Header Ads
Showing 57001 words to 60000 words out of 70788 words

Chapter 20 - KWARATA RETURN BY JAMILA MUSA.txt

Ads the beginning of article before Image

07 Jul 2024

760

Ads at the middle of Article

Gayam². Gurum² taunar nama. Abinci kuma nakai karo suka ci gaba da surutu......


Da hada "yan gidan Baba ƙarami zamu zo sukace basu zuwa. Cacai² gardama ta buɗe , bafa haka sukace ba ku faɗi gaskiya ni nafi san abinda mutum ya faɗa ana faɗinshi. Daga maida magana sai faɗa , har ana neman bugawa. Haƙuri na basu dakel dai suka haƙura , duk lemunan da aka kawo musu kowa cikin jakarta tasa abunta wacce bata da jaka ta matse abunta a hannu. Tashi sukayi wai zasuje su zagaya gida dan kar suje wata rana anayin labari su kasa ƙarda komai. Kamar wata geliya haka nabisu babu inda basu shiga ba a gidan sai ɗakin mai gidan ne kaɗai basu shiga ba. A store kuwa buhun garin kwakin nan suka jawo , kalluba suka cire ba tare da izinina ba suka hau rabo , wai wannan ai kiran tsiya ne wai meya kawo fir'auna aljanna ga gidan wuta. Haka dai sukai ta zambaɗa iskanci suna maganganun irin nasu na "yan cikin lungu. Duk abinda suka gani yayi musu a store sukayi gaba dashi. A ɗakina kuwa cewa sukayi in basu zazzagar kayan sawa. Fa'iza kuwa cewa tayi saidai wasu a basu kaya wasu takalmi wasu jikkuna , kuma wai waye ma nake bawa kwance gasu ? Duk zasu sakamin numbobinsu idan zamu koma sabon gida a basu kayan tsohon gida , weldrop na buɗe na fiddo musu kaya sukai ta zaɓe. Ciki kuwa hada rigunan da Dikko ya kawomin tsaraba suka ɗauka. Nan dai suka yini sai dare suka tafi nayi musu hasafin kuɗi masu nauhi suka kama gabansu....


Kwanan "yan gidan biyu da zuwa Dikko yana kallon hutana na a waya ya karkatomin waya wai insa mishi wannan rigar yau. So ɗaya na kalleta nace na bada ta. Sake zuƙo hoton yayi yace wannan kalli. Ba tare dana kalleshi ba nace wannan ɗin. Haba yarinya wasa kikeyi , wallahi da gaske na bayar da ita , cike da ɓacin rai yace waye yace kika bayarmin kayata...........?


Kar kuji Dikko yana da kuɗi kuce ya tsaya akan wani banzar riga yana surutunshi. Duk iya kuɗin namiji ke mace yafa kamata da Allah ki riƙa abu da lissafi. Tunatarwa ne. Duk irin kuɗin mijinki baifa kamata haka ba gaskiya , ta yuwu kila a jikin wata ya gani tayi mishi kyau ya siyo shima kiyi mishi gayu. Bawai nace ba'ayin kyauta ko karki bayar a , a abunda dai ina nufi a ɗan riƙayinshi haka dai da lissafi.


Domin shidai Dikko a saudiya yaga riga jikin wata "yar budurwar balarabiya. Shine ya hasko idan tashi matar ta shiga a irin rigar itama zata bada irin abinda waccan ta bayar , ina fatan dai kun ɗan fahimceni. Shine ya shiga shima ya samota kalarta da komai da komai dan ayi mishi ado a gidanshi shima. A ita ga matar mai kuɗin banza idan na bayar gobe ya siyo wani. Ita ya siyo domin ke..., bashi da tabbas idan ya koma siye ya samo irinta , ta yuwu a canja kala ko kuma a samu banbancin company. Shin ba'a shiga haƙƙi ba....? Saboda haka idan dai namiji ya siyo abu ya kawo miki lallai yana da dalilinshi......


Ai na baka ya rabaka da abunka. Ni kike faɗama wannan maganar dan kin ɗaukeni abokin wasar ki ? Yayi maganar cikin fushi yana tashi zaune. Ni zan siyo miki abu ki bayar dashi ? Nayi miki magana zaki faɗamin na baki ya rabani da abuna....? Yayi maganar yana saukowa daga saman gado , miƙewa nayi da sauri. Cikin firgitacciyar murya yace idan kika fita sai nai miki shigar bulet.........

































08/02/2020


















*JAMILA MUSA...*
[2/14, 12:12] ~M K: ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_






*KWARATA RETURN...*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_




Rubutawa...
*JAMILA MUSA...*






*SAI NA AURI D ' K*






🅿 ------ 10




Shafin nan daga farkon shi har can² karshenshi. Sadaukarwa ne gareku "ya "ya masu albarka.
*ABDULRAHMAN B ' K LAWAL*
&
*JA'AFAR B ' K LAWAL*


Ina roƙar Allah subahanahu wata'ala da ya albarkaci rayuwarku. Ya jiɓanci lamurranku ya jiƙanku ya ɗaukaku darajarku yasa ku gama da duniya lafiya. Ina roƙon ubangiji da yasa kuyi kyakkyawan ƙarshe. Allah ya dafa muku ya kareku da kariyarSa , ya tsareku da tsaronSa a duk inda kuka shiga yasa albarka a rayuwarku ya ƙulle idanuwa da zuciyoyin duk wani gurɓatacce daga gareku. Allah yasa ku dace a gidan duniya da ƙiyama. Allah yai muku albarka don darajar fiyayyen halitta Sallallahu Alaihi Wa'alihi Wasallam. Ameen ya Allah. Duk mai san manzan Allah S. A. W yace amin..... Duk wanda yace amin , ya Allah kasa ya gama da iyayenshi lafiya. Idan kuma sun rigamu gidan gaskiya Allah ka jiƙansu ka sadasu da rahmar ka , kasa can ya fiye musu nan har Babana.... Allah kasa sun huta. Mu kuma ka kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo Amin.






Idanuwa na cike da hawaye nace ai dama ba fita zanyi ba haƙuri zan baka. Na ƙarasa maganar ina ƙoƙarin durƙusawa ƙasa. Tausasa murya nayi cike da ladabi na furta kayi haƙuri insha Allah bazan sake ba. Komawa yayi ya zauna danshi yana da karyayyar zuciya , ko yana furta sai na kasheki.......... Saina kashe² idan dai zanyi kuka ko yaga na ɓata rai zaice An mata bakijin magana kaza². Da lallausar murya ya furta gaskiya banji daɗi ba. Kuma karki sakemin irin haka daga yau...? Nace tom. Duk abinda ni nawa ne ? Idan dai har nine na siyoshi da hannuna koma miye ko mene ne ko wane iri ne karki kurkusa ki yanke hukunci ba izinina na faɗa miki. Na sake cewa tom. Ni kwanaki da zan aske ya nuna gemunshi ba kuka kikayi ba ? Shiru nayi ina kallon ƙasa kamar mijin da matanshi suka ritsa a ɗakin "yar aiki.


Ke me yasa kikayi kuka ? Cewa kikayi in rufa miki asiri ko ni ina so idan kika ga masu gemu kiyi ta kallonsu ne ? Cikin ɗaga murya yace tou da irin wannan dalilin da zaisa ki kalli wani mai gemun a waje , tou nima irin wannan dalilin ne yasa na siyo rigar nan. Ko an faɗa miki niba mutum bane ba ? Ance miki ni nawa idon bai iya kallon mata ba ? Ko an faɗa miki ni banajin irin yadda kike ji ? Ko an faɗa miki niɗin dutse ne ni da banajin yanayi a jikina iye ? Ya faɗa yana nuna kanshi da ɗan yatsa. Tou irin abinda kikeji idan kika kalleni da yanayin da kikaji idan kika shafa fuskata ko kika zo kika rumgumeni , duk irin yanayin da kikeji idan kina shashshafa ko ina a jikina ni nafiki na wuce na zarce ki jin irin wannan yanayin. Ko sai ke kaɗai kike so a burge ki ? Wannan ai rashin adalci ne, zalinci ne. Ji nakeyi kamar ince miki ban yafe ba. Fashewa nayi da kuka nace Allah ya isa zakayi min ne ? Cikin ɗaga murya yace dan in nuna miki girma da ciwon da naji wallahi akan bayar da rigar nan da kikayi ? Yau da kin sameni akan tsini duk wanda ya tsaya miki da sai nasa kin anso rigunan nan.... Cikin shashshekar kuka nace dan ci baya ? Kece kika ci baya mai shiga haƙƙi miji. Har wasu banzaye sunfi mijinki mutunci , "yan gidan namu ne banzaye ? Suɗin , duk wacce kika gani a cikinsu idan ta dafe kan mijinta shiru zakiji. Irinki ne masu duhun tunani mutane ke rabawa da miji. Kila ma kin basu labarin ni na siyo sai su ɗauka , ke baki iya sakawa su bara su riƙa sakowa suna burgeshi , kina can kwance kina yarinta za'a buga wasan a barki da hauka. Idan ma kika ɓatamin rai na hasala da yawa duk shegiyar dana sake gani a gidan nan saina bata kashin bala'e. Me yasa nake baki kuɗi ? Dan kiyi rayuwarki karki shigamin rayuwa kije kiyi huɗɗarki da mutanenki ko na hanaki ? Ko nace karkiyi ? Ban takura miki ba ban shiga rayuwarki ba An mata , na barki kiyi sabgar gabanki dan kema ki zama mai "yan ci kamar yadda ko wane ɗa yake da "yanci , amma kin ɗaukeni kamar wani lusari ko an faɗa miki tsoro yasa na barki kike abunda kika ga dama ne ? Bana san na matsa miki ne ke kanki idan na takura miki rayuwar gidan nan bata miki daɗi. Nawa ne ba naki ba.


Ko kayanki ne ba nawa ba iye ? Ke kika siyo su ne ? Nine na gani ya burge na siyo domin ki , ki saka nima inji shauƙi inje irin yanayin da kike shiga idan kika kwanta jikina , ke wai bakya gane komai ? Komai sai an fito ɓaro² an fallasa miki saboda kina da jakin kwalwa. Da kinga na fara sauke²n kaya baki da zama lafiya. Kar in bada miki wannan , kina so kiga na saka wannan , ke wannan yana miki kyau. Ko nace bana sanshi sakani gaba kike kitaimin kuka ke mai idon fitar da hawaye. Shin yanzu ke ba da kanki kike fidda kayan dake baki ra'ayinsu nawa ki bada su ? Duk yadda nake san abu idan kika ce baki sanshi dole haƙuri nakeyi dashi. Duk yadda bana san abu idan kika cemin kina so haƙuri nakeyi. Sanyaya murya yayi yace duk dai dan in burgeki. Amma da yake baki da adalci babu abinda ya dameki inyi farin ciki ko kishirya haka. Ki burgeni ko karki burge kedai kanki kika sani burinki in miki kiji daɗi. Wannan shine rayuwar farin ciki.....? Ya ƙarasa faɗa yana kaiwa katifa duka , baki da adalci sam² kullum baki da burin burgeni saidai neman hanyar musgunamin. Tou daga yau tunda iskanci ne abun naki na rantse da girman Allah kika sake ɓatamin rai saina lalata miki fata.... Tom. Zazzaro ido yayi yace karki cemin tom akan komai kice bazaki ƙara ba.......... Ya faɗa yana rufe idanuwanshi. Da sauri nace bazan ƙara ba insha Allah. Hanya ya nunamin in fitar mishi daga ɗaki. Da sauri na fice na barshi yana ta mita.....


Tsaye take a kitchen tasha ado kamar zataje gasar wanka sai fitar da wani irin sirrintaccen ƙamshi takeyi. A gabanta kuwa kiret in kwai ne take ta dandaƙa ba sassauci. A gefenta kuma "yar matsadiyar wayarta iphone ce keta rero waƙoƙin turanci ita kuma tana rakiyarsu da bakinta. Wata irin zundumemiyar ashariya Yazeed ya ciko bakinshi da ita ya zundumawa Jiddah dake ta farfasa kwayaye....... Wandon jikinshi kuwa sai riƙonshi yake a hannu yana ƙoƙarin ɗaure belt dan wandon ya tsaya. Kuturmar dumadu.....? Kwan zaki cinye dan uwarki...... ? Waye yace miki anacin ganyen filawar da aka jera dan ƙawata ƙawar gida ? Cike da masifa Jiddah tace kai kaima dan uwarka ! Ko an faɗa maka shiru² tsoro ne wai iye ? Idan baka so inci kwai kawai ka bani sakina inyi gaba ai muma a gidan namu anacin kwan. Cike da ɓacin rai Yazeed yace kin taɓa ganin majiyyaci a maƙabarta ? Ai asibiti shine majiyyaci yake zuwa dan ganin likita , shine zai dubashi ya gano ciwonshi ya bashi magani sai ya samu waraka da izinin Allah. Maƙabarta kuwa gidane na matacci , wannan gida da kika ganshi nahir jinyace daga gareni idan kuwa har kika fita a gidan nan gawarki ce aka fidda. Ni bana aure dan saki saidai inci uwar fatar mace tai iskanci. Aurena yana nan ram² baya girgiza no saki an no barkono yaja yaji da bakinshi. Ni nan da kika ganni matakin iskanci na taka bansan iyakar nahiyoyin rashin kunyar dana ƙyetara ba. Ɗan iska ne ni na nunawa a satilayit banda mutunci ga muni banda kyau ko nai wanka..... Da ke a tunaninki na aureki domin kisan wuta ? Nine ma zaki kashe wuta dani ? Tou yanzu na kunnu nayi ta ci gaba da ci daga nan har a tsaida ƙiyama. Bana sanyi bana siƙewa bare kuma kiyi tunanin zan mutu.


Ai wannan auren ko auren da aka daura a coci bai kaishi ƙarko da aminci ba. Yaci uwar auren coci ya zarta na kotu kuma. Yadda bakya tunani auren ya wuce inda kwalwarki bata iya hasasowa saboda ya linka auren zobe dan auren Yazeedu auren kabari ne. Kuma haka gidana yake idan an shigo ba'a tafiya saidai idan za'a tafi kabari , nunawa yayi da hannunsa yana ci gaba da cewa wannan nasan zahiri ne tafiya ɗaya ba dawowa. A bakin tarihin rayuwarki waye kikaji ya shiga cikin ramin kabari ya fito ? Tou ba'a fita sai ranar da ƙiyama ta tsaya , wato ranar yauma tubalasra'il. Ranar girbe abinda ka shuka , ranar da uwa bata gane ɗanta miji idan yaga matarshi zaisha kwana. Tou gidan nan maƙabartarki ne a nan kabarinki yake idan kinga kin fita a gidan nan mutuwa kikayi dan ƙaniyar iskanci. Ya ƙarasa maganar yana shaƙe wuyan Jiddah tare da cewa biyamin kwai na....


Yana shaƙe da ita yaci gaba da cewa shin bana faɗa miki abincin gidana adon idon duniya ne ba ? Dakel tace e , Yazeed yace amma kika ce kinji kin yadda ko ba haka nayi dake ba ? Cikin jin zafi shaƙa tace haka ne. Riƙe wuyanta yayi da hannu ɗaya yace duk kwai ɗaya dubu ɗaya na siyo abuna. Kuɗin mota da kuɗin kunna gas a gidana ba ranar sanwa ba. Bakina dana ɓata wurin ciniki , kin yanka albasa ba'a kan ƙa'idar ma'ikata ba. Zagin miji wanda babu shi a kundun tarihin musulci zunubi ne mai girma , domin wanke kai daga wutar Allah neman gafara da biyan kuɗin diyya dubu ɗari. Cin zarafin miji kin daƙile min guyuwa akan ƙalubantar ciyarwa kince gidanku akwai abinci. Domin samun sassauci kwanciyar kabari cikin salama zaki biya dubu hamsin domin wanke kai daga bugun mala'eku. Naira budu tamanin na neman yafiya ne domin kiyi kwanciyar kabari cikin salama. Da hannun da bai riƙe wuyanta ba ya fara lissafun kuɗin a wayarshi.


Yana lissafa kuɗin yake cewa yau kuma anyi buking ina a wasan danbe ki biya kuɗinki da wuri ki yanki tikiti tun kafin ƙarfina ya ƙare. Ki bada budu goma tunda ke ta gida ce , zan siyar miki dashi ne akan farashi mai sauƙi amma ba haka ake siyarwa ba dan kada jibi ince miki dubu talatin ki fara wallahi² , cikin wahalalliyar murya tace bana so. Basai kinyi muradi ba kuɗin gado da katifa na yafe miki tunda ke matar gida ce. Kuɗin kwai naira dubu talatin. Cikin kakari Jiddah tace ai ba duka naci ba , damuwarki ne wannan inji Yazeed yaci gaba da cewa + naira dubu biyar ta-ra akan kin tari numfashin miji yana magana kina sako mishi baki..... Duka abinda kuɗinki suka kama dubu ɗari biyu da tis'in da biyar , amma ɗari 3 zaki bayar hada ladar lissafi dubu biyar , ya ƙarasa maganar yana sakin wuyarta ya turata can baya. Riƙe wurin daya shaƙa tayi tana ta tari , ƙuhul² kamar sakin mayu.


Wai wannan wane irin zalinci ne ? A fusace ya nufi wurinta ya ɗaga hannu yace zan....... Da sauri ta duƙe. Wayarta ya ɗauka ya miƙa mata tare da cewa maza inji alart. Jiddah na kuka tayi ma Yazeed transfer. Dariya yayi bayan yaga tabbacin kwanciyarsu a asusun bankinshi ya rumgumeta yana sumbatar ta. Ina sanki haɗaɗiyar matata abun alfahirina bugun zuciyata , gaskiya yafa kamata azo a ƙulla hanyar neman wasu kuɗin kafin asusunki yayi shiru , ya faɗa yana fita daga kicin in sweetheart kisha shagalinki lafiya , lambar lokacin ki shine. 0 3 4 9 am. Wato yana nufin lokacinta da zai bata na katin danbe da ta siya shine 03:49am ya yada mata katin yayi gabanshi....... Kuka Jiddaah tai tayi tana Allah ya isa. Saida tasha kukanta har ta gode Allah ta kira Nabeela ta rattafa mata komai tayi ƙari akan abinda yayi mata ta kulle da cewa kuma yace baya sakinta. Abunka da ɗan uwa Nabeela taita kuka ta kira Rabiya ta faɗa mata. Rabiya ma taita tsinewa Yazeed wai zata faɗawa Dikko wallahi sai an kaso auren nan , yasan ashe Yazeed tsinannen Allah ne yasa aka haɗa auren saboda cuta irin nashi kaza² , taya Yazeed zai kulle yarinya a gida ba abinci yana bata gwale² sai duka ? A yinin ranar haka sukai ta yaɗa magana tsakanin su "yan ɗakinsu.


Daga baya suka bawa Jiddah haƙuri tare da tura mata kuɗi ta siya abinci kafin a samu mafita saifa Yazeed ya sakota ɗan iska mara mutunci anyi masa rana zai yiwa mutane dare. Rabiya da kanta tazo har gida taba Dikko labari , mugu yaji mugunta yasha dariya harta zarce musali. Saida yasha dariyarshi sannan ya turawa Sultana saƙo tazo palonshi , bayan naje yace Rabiya ta maido labari baya. Ran Rabiya kuwa ya hayaƙa taita zagin Dikko , waishi wane irin ɗan iska ne ? Ta faɗa mishi ciwo yana ta wata dariyar iskanci ? Cikin dariya yace bakinki ko nawa ? Fuuu Rabiya tai zuciya ta ɗauki jakarta , Dikko yace Hajjaju tsaya da Allah

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads