Header Ads
Showing 27001 words to 30000 words out of 46028 words

Chapter 10 - YAR KWALLIYA COMPLETED Book by Husba'ahfama.txt

Ads the beginning of article before Image

Unknown   

03 Jul 2024

435

Ads at the middle of Article

👝👝👝
👠👠
👝


💄💅 *'YAR KWALLIYA* 💅💄


👝
👠👠
👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠




Written by *husba'ahfama*




35-36




Abinyi shine muwanke kamar yanda suka ce amma karya fita


Ko to shikenan mu tafi


Suka tafi suna Jan kayan a kasa har suka karasa dakin su ban daki suka wuce suka zube kayan a kasa


Abu tace Nifa banga sabulun wankiba gadai bokiti Anan


Binta ta yamitse fuska tace Nifa dadina dake qauyan ci su basa amfani da sabulu ga abinda suke wanki dashi ta nuna hypo da bula


Haba tab sufa yan gidan nan badai karyaba yanzu meye aibin sabulu da basa amfani dashi


Binta tace waya sani kila suna son su bambanta kansu da mu yan qauye miko bokitin


Abu ta miko suka Sa kayan a ciki Binta ta dau hypo Abu ta dau bula Binta gaba1robar hypo ta juye a kayan Abu ma kwalin gaba1 ta juye na bula a kayan gashi kayan Ja ne


Abu tace ni abin wankin nasu Amai yake niyar sani


Nikuma bacci nake ji


Zomuje muyi bacci indan muntashi sai muyi KWALLIYA


To muje su Abu suka kwanta bacci Kaya kuma na jike harsu Aqeel suka dawo suna bacci koda suka tashi kayan


KWALLIYA Abu ta dauko musu sukayi Wannan karan KWALLIYAR tafi muni dan a fukar nan babu inda suka bari ko


ina sunsa Jan baki da kwalli da Eye shadow saida suka gama sannan Suka je gurin kayan da suka bari a cikin ruwa


Abu ta shiga mamakin ganin ruwan ya canza kala daga Fari ya koma Blue tasa hannu ta dauko rigar


Tace hege iro lokacin da nakai mihi kayana ya Rina min yace hibaze rinaba saina bahi kudi waya mutu waya tahi yanzu Gahi munkoyi rini cikin sauki jan kaya ya koma haka shagali


Binta tace kece kika wani damu da wani iro bantaba kaimai riniba yanzudai mu matse kayan


Abu tace to suka matse kayan binta ta Bude rigar taga tana kallon Abu ta cikin rigar Abu na kallon ta


Kayan ya huhuje ya canja kala


I hu Binta tasa ta saki rigar a kasa sosai ta gigice ganin yanda rigar ta koma ita kanta bata san dalilin rude warta ba


Abu tarike ta tace Binta ki dawo cikin hanka linki mana meye abin damuwa Anan sukai aimusu faci sukansu zasu so kayan


Allah Abu ni harna shiga damuwa bawani Abu nake tsoroba illa nunar rana tinda muka zo gidan nan yake jin haushin mu


Rabu dahi Wannan na mihi uziri kanshi baya aiki zo muje gasu can suna hira Abu ta rike hannun Binta da bokitin da kyan a ciki suka wuce falo


Suna shiga Abu tayi ido4 da Aqeel ta fashe da kuka Binta na ganin haka itama tasa kuka


Hajiya tace lpy kuke kuka wannan bokitin na meye


Amal tace tinda kika ga suna kuka wata tsiyar suka shuka Nina sani


Nidai nace bada yawuna ba amma ka dauka ka basu duk abinda yasamu Kaya na bazan hakura ba wlh zaku gane kuran Ku


Abu da Binta najin haka suka kara sautin kukan da suke yi


Aqeel ya daka musu tsawa yace kuyi wa mutane shiru me kuka yiwa kayan


Suka kara fashewa da kuka


Hajiya tace Aqeel ka musu a hankali Abu meya faru Ku saki jiki kuyi magana ina nan ba abinda ze faru duk kun daga min hankali


Abu tace hakane kuma mune dai aka bamu wanki muka yi kuma ta fashe da kuka


Binta tace yi shiru Abu abin hine masu rini a za ma ninnan sunyi karanci mu samman a birni mun yi muku wanki kamar yanda kuka ce harda rini muka muku


Aqeel cikin kaguwa Yaji abinda ya samu kayan yace Ke Me KWALLIYAR Aljanu kifada mana abinda kuka yiwa kayan mana idan kuka bari na sake magana hmm kunsan sauran


Abu da Binta suka goge hawa yan fuskar su suka sunkuya kowa ya dauko riga1 Abu ta saita Aqeel ta Bude rigar tana kallon Aqeel yana kallon ta tawani wawa keken yaga ta tsakiyar rigar

Binta ma Arif ta saita da rigar yana kallon ta tana kallon shi


Aqeel a zuciye ya mike ya nufu Binta da gudu ta koma bayan Amal


Hajiya tace Aqeel zoka zauna barni dasu tukun na Abu garin ya haka ya faru


Binta tace in banda nunar rana da abinhi meye a ciki dan kayan ya yage Gashi kamar an kwato daga bakin kura nidai
bana cin Kaya balle ace nice ni


da naga rigar nan harya tunomin da wani ma haukaci a *DARAUDAU* hima haka kayansa suke muyi ta tsokanar hi


Abu tace Allah sarki koyayi aure ma ban saniba kaga yanzu kudauki kayan kukai a muku faci idan akayi muku faci hmm ba a cewa komai dan kyanda


kayan nan zasuyi sai yan garin nan sun koka da kayan kuma zaku biya kudin rini dan ba a banza muka Rina ba Ehhhe


Hajiya tace Abu kayan za a kai faci kuma ASA a jiki dan hauka


Arif yace ina Wannan mahau kacin da kuke fada shiya dace daku beyi aureba kuyake jira dankuma bakuda hankali kamar ku kila maya fiku hankali


Amal tace me kuka yi amfa nida shi wajan wanke kayan


Binta tace jita dan Allah da wata ma gana sai kace Baku kuka ajiye dan wanki ba na roba munjuye hi gaba1 na kwalima haka


Gaba dayansu salati kawai sukeyi


Hajiya tace Dole Kayan ya yage ya canza kala kuma dai bakwa son kayan shiyasa kuka basu su wanke muku se kuyi hakuri Ku anshi kayan a haka kukai faci ta bakin nasu


Abu tace hine magana hajiya hiyasa nake sanki yasin kina saurin gane wa banda su nunar rana


Aqeel yace a haka baze yiyuba mommy ya mike yazo kusa da Amal yadaga hannun ya kaiwa Abu duka


Hajiya kina ganin nunar rana ko


duka yakumakai mata a baki


Yace daga yau nadena raga miki duk sanda kika ce nunar rana saina cire miki hakori kucaca kawai


Hajiya tace banga amfanin fadan da kuke musuba alhalin kune da laifi idan Baku basu kayan ba haka ze faru Arif ya kayi shiru


Mommy mezan ce tsautsayine ko


Abu da binta sukace Eh


Arif yayi dariyar mugun ta


Karar shigowar mota sukaji kafin motar ta tsaya suka sauko


Da gudu suka shigo falon


Abu da Binta na ganin su jiki ya fara rawa idoya ciko da hawaye


Sojojine sukazo gidan Abokan su Arif ne Arif yasan da zuwan su


Agaban hajiya suka tsaya suna gaidata1bayan1 hajiya na Amsawa


Abu da Binta ba bakin magana kiris kwai suke jira su fashe da kuka


Amal ta gaida su jin Abu da Binta sunyi shiru Arif yace Ku gaida su abo kan mune


Aqeel yace Ahmad dama ana ganin Ku


Ahmad yace Eh wlh yanzuma wucewa muka zoyi ta unguwar ku Aisha tace min kundawo saidai kun kusa komawa shine nace bari nazo mu gaisa


Arif yace tin dazu ya sanar dani cewa yayi nayi shiru yanaso ya baku mamaki ne


Ahmad yace wayan nan fa kai kalli wani KWALLIYA kamar an hako su daga rami nibadan da mutane a nanba sai nace gamo nayi kalli yanda ta kafeni da idanu


Harlokacin Abu da binta basu dena kallon suba


Ahman yace Ke lpy kodai wani laifin kukayi


Allah ya baku hakuri karku tafi damu bazamu sake ba tam bayi hajiya ita kanta tasan bama laifi tinda mukazo bamu taba laifin ba


Aqeel yace karya sukeyi Ahmad tinda sukazo suke samu suru to kalli yanda sukayi da kayan nan daga basu su wanke idan barrack zaku kutafi dasu Ku kaisu kudakesu karkuma kudawo dasu munbaku


A'a hajiya kisa baki kinga suna kyauta damu waiyoo inna yaya Nura gasoja ze kasheni waiyoo inna nadena


Arif yace karya ta keyi karku yarda bazasu dena halin suba kutafi dasu kawai


Binta tasa iho tana kiran umma kite makeni zasu kashe mu


Cika gidan da suka yi dakuka yasa 1 daga cikin sojojin ya daka musu tsawa


Abu da Binta suka rude saiga fitsari na zubowa kamar yara kafana rawa


Amal dariya kawai takeyi ta kasa cewa komai Aqeel da Arif suka hade rai


David yace daku zamu tafi Ku wuce mu tafi


Koda Abu da Binta suka ga bindigar hannun shi suka kara gigi cewa


Hajiya tace sun dena Ahmad kar a tafi dasu


David yace maman mu yan2 sun gama magana mu zamu tafi dasu kuyi magana da ita


Abu da Binta suka kafe hajiya da jajayan ida nunsu suka ce hajiya mundena baza musake ba idan kika bari suka tafi damu ta matsa kusa da hajiya tace me Jan idoncan da bindiga a hannu kashe mu zeyi


Hajiya ta kalli Arif


Ahmad ya hade rai yace mekika ce mata koma dai me kikace be da meniba Ku wuce mu tafi


Abu ta rude tace hajiya kiyafemin idan kinga inna kice taya femin Allah yayi nizan rigata mutuwa lokacina yayi


kicewa yaya Nura ina qaunar shi kuma nayi kewar shi kinga Wannan mezibin mugayan tinda yasa baki nasan komai ya baci














































New writer's


Hakan Take *husba'ahfama* 🌹🌹💋




👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝
👠👠
👝


💄💅 *'YAR KWALLIYA* 💅💄

👝
👠👠
👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠




Written by *husba'ahfama*




37-38




Ahmad ya daka mata tsawa yace nine me zibin mugaye naji na yarda David kutafi dasu


Binta da Abu ciki ya murda suka fara tsalle suna ihu harda kuka


Aqeel yace meye haka kuma Ahmad kana gani ko kokun tafi dasu kumusu dukan tsiya Ku karya kafa finsu da hannaye


Abu tace hajiya kina jiko karya mu zasuyi kiba su haku waiyoo Allah na


Hajiya tace ba inda zaku Ahmad kuyi hakuri indan sun sake nida kaina zan kira Ku


Arif yace to mommy saidai ki bari David ya dakesu tukun na jikin su ya gaya musu


Aqeel yace kayi musu dukan kawo wuka nikuma zan kira motar Asibiti


Abu da Binta Suka zube kasa suna kuka suna cewa ba inda zasu David yace su tashi Abu da Binta Suka ki tashi Ahmad


na daka musu tsawa Suka tashi suna tashi David ya daukesu da mari saida suka ga taurari


Ahmad yace mu zamu tafi kukuma mu tafi Abu da binta ido yayi Ja sai kallon hajiya sukeyi Aqeel da Arif namusu dariya ganin yanda Abu da Binta Suka rude


Hajiya tace Ku tsaya kusha koda lemone mana mun Tsaya muna magana ba a kawo muku komai ba Amal dauko musu lemo


Hajiya ki barshi akan hanya muke zamu ware rana muzo mu yinar muku


Tab Saikun sha lemo zaku tafi inbaku shaba Ku tafi dashi ze muku amfani tinda akan hanya kuke
Taje ta dauko ta kawo musu


Suka musu rakiya zuwa waje Abu da Binta na ganin su a jikin mota sojoji suka fara kyarma jikinsu yai zafi


Amal tace Abu Binta lpy
Abu da binta sukayi shiru


Amal ta tabasu zafi taji da sauri da dauke hannun ta a jikin su


Mommy jikinsu zafi basuda lpy


Aqeel yace Ahmad karya ne basa so Ku tafi dasu ne kawai


Hajiya bata ce komai ba ta kama Hannun su zasu shiga gida


Ahmad yace mommy zaki tafi dasu basu yi Alkawarin dena abinda sukeyiba


Abu da Binta sukayi caraf sukace mundena bazamu karaba


Ahmad yace kuma kara kira kawai yan2 zasu mana muzo mu tafi daku shi kenan kuma baza a kara jin labarin kuba


Hajiya tai musu sallama ta shiga ciki dasu Abu da Amal


Arif dariya kawai yakeyi Ahmad ma haka


Ahmad yace yan2 ba wasaba dana gansu na dauka matan kune dan nasan Wannan dogon burin naku dawuya ya ciki dan Kun Ja dayawa


Haba dai Allah ya kiyaye ba dai muba kaga idan kana ciki sai kayi magana tin kafin mu bada su cewar Aqeel


Ahmad yace yaran abin dariyar su yayi yawa irin Wannan tsoran haka


Arif yace shir mensu kuma saiya kusa saka kuka kaga dai yanda suka yiwa kayan mu Kaya na2 kenan


Ahmad yace kace yabi jiki to gaskiya zan gaya muku wayan nan bazasu nutsuba saidai su rage wani Abin koda sun waye


Aqeel yace Allah Ahmad


Da gaske nake fada maka yana yinsu zaka gani bana Tina nin Wannan abin zesa su nutsu mu zamu tafi


Kace da sauran aiki


Ahmad yayi dariya


Suka shiga mota suka tafi


Abu da binta naciki jiki zafi yaki sauki in banda karuwa ba abinda yakeyi


Suna dakinsu a kwance sai rawar sanyi sukeyi
Arif da Aqeel dakin suka je


Aqeel ya daka musu tsawa yace Waze muku aikin fitsa rinku da kukazo kuka kwanta


Zazzabine a jikinmu shiyasa muka kasa gyarawa


Ko to Ku tashi Ku wuce manya da kudai Asibi da kande baza su muku aikin fitsari ba

To gamu nan zuwa


Da dai yafi kutashi yanzu da rashin jine dakunyi kun gama dake yanzu fitsarin kune shine zakuce bakuda lpy ko cewar Arif


Aqeel yace yaran unguwa zan fita na tara muku su muku wakar fitsari


Abu tace Kut Allah ya basu sa'a naji wani yace fitsari hmm Yasin bakin shi zanfasa na zubar da hakorin bakin kirasu kaga


Aqeel yace Wani kinga Nifa nariga na baro jirgin ki Abu kanki baya aiki kinfi gane fasawa da duka da danbe inajiye miki randa zaki samu dai dai ke


Arif ya kalli Binta da tayi shiru tana jinsu yace ke lpy


Tace jinake kamar jikina ba ya tare dani ga kaina namin ciwo ga soja ya mareni ga saitin gurin ciwo kawai yakeyi


Arif yace kefa dama kin iya kan kara Naganoki da cin abincine baza Kiyi Lissa fin nanba kuje Ku gyara fitsarin na kaiku Asibiti


To suka ce suka fita gurin me gadi Suka je sukasa ya Bude musu kofa


Megadi yace gaskiya bazan bude ba bakusan matsalar da kuka sani ciki bane


Abu tace Kaga nan wajene ba inda zamu kasa zamu Ehbo


Megadi yace yanzu naji magana kuje ina kallon Ku


Suka fita Abu ta baza maya fin jikinta Binta ta zuba mata kasa da kyar suka samu suka kulle mayafin sukayi kama kama


suka dawo cikin gida inda sukai fitsarin sukaje suka ajiye kullin kasa Arif da Aqeel na zaune suna kallo A tashar


AREWA24 suna kallon mai mai cin gari ya waye Abu ta kwance kullin suka juye kasar a gurin da sukayi fitsari Binta ta baza


kasar Aqeel da Arif tashin kasa kawai suka ji suna juyowa suka ga inda kasar yake Abu ta bige maya finta ta maida gwullin da tayi dashi a kugunta


Arif yace ma su KWALLIYAR Aljanu anya kanku 1 kuwa meye na zuba kasa Anan kuduba fadin falon nan a ina kuka ga kasa da zaku zo kuzuba


Binta tace kaga nunar rana karkusake kuce bamuyi dai_dai ba danku kun iya ciki baki mu a *DARAUDAU* da kasa muke rufe fitsari tam bayi abu


Abu tace ina nan bame karyataki ko dandali indan munje fitsari ya kama mu saimu samu guri muyi mu rufe da kasa ta fada tana dariya


Aqeel tsabar haushi ya kasa cewa komai komawa yayi ya zauna bazaku hauka taniba wlh nagode Allah hutum mu yakusa karewa dabansan yanda zan yiba Wannan ai rashin hankaline


Abu tace Banga abin rashin hankali a nan ba mun gama kuzo ku kaimu inda kukace zaku kaimu Yasin muna jin jiki


Aqeel a kufula yace Ku mutu Yasin yaran nan kozasu waye sai anshawuya Yasin Kunji ko kunfara samin qauyan cinku a baki


Haya niyarsu hajiya da Amal suka jiyo suka fito


Amal baki ta saki tana kallon kasar cikin mamaki ta tambaya tace waye da Wannan aiki ko ince tinanin waye a cikin Ku


Binta tace namune nan da magana ne ke nafa Riga na gane take taken ki abamu fili yau mu kece raini tsaka ninmu ki gani inbam miki dukan tsayaba


Abu tace nakine ya fito fili nima inada cikinta kiris nake jira jikin wata ze gaya mata


Bayan Hajiya Amal takoma tace wato kun shirya yanda zaku zaneni tsabar mukunta ko to shi kenan yaya Ahmad beyi nisaba sena Kirashi yadawo


Binta tace Mudai hajiya bamuda lpy kice sukaimu gurin magani ko sassakene a bamu musha


Arif Ku kaisu Asibiti karku damu da nan zansa kande ta share Abu binta Allah ya kara sauki


Aqeel yace mommy kice musu

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads