Header Ads
Showing 21001 words to 24000 words out of 46028 words

Chapter 8 - YAR KWALLIYA COMPLETED Book by Husba'ahfama.txt

Ads the beginning of article before Image

Unknown   

03 Jul 2024

433

Ads at the middle of Article

bace nunar rana tukun na ma Abu ta fada a cikin zuciyar ta


Amal tace yaya ya za ayi yanzu


Aqeel ya kasa cewa komai sai huci yake


Abu tace susha ruwa su tafi tinda abincin ba dole bane dama duk Wannan aboki akayi wa girkegirke haka Nina dauka sarkine ze kawo muku ziyara ruwanma karku baso tinda gidan bana gyatimi bane


A fusace Aqeel ya juyo yana huci shi tinda yazo gun bekula da itaba se yanzu mur yarta Yaji sai lokacin yasan tana gurin ya zari shar bebiyar wuka tana kyalli yabi Abu dashi


Dagudu suka wuce su Usman Amal na binsu a baya sukayi dakin hajiya


Gudun da taji yasata saurin mikewa tace lpy Aqeel mezan gani haka


Yace hajiya matsa ki bani ita ina abincin da aka dafawa su Usman babu shi ita kadai tasan inda ta kai shi


Abu tace hajiya karki yarda da abinda zece wana tabbaci yake dashi na cewa nina boye abinci


Inni naboye abincin ina nakaihi


Yace mommy ita kadai ce zata aikata haka Nina sani


Abu ta fito daga bayan hajiya tana murguda baki zatayi magana Aqeel ya dauketa da mari


Abu ta gigice takurma ihu ta zube kasa tana birgima


Yaya meyasa meyasa ka mareta kome ta maka ka dinga hakuri mana cewar Amal


Yimin shiru yadaka wa amal tsawa kema yanzu nahada dake nakula tinda sukazo kike goyan bayansu bakyaso aimusu fada kuma kina ganin irin abin da sukeyi bedaceba


Hajiya tace Aqeel karka sake dukanta kome ta maka ka sanar dani ni nasan mezan mata


Amma mommy


Tadaga mishi hannu tace ya isa bana son jinkomai
kanta karasa maganar ta tuno maganar da Abu tace mata Binta kurace taci ta koshi


Waiyoo Aqeel temako zoka temaka ka dauko Binta mukaita asibiti Abu karkicemin duk yawan abincin nan ita ta cinye


Hajiya Nifa ba tsoran nunar rana na keyiba maganar gaskiya hine Binta taci iya cinta sauran kuma na rabawa mabu kata


Mommy kina jiko kinajin abinda take cewa
Wlh zan karkarya yarinyarnan


Nidai Aqeel yar mutane katemaka mu kaita asibiti


To naso ace ke kikaci ba ita ba saidai dani kike magana
Yafita daga dakin rai abace


Arif ya shigo hannun shi dauke da leda guda2


Aqeel dasauri ya karasa gurin shi yasanar dashi abinda Abu tayi seyai murmushi yace


Nasan wani Abu me kamar haka ze faro tinda na gane cewa indai ta fadi Abu saitayi yasa na ke fadada tina Nina karka damu ga Wannan nabi ya na siyo abincine masu dadin gaske


Kai naji dadi Amma hakan baya nufin na hakura dan yau raina ya baci sosai


Yace karka damu muma zamu hukunta su


Su kayi dariyar mugunta


Arif yaje suka gaisa da Usman
Aqeel ya jera abincin da Arif ya siyo Aqeel ya fita kunyar Abokin shi dan Abincinda Arif ya siyo kamar a gidansu akayi


Saida yamma Usman da kannan Sa suka tafi


Lokacin ne Aqeel ya maida hankalin Sa ga Abu hukuncin da ze mata kawai yake Tina ni


Aqeel Tina ninme kakeyi haka


Kabari kawai Arif zo muje


Arif yabi bayan shi suka tafi kitchen sukaje


Arif yace me za muyi Anan


Zuba ido ka gani


Aqeel ya Dora ruwa yana ta fasa yasa taliya yana laushi kadan ya sauke ya kwashe yasa miya


Aqeel yace nagama mu tafi


To amma ka hada mata da giyarta ta dazu


Haka ne jeka dauko ka sameni a kofar dakin su


Arif yace to yaje ya nauko lema yanufi dakinsu Binta
Atsaye a kofar dakin yaga Aqeel
Aqeel na ganin Arif yazo yabude dakin ya shiga bacci kawai Abu da Binta sukeyi han kali kwance
Arif da Aqeel sukayi dariyar mugunta


Arif ya tsaya a bangaren da binta take
Aqeel ya Tsaya a bangaren Abu


Atare suka daga hannu suka Kai musu duka me shiga jiki a gigice suka mike suna ihu


Aqeel ya daka musu tsawa
Suka yi shiru suna kallon su Arif


Arif yace kun kyauta a binta kukayi kunbirgeni sosai Ku zonan


Binta tace nan ina muyi me kuma banda Wannan cin zalin da kuka mana


Aqeel rai ahade yace cinzali ko to bari namuku dukan kawo wuka muga abin da zaku kira Wannan kuma


Abu tace nuna karmuyi haka mana bari muzo
Agabanshi so ka Tsaya


Aqeel yace ku zauna a gaban kwanan dana kawo


To sukace sukayi kamar yanda yace


Arif yace Ku Bude kuci


Binta tace dandai ci gidan kazo ta Bude kwanon tana ganin abinda ke ciki tasa kara


Aqeel ya zaro wuka yace kokiyi shiru kona caka miki ba ina nufin hakan zan farayiba saina fara gunduwa gunduwa daku tukun na


Binta ta rufe baki


Abu tace nunar rana bama cin sutsa fa kukawo mana wani abin banda Wannan yai dariyar mugunta


Arif yace Ko lokacin da kuka rabar da abincin kunyi shawara dani


Abu ta girgiza kai alamar a'a


Aqeel yace Yauwa dan haka Ku cinye sutsar nan gaba1 banaso naga komai a cikin kwanan nan


Baza mu iyaba harni har kwada yina ban taba cin sutsa ba yasin cewar Binta


Balle ni Abu bazan iyaba dan Allah kuyi hakuri


Aqeel yace Hakuri Sam bazamu hakuraba har sai kun cinye sutsar nan gaba1 ya daga wukarshi yana sha fawa


To za muci Abu ta juya kai tasa hannu ta debo taliya jitayi yana mata motsi a hannu ta zubar dashi


Aqeel ya hade rai yace 'YAR KWALLIYA kinjawa kanki bayan kuncinye taliya ga lemo kushanye shi tas shima


Giya dan Allah kayi hakuri malam Rabi'u yace ba kyau shan giya fa


Tinda kika kirashi giya kekadai zaki shanye cewar Arif


Lokacinku ya fara daga yanzu inba Ku cinyeba ga Aqeel a kusa dani
Aqeel ya daga wuka ya nuna musu


To shi kenan zamuci haka Abu da Binta suka rufe ido suna cin sutsa ta bakin nasu




Suna hawaye serige ciki suke kamar zasuyi amai




























New writer's


Hakan Take *husba'ahfama* 🌹🌹💋




👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝
👠👠
👝


💄💅 *'YAR KWALLIYA* 💅💄

👝
👠👠
👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠




Written by *husba'ahfama*




29-30


Harsuka cinye Abu da Binta sai rike wuya sukeyi


Arif yace kun gama da Wannan saura lemo


Gaskiya Ku barmu haka


Aqeel ya wasa wuka


Binta tace Abu yi shiru bamu


Arif ya zuba ya basu

Suka ansa suna sha


Binta Kura kyaci da Gashi tana sha taji dadi ta kafa kai ta shanye ta mika mishi Kofi


Arif yace Me zanyi dashi


Tace Wani zaka zuba min


Arif ya zuba mata takuma shanyewa ta miko mishi Kofi shikuma yabata gaba daya ta ansa tashanye


Binta tace bawani Ku karo min Yasin giyar badai dadi ba wai kaf qauyen mu idan za a zagaye bana tinanin za a samu ya Wannan


Arif da Aqeel suka kalli juna


Aqeel yace ke harkin shanye


Abu tace Eh na gama tafada tana hawaye


Aqeel yace Yauwa ita dai waccan wani hanyar zamu sake dan na kula Wannan kura ce yanuna Binta


Kiran salla sukaji suka mike zasu tafi masallaci


Aqeel yaga su Abu ba a daniyar tashi kwanciya ma suke shirin yi a gurin ya daka musu tsawa yace meye haka bakuji kiran sallabane kuke shirin kwanciya


Abu tace munyi tin a *DARAUDAU* ba a binmu bahin salla


zaro ido sukayi atare suka hada baki sukace mekukace sukace mun shiga UKU Akwai bamban aiki


Arif cikin mamaki ya dawo ya zauna yana fukan tarta yace ban ganeba


Binta tace sallar sati1 muke hadawa muyi a rana1 kaga sauran ranakun mun huta Ku kuna salla mukuma muna hutu ta fada tana dariya


Aqeel yace hauka zalla bana tinanin kan yaran nan a kwai kwakwalwa wlh kai kaji wani Abu ko yaro bazeyi shir mannan ba


Arif yace kuna zuwa islamiya a qauye


Abu tace muna zuwa malam rabi'un ne dan rainin han Kali Abu kadan duka hine muka dena zuwa ban fada makaba


har bokoko a wuta munyi sau1 mukaje shima ya raina mana hankali muka hukuntashi bamu sake komawaba sai gamu a barni tafada tana dariya harda tafawa


Aqeel kaji magana gangariya nakula jahilcine kawai yake dawai niya dasu amma komai yazo karshe


Aqeel yace shi malam rabi'un ne ya ce Ku dinga hada sallah


A'a mune mukaga hakan yafi dacewa saboda bamuda lokaci zama muyi akan lokaci saboda dasafe mu debo ruwa darana naraka Binta tallar gurjiya da yamma muje dandali tafada tana rawa


Aqeel ya kalli Arif yace a kwai matsala ke dena mana rawa ko kinji kidane nibana tinanin kawunan yaran nan zasu dau karatu


Arif yace koma meye sunan Ku ban damu na saniba kutashi kuyi Alwala kuyi sallah yanzu sannan Ku sani ba a hada sallah kowacce ana yinta akan lokacinta kunaji


Allahu'akubar kaji malamai munji kuma mun gane zamu gyara wai bazaku kaimu dandali bane natara rawa masu yawa Ku kaini na juye yanbirni su gani su sani mu yan qauye hmm tatashi tana rawa


Aqeel yace yarin yarnan a bace take bata gane komai zomuje masallaci kaga har an tada sallah


Suka tafi sukabar Abu na rawa binta na zaune tana shafa ciki


Binta tace Abu zoki rakani gona nayi kahi sunan basuda shadda Gashi a matse nake waiyoo


Abu ta dena rawar da take cikin mamaki tace binta kefa ki kace yan birni basa kahi ya haka kuma keza kice na rakaki gona


Kinga su wayanda aka Haifa a birni nake nufi banda mu kinga aimu zuwa mukayi ko


eh hakane kinga yanzu yamma tayi kihiga inda aka yi mana wanka ina randar nan ta ruwa Wannan farin


Binta tace Eh na ganeta


Kije Kiyi a ciki


Abu ba komai


bakomai jeki na Tsaya miki


Binta ta shiga tayi ta fito tana rike ciki tana yamitse fuska


Abu hanci a toshe tace Binta duk warin kahin kine haka kamar mushe


Bana son wula kanci lafiyace da bani dashi bazan yiba


Amal ta Bude ta shugo tana shigowa warin ya daki hancin ta tace meye haka warin meye Wannan


Binta tace ji wani Abu da takeyi kamar bata taba yin kashi ba wayasanima ko naki yafi nawa wari


Amal tace a ina kikeyi


Binta tace shiga nan ta nuna ban daki zakiga randar ruwan nan a ciki nayi karki damu sanda na Debi ruwan tsarki a randar tukunna nayi


Randa Amal ta mai maita cikin ban dakin tashi ga tasamu binta batayi shirmeba korawane kawai bata yiba ta kirata ta nuna mata yanda akeyi


Abu tace Tab saura kiris mu fita waje Neman Gona da zatayi a can Ashe Gwanda da bamu fitaba da munsha wa halar
Banza


Shiyasa nace kome kuke so Ku tam bayeni


To ai mun gane yanzu kuma


Bari naje gurin mommy ina zuwa


Tabude ta fita su Aqeel ta samu a dakin


Aqeel yace mommy gaskiya a nemawa yaran nan malamin da ze dinga koya musu karatu a gida idan suka fara hankali a kai su makaranta


Arif yace mommy yaran nan naki da girman su hada sallah sukeyi


Hajiya tace Eh hada sallah bangane ba


Aqeel yace hmm dazu suka fada mana waisu sallar sati1 sukeyi a tare rana kunda zezo kuma sun huta


Hajiya tace tab Allah ya rufa asiri yakamata musamo musu malami yanzudai malamin da ze dinga koya musu Qur'ani da sauran littattafai na addini shine malam kabiru dama shiya ke koyawa Amal


Arif yace hakan ma yayi idan suka ga amal kila su zauna mommy boko fa


Eh to Wannan dinma kabiru ze iya koya musu tinda tsohun malin makaranta ne


Arif yace to mommy zan Kirashi na sanar dashi daga gobe zasu fara inba hakaba abin nasu lalacewa ze karayi


Hajiya tace yauwa Aqeel idan malamin yazo kuja musu kunne karsu yiwa malamin halin nan nasu dan naga suna


tsoron ku sosai Niko yakayi da Usman duk kunya ta hanani fitowa koda muke Salama Akunyace nake wlh


Aqeel yayi dariya yace mommy Arif ya findake kunya shiya siyo abinci ya kawo bazama kice a waje aka yiba kannen Usman sunce suna godiya da yautar da kika musu


Alhamdulillah amma naji dadi Allah ya muku Albarka


Ameen mommy tafiyar mu zuwa America na kara matsowa fa


Hakane fa harna fara kewar Ku


Mommy karki damu ga *'YAR KWALLIYA* da *KURA* za su debe miki kewa suka fada suna dariya


Hajiya tace yaran nawane kuraye lallai inajiye muku wlh ranar jinkunya musammanma Aqeel kafi kushe su


Tab indai wayan nan ne ranar bazata zoba nida zan dauko miki sirika a America me zanyi da wata yar qauye


Allah yaya to shi kenan zamu gani cewar Amal


Mommy saida safe mu zamu tafi


Allah yatashe mu lpy


Washe gari da safe Abu ko karyawa basu yiba suka fice daga gidan


Abu na tafiya tana mita


Kai dan Allah ki Tsaya Abu mitar me kikeyi


Binta tinda mukazo basu kaimu sun nuna mana gariba sun barmu a guri1 sannan gasu nunar rana gidan ma ba dadi ko dandali basu kai muba


Binta tace shine abin damuwa to ba Gashi mun fitoba muga gari iya san ranmu daga nan muje muga dan dali


Hakane kuma saida sukayi tafiya me tsawo sukayi nisa da gidan sosai

Duk wanda ya gansu mamaki yakeyi ganin KWALLIYAR dake fusko kinsu duk wanda ya kallesu baya karawa


Abu ta jabe a kasa tace daga nan babu inda zani


Meyasa


Saboda yunwa nakeji indan banciba bazan iya tafi yaba


To bari naga ko zamuga abin siyar wa


Wata yarinya ta wuce ta ga bansu tace zaku sai waina


Binta tace waina Abu kinji waina tab shegu yan birni nasani ai duk abinku saikun hada da qauye sauke mu gani


Yarin yar ta sauke sukace na nawa ne a ciki


Tace dubu1


Abu tace Yarinya kingama ciniki yidari


Yarinya tayi dariya


Abuda binta suka Sa hannu a robar waina suna ci


Can gida kuwa ne mansu kaiwai a keyi suzo suci a binci gashi kuma malamin da ze koyar dasu yazo


Amal tace yaya Aqeel bangan subafa


Baki gansuba kamarya ina zasuto cewar Arif


Amal tace nima ban saniba


Hajiya ta daga hannu sama tana cewa Allah kasa muga yaran nan Allah kakaresu a duk inda suke


Aqeel yace mommy dan Allah karki damu zamu nemo su duk inda suke bari mu tam bayi me gadi koyaga fitar su


Dukan su suka je gurin megadi


Arif yace kaga fitar kannen mu guda2nan da sukazo


Eh nagani sunce min suntafi bude ido


Alhaji yace Bude ido kai Arif Aqeel kuzo muje Neman su


Aqeel rai a bace yacewa megadi tin yaushe kake aiki a gidan nan dasuka ce maka haka saika zo ka tam baye mu kafin ka barsu su fita


Ayi min Afuwa insha Allahu hakan baze sake faruwaba


Arif yace daddy karka damu kukoma ciki zamu nemosu da kanmu mu kawo su


Amal tace yaya zan biku


Arif yace taho mu tafi


Hajiya tace saikun dawo Ku kula da kanku idan kun gansu Ku kira Ku fada mana


To mommy


Me gadi ya bude musu suka fita Neman su abu


Saida su kaci suka koshi sukace taje ta siyo musu ruwa da kudinta tajeta siyo ta kawo musu suka sha


Alhamdulillah Allah na gode maka yanzu naji dai_dai dauki wai narki ki tafi Allah ya kawo ka zuwa


Yarin yar tace kubani kudina saina tafi


Binta ta kaiwa yarin yar duka tace rashin kunya zaki mana bazamu biya ba Kiyi abinda zakiyi






























New writer's


Hakan Take *husba'ahfama* 🌹🌹💋




👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝
👠👠
👝


💄💅 *'YAR KWALLIYA* 💅💄


👝
👠👠
👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠




Written by *husba'ahfama*




31-32




Yarin yar tace hakama zakice wlh Baku isaba duk abinda kuke takama dashi Nina fiku bala'i yanzu zan dakeku na daki kudina na kaiku gurin yan sanda


Binta tace Ko to bisimillah mafashi keda kinsan komu suwaye tsayawa ma baza Kiyi a nan ba


Yarin yar ta kai wa Abu duka


Abu rai a bace takai mata wani mugun naushi saigata a kasa Abu da binta suka rufar wa yarin yar sukai mata duka


Abu tace Banza a banza kemu zaki nunawa taurin

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads