Showing 1 words to 3000 words out of 65672 words
Chapter 1 - A ZURI'AR ARAB COMPLETE BY MHIZ INNOCENT .txt
ο»ΏQ ZURI'AR ARABβ‘β* An amazing and heart touching story
By MHIZ INNOCENT π»
~08105359153~
Number dina d take always welcoming naku a DM π but pls message me amfani couz number nan an tanade ta ne especially sbd ku ππ»
Its a fictional story so duk wata ko wani d labarin yyi kama d nashi akasi ne aka samu ina fatan xaku kasance d alqalamina tun daga farko har qarshe dan jin wannan labarin me dauke d nishadi zallar cakwakiyar soyayya cin amana d sauransu
Ina miqo gaesuwa a gareku INNOCENTIES ππ Mhiz Innocent luv u owl π»
Bismillahirrahmanir rahim
Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki wanda y bani ikon fara rubuta wannan littafi yah Allah na roqeka dan tsarkin mulkinka kasa yanda na fara rubuta shi lpia na gama shi lpia ameen y rabbil alameen
Wannan littafi gaba dayansa sadaukarwa ne ga er uwata rabin jikina *Yaya* Allah y qaro muku xaman lpia keda mijinki d xuri'a dayyiba π
Godia ta musamman ga en uwna Sa'adatouh Yusuf d Fateema Aliyu ina matuqar qaunarku irin sosae dinn
Qawayena kuma aminaena fateema bashir ummulkhaer Yusuf and maemuna abubukar
Gaesuwa ga en amanata
Khaleesah
Hajara
Azeezah
Humaerah
Aesha
Jameelah
Heart u owl π
, sosae take kallanta tunani fal cikin ranta
haqiqa indae tace xata kirata da fateema kullum ne se er uwatta ta dawo mata
hakan y sanyata janyo wayarta ta shiga wajen xa6en suna
ta dade tana dubawa seda ta samo me ma'ana sannan ta ajjiye wayar
daedae lokacin d arman y shigo a guje kamar yadda ya saba
hango jinjira a hannun mahaefiyartasa y sanya shi qara sauri yana fadin
" mamama " ( haka yke kiranta dashi tun kapin y iya magana sbd haka yaji en uwanta na kiranta d yaya rahama shi kuma be iya fada b sedae yace mamama kuma a haka y dore har ynxn?)
" Mamama baby ce an barmana ita ? ya tambaya yana kallan babyn
murmushi haj rahma tayi tana dada godewa Allah da akan abinda take saqawa a ranta tace
" ehh arman an bar muku ita har abada "
cikin matuqar jin dadi yce
" yeehhh ! mamama xan dinga mata komae daga yau ! baby taho ! y fada yana qoqarn daukarta
" a'ah arman bari tukun kaje k chanja uniform se kazo ka dauketa "
dariya yyi sosae yce
" amma inna fito a hannuna xatay ta xama ko ? daga yau babyna ce " y fada yana sake fadada fuskarsa d murmushi
murmushi ta kuma masa tce
" ehh amma dg yau b sunanta baby ba an saka mata suna sunanta SANAH !!
yamutse fuska yyi kamar wani babba yce
" da dadi " sannan y wuce dakinsa d yke kusa dana mamaman
girgiza kae mamama tayi daedae lokacin d take amsa sallamar Alh alqaseem
shima fuskarsa dauke d murmushi y qaraso y xauna yana kallan babyn
yce
" rahma y qarin haquri ?
" Mungode Allah " ta fada tana gyara kwanciyar Sanah akan cinyarta wadda ke qoqarin tashi
kallanta yyi ckn nutsuwa yce
" rahma bani hankalinki nan "
jin haka y sanya ta bada dukka hankalinta
yce
" ina fatan dae babu wata Matsala koh ?
yanayinta kadae y nuna masa babu matsalar amma dukda haka seda yaji daga bakinta
" tace ehh daddyn arman babu " ta fada fuskar ta dauke d murmushin dake nuna yadda taji dadin tambayar daya mata wadda ke dauke d tarin kulawarsa a garesu baki 1
Jinjina kae yyi sosae yana fadin
" Masha Allah ! Allah y gafartawa fateema sannan y raya baby fateema "
" Ameen " tace kana ta dora d
" daddyn arman an xa6a mata suna pah "
yce
" ahh masha Allah wanne suna aka saka mata ?
murmushi tayi tana kallan babyn kapin tace
" SANAH !
tashi yyi ya kar6eta yana fadin
" toh Allah y raya mana Fateema Sanah "
daedae lokacin Arman y fito ckn qananan kaya y qaraso yn fadin
" daddy kaga mamama ta samomin baby koh ?
dariya y bawa daddyn nasa yce
" ehh mana boy ae mamanka tana qaunarka shys ta samomk baby "
qoqarin kar6arta ykeyi
mamama tce
" kaaga bakaci abinci b snn bakayi sallah b koh ?
yce
" aah mamama nayi sallah pah abinci ne banci b km ae itama baby bata ci b ! don Allah ki bani ita " y fada kamar me shirin sakin kuka
daddy yce
" toh jeka xauna "
b musu y xauna daddy y dorams ita kan cinyarsa daedae lokacin km data faara kuka
d sauri mamama ta tashi ta nupi kitchen ta hado mata madara t daawo
kapin ta daawo harya tashi yana tafiya d ita a kafadunsa kamar y saba d raenon
daddy kua binsa d kallo kwae yana murmushi
mamama ta qaraso xata kar6i Sanah yae saurin fadin
" pls mamama ki bani ni xan bata "
tce
" ohh ni ennan arman madarar ma kae xaka bata ?
yce " ehh "
aekuwa haka y sauko d ita kan cinyarsa
mamama ta tallapo kanta ya dinga bata madarar a hankali
mamama har mamaki take irin yadda arman din yke acting kamar y saba
tana gama sha mamama ta kar6eta ta dorata kapada seda tayi gyatsa sannan ta bashi ita
aekuwa y gane yanda akeyi din bayan an gama basu madarar
ranar wuni yayi yana hidima da Sanah din
islamiyya ma da qyar y tafi seda mamama ta masa Jan ido.
Tun daga ranar pah duk wata kulawar Sanah din Arman keyin ta
bata madara , sakata tayi bacci d sauran abubuwa
wanka d tsarki d saka Pampers ne kwae mamama ke mata amma komae shike mata
wata irin qaunar yarinyar yke kamar bashi d wasu en uwan wanda suke cousins kuma suke tare gida 1
bacci kwae ke rabasu se km in zeje makaranta.
Yana xaune gefen qaramin gadon Sanah din d irin abin wasan yarannan a hannunsa yana karkada mata shi
se kua 6al6ala dariya take
shi km hakan na qaramasa qaemi
daedae lokacin mamama ta shigo tana fadin
" arman "
" na'am mamama gani nan ! baby nakewa wasa "
murmushi tayi tace
" uhmm ae na gani arman toh seka dauketa k kaewa auntynka ( kishiyarta maman Khalid kenan yaron dt xo dashi gidan )
6ata rae yyi kapin yce
" mamama tana jin dadin wasan pah kar a sakata kuka "
" A'ah kaaga babu wanda xe sakata kuka auntyn ce pah kwae "
d hanzari y miqe yana fadin
" yawwah dama banaso Khalid dinnan y dauketa kullum y dauketa setayi kuka "
girgiza kae mamama tayi
" arman banda rigimarka ita Sanah ina tasan waye ma ya dauketa ballantana tayi masa qwuiwa "
bema jita ba dan harya dauki Sanah din y fice d ita
binsa tayi d kallo kana ta miqe itama ta fito
A gefe ta sameshi kusa d auntyn dke dauke d Sanah a hannu
d alama jira yke ta kalleta shi km y kar6a abarsa su koma
aekam ko minti 1 batae a hannun ta b ta miqa masa tana fadin
" gata "
d sauri y kar6a yana barin wajen
auntyn ta juyo d kallanta kan mamama tce
" ashe kuma abinda y faaru kenan ! toh Allah yji qan rae "
" Ameen " mamama ta fada tana mamakin qarfin hali irin na auntyn
lokacin d qanwarta ta ta rasu bata nan amma wata 1 d rasuwar ta daawo
sedae yau sanah ta kusa wata 3 se ynx xataxo mata gaesuwa hadda neman iri na ganin 'yar da marigayiyar ta bari
bayan gabadaya faccalolinta duk seda sukaje mata gaesuwa harcan gidan qanwarta ta
bata qara mintuna 5 ba ta tashi tana fadin
" toh Allah yaji qan rae y raya abinda aka bari nabar Khalid shi kadae bari in wuce "
mamama tace
" toh an gode.
Tana nan xaune taga fitowar arman dauke d Sanah wadda a ynxn y sako mata rigar sanyi
kallansa tayi kapin tace
" ina kuma xakaje ?
" Wajen baffa xanje yau basu gaesa d baby b "
binsa tayi d kallo tana cewa
" toh k gaeda baffan "
" toh " yce yana ficewa daga 6angarennasu xuwa 6angaren former brigadier general Arab tsoho me ran qarfe
y sameshi a kishingide kamar koda yaushe d jarida a hannunsa yana karantawa ( mazan jiya kenan har ynxn akwae idon )
ya qarasa y xauna yana fadin
" baffa ga baby yau bata xo kun gaesa b "
murmushi y wanxu akan kyakykyawar fuskar tsohon yana ajjiye jaridar hannunsa y kar6i Sanah yana fadin
" ahh lallae abokina hala dae yau kae k shirya amaryartawa dan naga tafi kullum kyau "
dariya arman yyi yana fadin
" ehh baffa nine ae daama nafi mamama iyawa "
haka suka cigaba d hirar dama sun saba
kapin suka koma 6angarensu
a hanya suka hadu d Abba ( qanin daddy ) yana shirin fitowa shida souban
Abba yce
" ahh arman sanah ce a hannunka ?
yce
" ehh Abba daga wajen baffa muke "
" toh ka dena fitowa d ita a cikin sanyin nan saboda kar sanyi y kamata kaaji koh ? yayi maganar yana kar6arta
arman yce
" toh Abba "
souban yce
" Abba nima k bani sanah din in dauketa "
" aah kaga mu wuce kaga sauri nake karka makarar dani ". Abba y fada kapin y juyo yana kallan arman
" maza jeka kae sanah gida kazo mu wuce masallaci "
kar6arta yyi yana fadin
" toh.
Tun daxu yke ta faman lallashinta taqi yin shiru
ya bata madara taqi kar6a y jijjiga ta amma duk a banza
mamama ta qaraso dakin d sauri dan idar d sallahrta kenan t jiyo kukan sanah din
d sauri ta qaraso tana kar6arta
" lpia kua arman meya sameta ?
cikin yanayin kamar yana shirin kuka yce
" Nima bansaniba tun daxu kwae naga tana kuka kuma taqi yin shiru
duddubata mamaman tayi ko wani abunne y cijeta amma bata ga komae b ko wata alama
sedae taga kamar yarinyar tana kae hannunta saetin kunnanta ta janye hannun
amma se taga ta sake mayar d hannun tana qara sautin kukannata..........
Alqalamin Innocent ne βοΈ
*β‘βA ZURI'AR ARABβ‘β* An amazing and heart touching story
By Mhiz Innocent π»
Page 3
~08105359153~
Number dina d take always welcoming naku a DM π but pls message me amfani couz number nan an tanade ta ne especially sbd ku ππ»
Ina miqo gaesuwa a gareku INNOCENTIES ππ Mhiz Innocent luv u owl π»
cikin tashin hankali ta fito daga dakin sedae daddy baya nan
hakanne y sakata daukar mayafinta ta hau mota suka wuce asibiti ita d arman
tashin farko aka kar6esu ana dudduba yarinyar.
Mintuna wajen 20 kapin wani doctor yce d ita ta biyoshi office
kae tsaye ta shiga ta ja kujerar ta xauna arman na gefe yana kallansu
doctorn y xare glass dinsa
sannan yce
" hajiya daama yarinyar taki tunda kika haefeta tana d qarancin ji ne ?
Kallansa take sosae d alamar tambaya dan sam bata fahimci xancen nasa ina y dosa b
jin bata bashi amsa b y sanyashi fadin
" ohh sorry hajiya na manta ashe pah baby ce nasan ba xaku gane ko tana ji ko bata ji b !
so ynx dae bayani 1 shine hajiya yarinyarki tana d qarancin ji ne kuma dan tayi ciwon kunne b wata damuwa bace saboda xe iya dinga tasar mata a kowanne irin lokaci ne
amma ynx xamu san yanda xaayi insha Allah kapin babban likita yazo in yaso seya fadi abinda xaayi din
gabadaya mamama ta kasa cewa komae jin wae sanah tana d qarancin ji " kenan kurma ce ? ko me wannan likitan ykeso ya fadamata.
Magunguna y rubuta mata ba tare d tace masa komae b ta fito ta wuce pharmacy ta kar6i magungunan sannan suka wuce gida
shidae arman be fahimci komae b ya daega babyntasa tayi shiru
ita dae mamama bin sanah kwae take d kallo har wasu hawaye taji suna xubo mata
cikin sauri ta gogesu kapin ta dudduba magungunan sannan ta saka mata na shafawa a kunnen ta bata nasha tana ta yamutsa fuska
arman d bashi ke sha b shima se yamutsa fuskar yke
tana gama bata y dauketa yaje y kwantar d ita.
Gabadaya jin jikinta take babu qwari ta kasa yin komae tunanin sanah din y cika mata xuciya d ruhi
ynx qaramarta d ita bata d lpiar kunne
" yah salaam " ta fada tana dafe kanta
daedae lokacin d umma ( matar baba qaninsu daddy d Abba kenan ) d sallama ta shigo dakin
ganinta y sanya mamama daga ido tana fadin
" umman amrah sannu d shigowa "
" yawwah sannu dae maman arman ! dama shigowa nayi naji naaga dazu kin fita cikin sauri kamar babu lpia kuma ynx kin dawo ma kamar babu lpia ?
Jinjina kae mamaman tayi kapin tace
" wlh umman amrah kinga yarinyar nan ce taketa kuka tun daxu shine na kaeta asibiti suke tabbatar mana d cewar tana d qarancin ji shys yau d ciwon kunne ta tashi "
" Yah salaam yah salaam " umman ta fada ta maemaeta
" Eyyah Allah mae yadda yaso d bawansa Allah y bata lpia ! don Allah ki dena damun kanki kinji insha Allah idan d rabon warkewa kinga ae xata warke
Mamama tace
" haka ne insha Allah "
nan suka cigaba d hira dan daama tasu tazo 1 a cikin matan gidan kansu a hade yake yayinda aunty ( kishiyar mamama d mama matar Abba ) Kansu a hade yke kuma sune masu baqin hali a cikin gidan.
Dawowarsa kenan daga makaranta y shigo dakin yana kiran
" baby ! baby " d qarfi
sakamakon daga muryar d yke tana iya jiyoshi aekuwa ta fara xillo kan keken xaman d take
d hanzari ya qaraso yana rungumeta
" baby na daawo "
se dariya take itama tana kallansa cikin gwarancinta itama tace
" be..bi *
ranar murna kamar xeyi me har rawa seda yayi yau sanah tayi magana
yana nan yana murnarsa ya jiyo muryar souban daga parlour
daukar sanah yayi suka fito
ganinta ya sanya souban din qarasowa yana cewa
" arman kawota na dauketa na kaeta suyi wasa da afrah "
ta6e baki arman din yayi kamar wani babba
" a'ah souban indae kanaso suyi wasa kaje ka dauko afrahn ka kawo ta nan se suyi wasan "
" shikenan toh bari in daukota har amrahn baba ma xan dauko se suyita wasan tare "
shi dae arman bece masa komae b har y fice
aekuwa se gashi y kawo su duk akan kekunan xamansu dan duk xasuyi sa'anni sedae wannan ta bawa wannan wata ko watanni amma dae duk sun girmi sanah
haka suka hadasu sukuwa sukaeta wasansu souban d arman suna kallansu suna dariya in sunyi abin dariya.
Suna haka souban y jiyo muryar mamansu dga parlour tana fadin
" souban rashin kirkin naka har yakae ka fito min d yarinya a cikin sanyin nan ! toh miqomin abata ni ba shashasha bace "
a sukwane y janye keken d afrah ke kae y fita y kaewa maman ita
kana y daawo arman yce
" toh k dauki amrahn itama ka kaeta gidansu mana " dan shi kam Allah ma ya gani y gaji d wasan yafiso su 2 suyi abinsu
haka souban y dauka amrahn itama y kaeta 6angarensu kapin y wuce nasu.
Kwanaki suka cigaba d garawa satika na shudewa suka hadu suka bada shekaru 3 shaquwa me tsanani na sake shiga tsakanin arman d sanah
yanxu haka indae xaka mata magana d qarfi xataji abinda kke fada
amma indae a hankali kayi kamar yadda xakayi d mutum me normal kunne baxa taji b sedae kwae ta kalleka
ta faara xuwa islamiyya tana fahimtar karatun sosae duba d yanayin karatun islamiyya ana yinsa ne d qarfi
gata akwae qwaqwalwa ana yi musu karatu xataxo tana biyawa arman ko mamama ko daddynta.
" Baby ! Baby ! Ta fada d qarfi yanda tasan xe jita
d sauri y qaraso yana fadin
" baby gashi pah na siyo miki sweet din "
" me kace ? Ta fada cikin muryar ta na me koyo
yce
" ehh na siyomk sweet din "
kallan bakinsa kwae takeyi hakan yasa ta gane abinda yake fada dukda ma seda ya daga murya
tace
" toh ina sweet en ?
yce
" ohyah close ur eyes " y fada yana kulle idansa
ganin hk y sanya ta rufewa
shi km y miqo hannunsa ya dakko hannunta y dora mata akan hannun
ta bude ido tana kallan sweet din ta bude ido tana bude baki ( duk wani wayo d surutunsa ta dakko shi ) tace
" baby duka ?
yce
" yes baby !
rungumeshi tayi tana fadin
" kuma baxan sanwa amrah da afrah ba amma xan bawa mamama "
ta fada tana ficewa daga dakin
a parlour ta sami mamama d daddy ta qarasa wajen daddyn d gudu tce
" daddy kaaga baby y siyo min "
" ahh er gidan baby mu gani " daddy y fada yana kar6ar sweet din
ita kua se dariya take
mamama tace
" daddyn arman bani sweet dinnan yaron nan na hanashi siyowa sanah kayan zaqi haka amma yaqi ji "
daddy yce
" aah ki barta in kikae haka baxa taji dadi b ki barta a hankali xata dena shan xaqin " y fada yana kallan Sanah d tayi rau rau d ido hade d ta6e baki
Ba don taso b haka ta qyaleta
shi km daddy y miqamata sweet din yana kallanta
ita kuma seta kalleshi ta bada hankalin ta sosae dan so take ta fahimci abinda xe fada mata din
yce
" jeki daki "
d gudu kuwa ta kwasa duka suka bita d kallo
daddy yce
" uhmm rahama so nake in saka yarinyar nan a makaranta amma kuma ga yanayin lalurarta y kike ganin xaayi ?
Mamama tace
" nima tunanin d nake kenan tunda dae karatun boko daban dana islamiyya "
Jinjina kae daddy yyi kapin yce
" Kina bata maganin kua ?
mamama tce
" ehh ina bata kwae dae Allah ne beyi xata dinga ji sosae din b har ynx "
cikin nuna amincewa d xancennata yce
" hakane amma akwae wata shawara dana yanke
daama next week in Allah y kaemu xan je los Angeles toh insha Allah ki shirya se muje a duba