Showing 54001 words to 57000 words out of 65672 words
Chapter 19 - A ZURI'AR ARAB COMPLETE BY MHIZ INNOCENT .txt
nata sannan ta tsugunna tana dora kanta akan qirjinsa
" Baby ka yafemin don Allah, ka tashi ka farka Ina sonka !! ina qaunarka baby, don Allah ka farka haka nan " ta qarasa fada tana fashewa da wani kuka me tsuma zuciyar me sauraro tana sake qanqame tattausan hannayen nasa
Taku taji a bayanta alamar shigowae mutum kenan, dukda taji takun hakan be hanata dagowa ba, ta cigaba da kwanciyarta kan qirjin nasa
Ya qaraso yana harde hannayensa a qirji sannan yace
na
" Ya jikin nasa ?
Se a lokacin ta dago a hankali ta sauke dubanta akan fuskarsa
Yana nan dae kamar yadda ta sanshi a barrister souban dinsa
Seta dauke kae tana lumshe ido akan Arman tana budewa a lokaci guda sannan ta maeda dubanta kan souban sannan tace
" Alhamdulillah "
" Ae tun dazu na shigo dakin amma naga ba kiji shigowata ba saboda kin shiga soyayya " ya fada yana murmushi
Se taji kunya ta kamata dan haka ta murmusa tana sake kallan Arman din
" Allah ya qara afuwa " ya fada yana ficewa daga dakin
Seta sake komawa wajen Arman din dan yadda takeji yau din kamar tayi ta zama a jikinsa, hak kawae taji tana enjoying hakan .
**Bayan fitowar souban daga asibitin kae tsaye police station ya wuce inda aka kae wadanda suka janyo hatsarin Arman din
Sanda yaje ba'a kae ga sakasu a cell ba ana dae tuhumarsu ne
Wani dan sanda wanda ya fusata da lamarinsu yace
" Wlh za'a wuce daku court ne kae tsaye tunda an riga an kamaku red handed kune kukae causing wannan accident din "
Black ya juyar dakae yace
" Mufa bamu bane muka aekata laefin nan ba "
Wani daga cikin en sandan da shigowarsa kenan ya tsinci maganar da suke yace
" How dare u zakuce baku bane ? Ko akwae wani abun da kuke son fada bayan wannan ?
Black yace yana kallan dan uwansa
" Mufa sakamu akayi bamu da hadi da mutumin ma "
" Oh yah fada mana wanene ya sakaku ?
Dae_dae lokacin da souban ya qaraso cikin wajen idanunsa suka sauka akansu black wanda shima ya dago idanunsa suka hada ido da souban
Take a lokaci guda jikinsa yayi sanyi, toh tunda dae yaaga lamari na neman ca6ewa gwara ayita ta qare, dole su fadawa en sandan nan gaskiyar al'amari, su fada musu gaskiyar wanda yake sakasu wadannan ayyukan da suke dan kuwa yau ranar tonon silili ce............................
Kuyi manage da wannan
_Gskia team Baby Arman kun bani mamaki πΉ, wae yama sunan novel din ne ? Kuyi tunani sannan ku bawa kanku amsa_
Fatan anyi sallah lafiya en uwa, Allah ya maemaeta mana yasa muna da rabon ganin ta badi Ameen π»π«Ά
Daga alqamin Mhiz Innocent...............βοΈ
*β‘βA ZURI'AR ARABβ‘β* An amazing and heart touching story
By Mhiz Innocent π»
πTHE TALENT TROUPE WRITER'Sπ
Page 42
Ina miqo gaesuwa a gareku INNOCENTIES ππ Mhiz Innocent luv u owl ππ»
( Baby WhatsApp group link ) ππ
https://chat.whatsapp.com/ETMx34eVVElHuSQDD3QH2e
.............Seya dauke kansa daga kan souban ya kalli en sandan yace dae_dae lokacin da souban ya qarasa shigowa cikin wajen
" Khalid ne yake sakamu wadan nan ayyukan !
" Waye kuma khalid ? Dan sandan ya fada a fusace
Black ya nuna souban yace
" Wannan yasan waye Khalid din !
Cikin rashin fahimta souban wamda fuskarsa ma seda ta nuna hakan yace
" Ni ? Waye Khalid kuma ?
Abokin aekin black din yace
" Khalid dae na gidanku "
Cikin matuqar kaduwa souban yake kallansu su duka yana mamakin wannan kalami nasu, anya kuwa gaskiya suke fada ? Ko kuwa sun fada ne kawae dansu kaare kansu ?
Seya kauda duk wasu tunane_tunane da suke zuwar masa ya kallesu rae a 6ace yace
" Kada kuyi qoqarin laqabawa wani laefin da beji ba be gani ba danku ku6utar da kanku, yin hakan sake jefa kanku kuke cikin matsala Wanda basu san da hakan ba "
Black ya gyara zama fuskarnan tasa kamar ko yaushe babu annuri yace
" Qwarae da gaske Khalid ne ke sakamu wadannan ayyukan, bama sace ka kadae da akayi ba, bayan kuma wannan accident din da arman yayi, ya ta6a sakawa mun sace ita kanta sanah din kwanakin baya "
Souban ya yamutsa kansa yana sake kallansu cikin kullewar kae couz he is damn speechless
Se Dan sandan ne yace
" Yanzu a ina zamu sameshi ?
Black yayi musu kwatancen inda yake da tabbacin za'a sami Khalid in be sameshi bama ya bashi wani address din in case .
.........Mamama ta qaraso ta zauna akan kujerar da sanah take zaune tace
" Sanah ki tashi haka mu tafi koh ? Dare yana yi "
Seta kwa6e fuska kamar me shirin sakin kuka tace
" Plss mamama ni anan zan kwana "
" A'ah ki tashi mu tafi haka nan "
Se tayi rau rau da ido tana kallan mamaman
Mamama tace
" Let's go ! Gobe da safe In Sha Allah se kizo uhmmm ?
Seta gyada kae tana miqewa suka fice .
Tunda suka koma gida ta wuce dakinta mamama ke binta da kallo, ta fahimci wani al'amari ya faru da diyarta ta wanda wannan qaddarar ta hanata samun kulawa daga Arman din dan haka bayan sallahr Isha'i mamama ta gyare diyarta ta tsaff, dukda kunya da sanah din ta nuna amma ita mamaman ta murje idanunta tayi kamar bata san me take nufi ba .
*****Tun daga ranar ya kasance kullum sanah a asibiti take wuni, dukda ba wani ganinsa take sosae ba kuma ba jin maganarsa take ba, bata gajiya da zuwan se dare kamin take dawowa .
Kamar kullum yauma da ciwon kan ta dawo, ta shige dakinta kae tsaye ta fada toilet tayi wanka da ruwa me dumi saboda zazza6in daya saba rufe ta duk dare, ta dawo kan gadon ta ja blanket ta kwanta
Kafin takae ga kwanciyar mamama tayi sallama a dakin, bata iya amsawa ba se miqewa zaune da tayi da murmushi kan fuskarta
Mamama ta qaraso ta zauna gefen gadon tace
" Sanah ina fah lura dake bakya cin abinci kwanan nan , meye hakane ?
Seta yamutsa fuska tana fadin
" A qoshe nake ne mamama "
" ban yadda ba, Dan haka ki tashi kwae ki wuce muje kici "
Seta maraeraece fuska
" Allah mamama bana son tashi zazza6i ne a jikina "
" Subhanallahi, bari na kawo miki abincin daki in yaso se kici anan "
Haka ba don tana jin yunwa ba ta amsa da " Toh "
Minti 10 baya mamama a shigo da plate din fried rice with lever ta qarasa gefen gadon ta zauna, kana ta miqa mata plate din tana fadin
" Oh yah tashi kici in gani "
Seta kar6i plate din da spoon ta dora kan qafarta sannan ta fara juya abincin
Sam Sam qamshin beyi mata ba hakan yasa ta faara kwa6e fuska kafin tayi maza ta ajjiye shi kan side drawer tana shafa wuyanta tace
" Mamama bazan iyaci ba Allah sosae zazza6in ya kamani fah "
Cike da tausaya mamama tace
" Ohk ki kwanta zuwa da safe idan zazza6in be sauka ba se muje hospital ko daddy ya dubaki "
" Tohm Mamama " ta fada tana komawa ta kwanta gami da Jan blanket din.
Washe_gari har wajen qarfe 9 sanah bata tashi ba, bayan hakan ba al'adarta bane, kuma musamman yanzu data Riga ta saba qarfe 8 ce take mata a asibiti, Dan haka mamama ta qarasa dakin, seta hangeta can tana baccinta hankalinta kwance
Mamama ta qarasa ta dafa goshinta se taji babu zafi ko kadan alamar babu zazza6in a jikinta Dan haka a hankali ta fara tashinta
A hankali tayi miqa tana hamma gami da addu'a sannan ta fara murza idanunta
Mamama tace
" Qarfe 9 fa sanah kina ta bacci "
Seta turo bakinta tace
" Allah bansan har 9 tayi ba "
" Toh ki tashi ki shirya ko yau ba zakije ba ?
Da sauri ta girgiza kae kamar qadangaruwa tana saukowa daga kan gadon, yayinda ita kuma mamama ta fita daga dakin
Sanda ta fito qarfe 10 ta kusa t.b na kunne tana aekinta dan haka ta zauna akan kujerar parlourn tana jiran fitowar mamaman
Ba tafi mintuna 10 ba taji wani irin bacci me dadi yana sakadarta, seta sulale akan carpet tayi kwanciyarta abinta, nan da nan kuwa cikin qanqanin lokaci baccin ya dauketa.
Mamama a sauko daga sama seta hangi sanah din kwance kan carpet, ta qarasa da sauri tana ta6ata, babu zazza6i a jikinta kwata kwata seta fara qoqarin tashinta tana fadin
" Sanah !
Ta tashi a hankali tana kallan mamaman
Mamama tace
" lafiya dae koh ?
" Ehh mamama kawae baccin ne be isheni ba "
" Ohk toh ko kawae kije kiyi baccin, gobe se kije "
Da Sauri ta girgiza kae tana turo baki tace
" A'ah zanje ni dae "
Murmushi mamama tayi ba tare da tace komae ba ta bita da kallo sanda take qoqarin fita daga dakin.
Yau kam tare sukaje asibitin da amrah,
Suna qoqarin shiga cikin asibitin shi kuma souban yana qoqarin fitowa daga ciki
Se sukayi kaci6us dukkansu suka tsaya
Da murmushi kan fuskarsa ya kallesu su duka kamin yace
" Barkanku da zuwa "
" Ina kwana ? Suka hada baki wajen fadar hakan
" Alhamdullillah " souban ya fada
Amrah tace
" Yah souban wae dama ka dawo ? Amma ban ganka a gida ba "
Murmushi yayi yana shafa gashin bakinsa yace
" Ehh ! Ina wani aeki ne shiyasa ban shigo gida ba, but na kusa gamawa, ina gamawa zan dawo In Sha Allah "
" Tohm Allah ya kaemu "
Ita dae sanah se tayi gaba couz she's eager taga babyn nata
Itama amrahn tana shirin wucewa souban yace
" Qanwata kodae kinyi missing dina ne ?
Se tayi farrr da ido tana dariya ba tare da tace komae ba
Shi kuma souban yace
" Ki wuce ku dubashin, bye "
" Ohk " tace sannan tayi gaba
Yanzu kam an dan faara bari ana shiga dakin da yake, amma sedae a ganshi kawae ba'a zama a dakin.
Qofar dakin a jaye take dan haka suka tura dakin suka shiga
Amrah batafi minti 5 ba ta fita daga dakin tana fadin
" Ina jiranki a waje "
" Tohm " sanah ta amsa da hakan tana qarasawa wajen gadon nasa
Kamar koda yaushe ta kae tattausan hannunta kan hannunsa ta riqesu gam kamar wadda za'a qwacewa shi, sannan takae kanta kan qirjinsa kamar kullum idan tazo
Yau kam se taji ya damqe hannun sosae sa6anin da ita kadae take riqewa babu wani reaction daga 6angarensa
Da sauri ta miqe daga kwanciyar da tayi tana kallan hannun nasu da yake a cikin na juna
Wata qwallar farinciki ta samu damar kwaranyo mata, lokaci guda wani sassanyan murmushi ya kubce mata
Seta maeda dubanta kan kan kyakykyawar fuskarsa tana kallansa sosae
Hakan na nufin idan ta fadi wani abun zeji ta ? Imma baya jinta tasan dole yasan itace a wajen tunda gashi ya riqe mata hannu shima, Dan haka seta ranqwago saetin kunnensa a hankali ta fara magana cikin sanyi
" Babyyy ! Ta fada tana jan qarshen sunan
Tana shirin dorawa daga nan seta lura da wani hawaye daga idanunsa na 6angaren da take
Seta kaasa qarasa fadar abinda tayi niyyar fada din ta tsaya kamar wata sokuwa tana kallansa
Ae yanzu kam ba qwalla ba seta fashe da kukan da taketa riqewa tun dazun
Amrah dake zaune bakin qofar dakin ta qarasa shigowa jin kamar sheshsheqar kuka
Da sauri ta qarasa shiga qirjinta na bugawa tace
" Sanah meya faru ?..
Kafin ta qarasa maganar sanah ta qaraso ta rungumeta tana sake fashewa da wani sabon kukan
Amrah ta sake rudewa tace
" Sanah don Allah ki fadamin meya faru ?
Seda tayi me isarta sannan tace
" Amrah, baby ya kusa warkewa ! Yau har riqemin hannu yayi fah "
" Awwwwn love kids " ( In muku irinta wata crazy sister of myn πΉ ) Amrah ta fada tana murmushi sannan ta dora da fadin
" Allah sanah bansan sanda zaki girma ba, memakon ki godewa Allah shine kike kuka "
Seta tashi daga kafadar amrahn tana harararta gami da murguda baki
Murmushi Amrah tayi sannan ta juya dae_dae lokacin da ita kuma Sanah ta koma wajen babyn .
***Tunda suka dawo Amrah na 6angarensu sanah a dakinta, wajen qarfe 8 sanah ta kalli Amrah tana yamutsa fuska tace
" Wlh kaena ciwo yake Amrah, ga wani irin bacci da nakeji, bans so in fadawa mamama kar hankalinta ya tashi shiyasa ban fada mata kullum da zazza6i nake kwana ba "
Amrah tace
" Subhanallahi, sanah ae gwara ki fada mata kinga ae ko asibiti se kuje koh ?
Seta sake yamutsa fuska tace
" Ni kam Allah ki qyaleni banson zuwa wani asibiti "
" Ohk bari na samo miki magani kisha " Amrah ta fada tana miqewa
Seta riqota da sauri tana fadin
" Ke ni bana so Allah kuwa "
Ba tabi ta kanta ba ta wuce part dinsu.
Mintuna wajen 3 se gata ta dawo da maganin a hannunta ta miqa mata tace
" oh yah take it "
Juya baya tayi tana qoqarin kwanciya
Amrah tace
" Wlh zanje in fadawa mamaman in yaso seku tafi asibitin may be ma allura za'ayi miki " Amrah ta fada tana juyawa kamar zata fita
Seta tashi zaune kafin ciki ciki tace
" Kawo !
Amrah ta juyo, ita kuma sanah ta jefa mata wata uwar harara kamar idonta ze tsinko
Ita dae amrah bata bi ta kanta ba ta dauko rubber water ta miqa mata da maganin, ta kar6a kafin ta fara sauke wasu ajiyar zuciya kamar me shirin daukar wasu kaya masu nauyi
Seda ta gama ajiyar zuciyar sannan ta sha maganin ta kora da ruwan, sannan taja blanket ta kwanta
Amrah tace
" seda safe, Allah ya qara lafiya "
Bata amsa mata ba ita kuma bata damu ba danta san haushinta take ji, dan haka kawae ta fice daga dakin.
Tana nan kwancen taji cikinta na wani irin murdawa dan haka da Sauri ta miqe zaune tana riqe cikin nata, ga wani tashin zuciya da take ji kamar wadda taci wani abu me qarni bayan babu abinda ke cikinta se tea, bata gama tunanin ba tayi wani yunquri a guje ta fada toilet tayi ta kwara amai kamar zata amayar da kayan cikinta, yi take tana qarawa harda qaramin kukanta, seda ta gama ta gyara jikinta sannan ta fito daga toilet din tayi sauri ta haye kan gado kafin ma mamama ta shigo ballantana ta fahimci wani abun na damunta .
********A daya 6angaren kuwa tun ranar dasu black suka bada address din inda za'a sami Khalid en sanda suka fara bincikensa, address na farko basu sameshi a can ba saboda haka suka yi fakonsa a dayan address din Wanda suke da tabbacin zasu sameshi acan din.
Wani gida ne wanda yake a wata sabuwar unguwa wadda babu mutane sosae a cikinta, sanda sukaje qofar gidan babu mukulli a jikinta hakan ya alamta musu cewa akwae mutum kenan a cikin gidan, dan haka wasu suka tsaya a waje, wasu kuma suka shiga cikin gidan saboda babu mae gadi a gidan.
Dae_dae qofar parlourn suka tsaya wadda take a kulle, daya daga cikinsu yae knocking din qofar yana komawa da baya hannunsa riqe da bindiga....................
Mhiz Innocent ce.............βοΈ
*β‘βA ZURI'AR ARABβ‘β* An amazing and heart touching story
By Mhiz Innocent π»
πTHE TALENT TROUPE WRITER'Sπ
Page 43
Ina miqo gaesuwa a gareku INNOCENTIES ππ Mhiz Innocent luv u owl ππ»
( Baby WhatsApp group link ) ππ
https://chat.whatsapp.com/ETMx34eVVElHuSQDD3QH2e
.........Daga cikin dakin Khalid yaji knocking din wani banbarakwae, saboda yasan ba wanda yake shigo masa ballantana yace ko maqota ne, sannan a cikinsu black ba wanda ze tsaya knocking din nan sedae kawae su kirashi a waya, dan haka seya fara tunanin ko waye ?
A hankali ya taka zuwa bakin qofar sannan fuska a hade yace
" Waye ?
1 daga cikin en sandan yace yana gyara tsaewarsa
" saqo aka bamu mu kawo maka "
Seya sake 6ata fuska yace
" Inji wa ?
Dan sandan shima a fusace yace
" Black "
Jin ya ambaci sunan black yasa beyi wani tunani ba kae tsaye ya bude qofar, sedae kafin ya qarasa budewa har sun shigo cikin dakin
Wani ya riqeshi, wani kuma ya saetashi da bindiga yana fadin
" U'RE UNDER ARREST "
" Arrest ? Ya fada cikin mamaki yana kallan en sandan hannyensa a sama
" YES U'RE FIRED "
Daga haka suka tasa qeyarsa gaba se police station.
______A hankali ta ajjiye al'qur'anin dake hannunta, tayi addu'a sannan ta miqe, wayarta ta da tayi qara ta nufa ta dauka, tana mamakin ganin kiran daddyn a wannan tsohon daren saboda baya gida a asibiti ze kwana
Seta kawar da tunanin ta daga wayar tana karawa a kunnenta
" Hello ranka ya dade "
" Na tasheki a bacci koh ?
Se tayi murmushi me sauti ba tare da tace komae ba, yayinda daddy ya dora da fadin
" Wani babban albishir zan fada miki rahama "
Seta qarasa tashi gaba 1 kamin tace
" Ina jinka daddyn Arman, wane abin farin ciki ne ya samemu ?
" Arman ya farka !! Ya fada da farin ciki wanda muryarsa ma seda ta nuna hakan
Cikin tsananin farin ciki, wasu qwalla suka kwaranyo a fuskar mamaman, se kuma lokaci guda ta koma hamdala ga Allah buwaya gagara misali wanda shike yadda yaso a lokacin daya ga dama
Daddy yace
" Ni fah ba cewa nayi kimin kuka ba ranki uhmm "
Seta fara qoqarin hadiye kukan dan karya fito tace
" Yalla6ae bansan sanda hawayen suka fito bane, Allah mun gode maka, zamu samu ganinsa yanzu ?
Daddy yayi dariya
" Hala kin manta qarfe nawa ranki ya dade ?
Itama dariyar tayi sannan tace
" Allah ya kaemu gobe da safe "
" Ameen " ya fada yana kashe wayar.
_____Washe gari qarfe 7:30 mamama ta gama shiryawa kaana kae tsaye ta wuce dakin sanah
A zaune ta sameta kan stool din gaban mirror, kamar meyin kwalliya sedae ba abinda take, mamama ta qarasa tana kallanta sannan ta juyo suka hada ido, se take ganin kamar an chanja mata diyarta ta, se yanzu ta lura da wasu sauye_sauye dake tattare da ita misali ta sake wani fari sosae, ga kumatunta sundan taasa
" Lallae zaman gida ya kar6e ki sanah, Dan bata tunanin tunda suka tafi hutun strike bayan zuwansu los Angeles babu inda ta sake zuwa " mamama ta fada tana ajjiye abincin data shigo dashi a hannunta
" Ina kwana mamama ?
" Alhamdulillah, Yi maza kici abinci akwae wani albishir dazan miki "
Seta kalli abincin kawae tana yamutsa fuska tace
" Nikam mamama tea kawae zan sha "
Mamama ta 6ata rae
" Ayi mutum kullum sedae yasha tea babu wani abu daze riqe