa aurenta tou itama ta lashi bala'en hana aurenta da Dikko ko da kuwa hakan zai zamar mata silar barinta duniya , wannan kenan.
Kamar wasu mayu haka suke ta yayam² suna cin shawarmar da Yazeed yasa aka basu , Jiddah ma data zo yanzu an bata nata kasafin itama ɗayar mayyar ta lashe. Bayan ta gama ci ne tace ma Yazeed wurinshi tazo fa , babu wani damuwa yace ina saurarenki yayi maganar yana bata umarni da hannunshi tayi magana , kasan dai komai yana buƙatar sirri ba , cikin matan ne wata tayi katsalandi cewa ba buƙatar sirri a wurin nan malama faɗi abinda ya kawoki basai kun wani tashi ba , ke bake a maganar nan dan haka tsamewa mutane baki , Jiddah ta faɗa. Idan naƙi kuma ? Sai jikinki yayi tsami , umarni karuwar ta bayar cewa jikin Jiddah ya tsamama yanzun nan. Dakatar dasu Yazeed yayi ta hanyar miƙewa yacewa Jiddah suje , a motar Jiddah sukayi masauki dukansu.
A hankali ya turo ƙofar ɗakin kamar ɓaron tsakar dare a barikin sojoji , ƙiyyyyy ƙofar tayi ƙarar buɗeta a yayin daya fara tura ƙofar dan shiga cikin ɗakin. A tunanin shi tayi bacci amma da mamakinshi sai ya ganta zaune gefen katifa tana ta shafa wayarta mai tambarin apple a bayanta. Cike da ladabi ya takure daga bayan ƙyaure ya durƙusa cikin biyayya sannan ya matsa gaba kaɗan ya ajiye mata ledar daya shigo da ita da kuɗi cewa ranki ya daɗe gashi. Hankalinta yana saman wayarta tace masa nawa ne ? Cikin rawar jiki yace dubu biyar ne... ! Bakaji me nace maka ba ? Kiyi haƙuri dan girman Allah wallahi har rance na nema a daren nan ban samu ba , shiru tayi ta manta ma da yana cikin ɗakin taci gaba da sabgar gabanta a waya......
Yazeed barka da dare , barka dai matar mai gida , kanta taji yayi mata wani irin gingime cikin izza da nuna ita wata shegiya ce tace , am Ya Yazeed meya haɗaka da Ya D ' K , shiru yayi na wani lokaci sannan hawaye ya gangaro mishi daga idonshi yace , hmmm dare ake bi a samu suna , inko ba'sha dare ba asha rana , idan kikayi duba mutum biyun nan basa sabgoginsu da rana ko safiya , daren nan dai shine suke bi su nema kuma sun biɗa sun samu , kiyi tunani duk ɓarowa sai dare yayi yake fita dan haura katangu , masu nema wurin ubangiji idan dare yayi su lokacin garinsu ya waye , zasu kasance ne a saman abinda sallah suna Allah ka yafe mana ka bamu׳ , shin ko kinsan dalilin yasa D ' K yake huɗɗonshi cikin dare ne.....?
Kai kunnamin hasken can kaji , jikinshi yana ƙyarma ya tashi duk ya haɗa uwar zufa kamar manomin da ruwan damina ya ɗauke a lokacin da gero ya fara bininiy , duhu yabi ya lalubo makunnin fitila dan tunin duniya ta ajiye wayarta haka ne yaba duhu damar gauraye kaf ilahirin girman ɗakin , a kiɗime ya kalli Sa'adatu bayan haske yazo , cike da tasha tasu irin ta "yan tasha ta buɗe jikinta gaba ɗaya , idonta na dama ta kashe mishi cikin salon jan hankali , ha... Ya sauke ajiyar zuciya. Wasu wurare ta nuna masa a jikinta tare da bashi damar zuwa kusa da ita , tafiya yayi kusa da ita ya durƙusa ƙasa ƙiƙi² ya hunce ita kuma ta bashi damar tattaɓa jikinta itama tana tayashi da shashshafa mishi wasu mahimman wurare a jikinshi dan tabbatar mishi da martar cewa shima namiji ne. Kaɗan ta ɗan lulashi saman network saida ya tafi ya kusa cinma nasara tace dubu biyar ya ƙare , dan haka ta saukeshi daga saman katifarta ta mayar da kayanta sai ya kawo cikon dubu biyar zai shiga gabatar da wasan danbe...... Wani irin gurnani yayi tare sake nufa inda Sa'adatu take yana wani irin huci kamar an jiƙa mahaukaci a lokacin sanyi , dakatar dashi tayi ta hanyar cewa idan ka haumin katifa saina yaga mutuncin ka , ni nafika ƙaryar rashin kunya iskanci tasha da kuma lalacewa , tattara gashin kanta tayi cewa bani kazar inci...... Ta ƙarasa maganar tana ɗaga mishi gira. Kamar wani gele haka ya miƙo mata , yagar kazar ta farayi saida ta cika bakinta da ita sannan tace tou yi sauri kaje ka samo cikon kuɗin ka kawo ni kuma na ɗoraka a saman lambar girma tayi maganar tana murmushi tare dakai hannunta ta nuna mishi tsakiyar filin wasan danbe...... Bashi da yadda zaiyi dole ya maida kayanshi ya fita daga ɗakin dan yasan tashar Ade mai gilashi ta girmin tunaninshi.
Gyara zama Jiddah tayi ta kalli Yazeed sosai sannan ta tambayeshi kamar yadda ya tambayeta itama tace me kuwa yasa yake huɗɗonshi cikin dare....... ? Yazeed yace shine abinda nake so na sani tun farko kenan dan duk yadda akayi nasarar rayuwarshi a cikin dare take , kinga D ' K baya waya da rana saida daddare idan kika cire wasu ƙalilin mutane wanda su wayarsu ma daban ya fitar musu , uwa uba matarshi sai Ashiru danni tunda Ashiru ya wulaƙanta ni ya korani daga company ya kawo Abbakar bana samun layin da nake kiranshi dashi da rana ko safe duk dai lokacin dana so nayi magana dashi. Jiddah tace nima yanzu ko na kira saima acemin number ma babu ita a duniya saida na sameshi a layin da kowa yake samunshi , idan kuma na saka number a wani waya shima dai baya tafiya wai meya ɗauki mutane ne.... ? Jiddah tace koma meya ɗaukemu zamuji mu kuma gani idan na koma gidanshi.
Wani irin kallon raini Yazeed yayi mata mai nuni da tama samu warwarewar tunani , ita kuma tana ci gaba da cewa manta da wannan damuwar kaji abinda ya kawoni wurinka , inajin ki ya faɗa bai sake kallonta ba , hoton Sharifa ta nuna mishi tana ce masa kasanta ne ? Kallon hoton yayi sosai sannan ya miƙawa Jiddah yace ya akayi ne ? Yaya D ' K yayi mata liƙi kuma aurenta zaiyi , kai tsaye Yazeed yace wallahi D ' K bazai aureta ba , ke kina wasa da Dikko ko ? Tou D ' K mashaune shi ɓadda musulmi , shi kanshi tsoron kanshi yakeyi kuma bai yadda da kanshi ba , ita wannan yarinya da kike magana yanzu haka tana wurinshi Abuja taje mishi rakiya zaiyi tafiya. Jiddah tace zai aureta , Yazeed yace bazai aureta ba , haka sukayi ta maimaitawa kusan sau goma , shi Yazeed yace Dikko bazai auri Sharifa ba , Jiddah tace zai aureta , daga ƙarshe dai suka rabu a haka kowa yana cewa zaka gani , shima yace mata zaki gani.....
A wahalce ta ajiye kwalbar cikin maye tace wallahi saina auri D ' K , wata irin dariya Amisty tayi tare da cewa Dikkon ne zai auri "yar shaye² ? Cikin maye tayi magana cewa tsaya kisha kallo...... Dariya Amisty ta sakeyi tare da cewa me kuwa zan kalla saidai inga yadda zakici ubaki , murya a lalace da maye Hafsa ta nuna Amisty da ɗan yatsa tana rufe ido da yanayin buguwa murmushi ɗauke a fuskarta tace kema kina layin "yan hassada ko......? Tayi dariya. Tou dama malam ya faɗamin "yan hassada zasu fito ɗaya bayan ɗaya ngode ma Malam daya nunamin ke Kaka , ashe haka kike hassadata ban sani ba ? Gaki nan Malam ya zaƙulomin , buɗe tafin hannunta tayi tare da nuna ma Amisty tace me kika gani ne ? Wata irin ƙatuwar ƙuna ce a tafin hannunta , bayan ta tabbatar Amisty ta kalla ta naɗe hannun da tsumma kamar yadda yake farko cewa malam yace wannan ƙunar sai a gidan D ' K zai warke , ta ƙarasa maganar tana dariya irin ta mashaya......
Da massara ya isa Abuja shi yasa tunda ya shiga ciki bai fito ba yana kwance a gado jikinshi har ƙyarma yakeyi , saida yayi sallah isha'e yasha magani ya koma bargo. Ba tare daya juya bayanshi ba yace Papi tashi ka kawomin wayata ana kirana , sauka yayi ya ɗauko wayar ya kawo mishi , samin a kunne na yayi maganar yana kallon Papi , yadda yaga anayi idan za'a ɗauki wayar yayi tare da ɗorawa a saman kunnen Dikko shi kuma ya fara magana , bayan gaisuwa yace wallahi banajin daɗi ne Momy , magana tayi sannan yace a , a , shiru ya sakeyi bayan wani lokaci yace gaskiya ban sani ba. Ey Papi Momy zatayi magana dakai , cire wayar yayi daga wurin Dikko ya kara a kunenshi yana magana da tsantsamar muryarshi